← Book details Ganin Ido Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 154

Sashe 56

Ganin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

53
*ZUZEAM VENTURES*
08144015291
https://wa.link/l1gcz8
ASSALAMU ALAIKUM
Mata masu abun duniya🔥🔥🔥
*Zuzeam ventures* takawo muku babbar gara basa Duka akan 7k ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki  Garabasa gara basa, Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 7k na
1. Sashen kaza
2. Ciccibi
3. Gumba madara da chocolate
4. Gari 7in1
5. Tsimi mallaka 5. Tsimin matar minister
6. Women coffee 3in1 sunada kyauta abubuwa kamar haka:Matsin ba a Fira da wando 1k,Matsin maganin infection 1k,Dripping pills 1k,Turaren mallaka 2k
Total total gift 5k
Kiyi kokari ki kasance aciki  Garabasa kan garabasa Da 7k dinki ki mallaki kayan da ko 16k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah 08144015291 Maman yasmeen takuce  For more information say hi
Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam ventures tashirya tsaff dominku muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu
*DAHUWAR KAZA*
Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt Akwai kyauta mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya
MASU JEGO DA AMARE
Karku bari wannan dama ta wuceku
Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 2000 kacal.
Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd
Infection set
Sabon budurci set
Niima set
Basir set
Matsi mallaka
Amarya set
Uwar gıda set
Mai jego set.

*******
Ms Meenah bata samun kanta da farin da tsabanin dokin zuwa Nigeria ba sai yanzu datake jin ta matsu ta isa itama ta zauna cikin dangin Jeerahs duniyar Nigeria taga itace matar mutumin da kowa yake son gani,
Aga matar da itace takeda Fleet Raheem jeerah wanda duka mata bazasu samu ba hakama a kaf ahalin jeerah babu kamar Fleet Raheem jeerah dan haka suna buqatan ganin macensa uwar yarsa da baitaba hadawa da komaiba wadda take mulkin zuciyarsa.

A bangare daya bayan alfaharin datake son taje tayi da nunawa duniyarsa kanta tana son zuwa ne sbd su mommy datake jinsu kaman wasu ahalinta sbd a yanzu kusan sun maye mata gurbin duk wasu aminanta dik da batada wasu kawaye ko aminai 'yarta itace kawarta kuma aminiyarta dan haka a yanzu take shaawa da raayin rayuwa anan a cikin wainda take jinsu wanda ko so daya ma basu taba maganarsu da Dr Mum ba hakama itama yanxu dr mum batason doguwan waya da Ms Meenah din sbd kada tasan halinda ake ciki koda a Tsautsayi.

Ta gama shirin tafiyarta tsaf ranar tafiyan take jiran tayi kawai su tafi.

Sai da ya zama busy sosai sbd ayyukan dasuke gabansu sai daga baya ya saka imran yayi clearing duka schedules dinsa da cancellin duk wani appointment da suka bayaar suka tattara duka bar qasar jirginsa na dagawa.

Fammah tinda tasan iyayenta na hanyar xuwa ta kasa zaune da tsaye sbd tsantsan farin cikin da dole SANAAH itama take ciki dan tayata murnan zuwan iyayenta musamman Mum wadda dukansu suke maraba da ita sbd suna tsananin murnan zuwan nata,

Mommy kuwa farin cikin duka iyayen take dan su duka nata ne,

Komai na bangaren Dad dinta itace ta saka Safiya gyara mata komai nasa da kyau.

Duk hidimar datake yi tarban iyayenta da SANAAH akeyi dole sbd babu yanda zata iya kasa taya fammah farin ciki koda kuwa bata so sbd irin kaunar da fammah ke mata tayi yawan da kusan tafi tata sbd ita wani lokacin idan ta tina abinda yake boye sai taji jikinta na neman mutuwa ita kuwa fammah da batasan komaiba da dukkanin zuciya da ruhinta take tsananin kaunarta dan a yanzu duniya iyayenta biyu babu wanda yakai mata SANAAH a zuciya da rayuwa kaman yanda itama bayan mommynta da yaya Al'amin da Dad to kaf rayuwanta da zuciyarta babu kaman fammah.

Dayake yan matan koyaushe a cikin shirunsu da gayunsu suke babu buqatan zuwa koina gyara da suke kaman yanda fammah tayi niya.

Sun san sun taso a ranar da suka taso amma basuda tabbacin yaushe zasu iso sbd basusaniba ko zasu fara zuwa Morocco ko wata qasar dan haka tin a ranar jiya suka gama komai dan haka yau hutawa sukeyi.

SANAAH gurin Dad dinta taje sukasha firarsu ta bankwana sbd tasan yanzu bazata iya zuwa koyaushe ba hakama kotaje ba lallai ta iya tsayawaba sbd tsayawanta zai iya sakata haduwa da wanda bata buqatan gani sbd a yanzu da duka zuciya da gangar jikinta da ruhinta take qin auren na mutumin dayake Dad din Aminiyarta kuma rabin jikin mutumin dayake zuciyarta bazata iya ciresaba har abada bama zata iya ko kallansa a matsayin miji ba ta bangarori da dama sbd ganin kaman hakan yama haramta a tsakaninsu.

Bata dawo ba sai dare sosai ko data dawo Fammah ta gama shirin bacci zata kwanta dan haka itama qarasowa tayi tana zare hijabinta sbd already tayi shirin baccinta ta fita.

Hawa gado tayi tana janyo wayarta dan duba sakonnin dataga sun shigo na prof bayan an sanar da iyayensa da basa hakuri akanta ya dauke kafa na wani lokacin amma ganin irin yanda har lokacin take rayuwa da fammah da sauransu ya sakasa kasa hakura sbd zuciyarta neman bugawa takeyi akan rashinta dan haka ya fara neman wata sabuwar hanyar shiga zuciyarta ta bangaren fammah wadda take yayi mata akan SANAAH dinta sbd babu abinda ya rasa na dik wani hadadden namijin datake musu fatan samu sbd yanada kyan gaske ga kuma dukiya da ilimi da wayewa tareda class bayada wata hayaniya kawai dai ya girmesu sosai amma bawai ya zama babba ba dan baka ita komai yayi mata tafara kokarin cusashi da nema masa soyayyar SANAAH din tana banzatar da maganar SANAAH din dake sanar da ita tanada wanda Dad ya tsayar mata tukuna batama sansa ba batasan ina yake ba.

Cikin rashin bawa zancen mahimmanci fammah ke cewa

"Prof shine wanda muke so bama san wanda bamu san inda ma yake ba kokuma yanda yake ba,hakama grandfather banajin ya fada ne dan akwai wani din da gaske kila sedai dan kada ki kula kowa kafin gama karatunki yanzu kuma kinga,nidai Prof nakeso gaskia shine kadai yakai dacewan da zamu basa ke"

Yawan hakan da Fammah ke fada ya saka SANAAH jin inama baa riga an daura aurenba da soyayyarta zata bawa Prof din sbd kaucewa wannan auren da batajin akwai khairan a cikinsa,

Duk da hakan sai ta dan ringa sassautowa tana son bawa prof dama amma kuma tana kiyayewa tukuna sbd kiyaye haqqin Allah da auren dayake kanta kawai dai ta koma dan mutuncin da sukeyi a baya dashi sbd su dena mata maganar sonsa kwata kwata daga shi har Fammah din kuma hakan ce ta faru sai fammah ta dena damunta kwata kwata akansa sbd ganin yanzu suna gaisawa shima ganin hakan saiyayi tinanin ya samu sabuwar damar ne.

*****
Washe gari tana cikin baccinta mai dadi da basa tashi da wuri idan sukai sallan asuba suka koma suka kwanta sam basa tashi bakuma a tashinsu saisun tashi da kansu,

Guraren 9 ne na safe taji fammah ta shigo bargon datake rufe dashi mai tsananin laushi bata ce komaiba ta kamota gabaki dayanta tana tayarwa zaune cikeda farin ciki mai tsanani tana cewa

"My Baby SANAAH taso taso su Dad sun sauka suna hanyar isowa gida kafin su iso muje mu kunna Aircon da sake dan gyara komai tinda tin jiya aka gama komai yau baa sake aikin komai ba a gurin,Safiya na musu aikin breakfast so dole muje can mu gama kafin su iso"

SANAAH cikin baccinta mai dadi ta bude idanuwanta masu kyau da suka qara wani kyau da sauran bacci a cikinsu tace

"Girl ai kafin mu gama sun iso a bari Safiya ta gama aikin sai taje ta gyara,kokuma tabarmin breakfast din na qarasa kuje ku gyara can din"
Qarasa maganar tayi da sautinta me kaman na babies masu jin sauran bacci tana rungume fammah din da shigewa jikinta.

Gashinta fammah din ta shafa tareda kamawa da dan karfi har saida ta sake yar qara mai sautin shagwaba sosai tace

"Awww zaki kasheni ne ko huta?"

Dariya tayi tareda sake gashin tana cewa

"Oya tashi koba komai bazaki bari su isoba kina kwance kina bacci ba right¿ sbd yanda Mum take cikin tsananin matsuwa data ganmu,just get up girl"

Ba yanda ta iya sbd yanda Fammah ke cakudata dole ta bude idanuwanta gabaki daya tana tashi zaune ta kalleta da harara ta bata fuska.

Kissing kumatunta Fammah tayi tana dariya tace

"My sleeping beauty,my baby,my SANAAH,my besty,my......

Tureta SANAAH tayi tana sauka gadon ta nufi toilet ta shige tana cewa

"Ki dena dariya sbd you'll pay for this"

Dariya fammah ke mata cikin farin cikinta daya kasa boyewa na yau din.

Ko data fito brush da sauran yanda take wanke fuskanta every morning tayo ta fito fresh da ita fatarta da fuskanta suna wata glowing sbd yanda suka samu hutu da wata ninkin lafiyar fata har ita har fammah din.

Janta fammah tayi bata bari ta iya tsayawa komaiba dagasu sai kayan baccin jikinsu doguwan open abaya ne kadai SANAAH ta iya dorawa akan kayanta sai its kuma fammah datake sanye da hijab.

Slippers masu laushi ne a qafafun SANAAH wadda taso karban aikin abincin amma tini fammah ta jata sbd batason su iso basu gamaba suka baro dan shiryawa ba itama SANAAH din da bata ma fatar su iso yanzu dole haka ta sakawa kanta sauri zatai su gama su baro.

Suna shiga bangaren da wannan shine karanta na uku na shigowa amma qamshin dayake cikin palon bai gushe ba da duka duka aikin da sukai akwai sauran qamshin data tabbatarda da na mai bangaren ne.
Chapter 56 · 0% Book details