Sashe 130
Ganin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Breakfast ta zauna zata fara yi a dining SANAAH din ta farka tana tashi zaune ahankali tareda jin jikinta ya dan qara warware ta miqe tana daukan bargon ta kai daki ta ajiye ta fada bathroom.
Wani wankan ta kuma yi ta fito a shirye itama ta nufi dining din fammah na gurin har lokacin suka kalli juna ta dan dauke idanuwanta tana kokarin rikicewa sbd tsananin kunya duk da tana tsammanin fammah bata gane ba ta saki murmushin karfin hali tana dan qarasowa ta zauna tana rasa abin fada amma dai ta kame sosai sbd riqe steez dinta.
Fammah ma dan murmushin karfin halin kawai ta sake tana cewa
"Kin tashi daga baccin kenan,
Idan kina kwana a sofa jikinki xaiyi ciwo ba bare bansanma yaushe kika fara kwanciya a palo ba"
Wani dan sanyi SANAAH taji da jin kenan Fammah ta yadda da anan ta kwana palo dan haka ta dan sake sakewa sake janyo wata maganar.
Itama sama sama ta sake cin abinci suka gama suna baro dining din Ya Al'amin na shigowa zai fita yana waya a natse da wata kwanciyan hankali da rashin iya wayar hayaniya.
Fammah dake baya ce ta dago idanuwanta tana kallowa daidai yana daqowa a natse lokacinda ya qaraso cikin palon ba tsammani idanuwansu suka shiga na juna ganin hakan a waye da kulawa ya sake mata wani lafiyayyan murmushi yana dan mata gaisuwa da idanuwansa da suka sakata kasa gane komai ta kafesa da idonta dasuke kama sak dana ubanta.
SANAAH ya maida idanuwansa akanta ahankali yana daukesu daga fammah din yana miqa mata hannu suka gaisa tana murmushi da masa ina kwana qasa qasa sbd ganin yana waya.
A natse yake wayarsa da turanci mai tsari na yan qasar ya zauna a gefen Fammah wadda ta gagara tsayuwa ta zauna tana hana kanta sake kallansa sbd wani iri datake ji.
Zamansa a kusa da ita yana wayan ya sakata dan juyowa ahankali da nutsuwa ta kallesa qamshinsa na fitowa da jikinsa mai shiga jiki sosai yana shiga hancinta dan haka taji tana dake jin kasa dena kallansa amma kuma bazata iya hakanba dan haka tana dagowa saita sauke idanuwanta akan SANAAH dake dayan gefensa tana murmushi mai kyau tana kallanta ahankali wanda SANAAH din batama lura da tana hakan ba ita kuwa sai tinanin lokacinda SANAAH ke mata wani lafiyayyan kallo a baya ya fado mata wanda yanzu take gane tsananin son Dad dinta ne yake cinta a lokacin kenan.
Wannan tinanin ya sakata dauke idanuwanta daga kan SANAAH din ahankali tana hana kanta kowace tinanin dazai dameta.
Yana gama wayar gaisawa yayi dasu yana juyowa ya kalli fammah a natse wadda taqi kallansa gabaki daya shima bai kalleta sosaiba ya musu sallama ya fice.
Yana fita bada jimawa ba suka fita da Ana wadda ta kaisu wata lafiyayyar luxury spa da suka buqata kusan acan suka wuni sai yamma suka dawo suna dawowa wanka da abinci kawai sukaci suka zauna kallo da hayaniya a palo wadda kusan Ana kaman safiya take ta saki jikinta dasu su kuma daman basada wani wulaqantawa.
Sai dare Ya Al'amin ya dawo baima shigo gurinsu ba ya dai kira wayan fammah ya sanar da ita sbd SANAAH taqi waya har lokacin.
Da daddare Fleet yazo daukanta taqi barin ya shigo haka fita da sunan xuwa gurin Ya Al'amin mijinta bai barta ba ya tafi da ita babu ruwansa da kunya da kame kamen datake yi.
Washe gari sam ko ina bai bari ta fito ba dan haka Ya Al'amin dayasan bata nan sbd yaga fitarsu bai bari fammah ta shiga kadaici ko tinanin komaiba da zai dameta ya kira yace ta shirya zasu fara fita program nata.
Taji dadin hakan sbd tinanikan dakeson damunta dan haka ta shirya ta fito sanye da brown kaya masu kyau a jikinta da handbag dinta sai wayarta shi kuma kaman ko yaushe black kaya ne a jikinsa da fcap tana fitowa ya bude motar ya fito a natse yana waya ya bude mata motar ta shiga ya rife ya zagayo ya shiga yana kashe wayar ya juyo ahankali ya kalleta yana bude baki zaiyi magana ta rigasa cikin cikin son hana kunnuwanta jin muryansa dake sakata kasa hana kanta dagowa ta kallesa tace
"Good morning"
Sake kallanta yayi yana tada motar yaja suka fice kafin ya bude baki yace
"Kin tashi lafiya?
Gyada kai tayi ahankali
Ya waiwayo kadan ya kalleta yana sake wani kyakkyawan murmushi mai sauti daya saka fuskansa saka kirjinta nauyi yace
"Are you alright??
Cikin karfin hali da kamewa ta sake murmushin itama tana cewa
"Eh,fuskana ya nuna banda lafiya ne Ya Al'amin???
"No just asking"
Shiru sukai yana parkawa wani tsadadden gurin coffee ya shiga ya siyo mata ya fito yaja suka tafi wanda yau ne na farkonta so dole zai kasance da ita har wunin gabaki daya.
Ya sakata fara zuwa ne yau sbd ya bawa kowa time dinsa musamman su SANAAH da nauyin fammah yake kokarin hanata sakewa da mijinta ita kanta famman yasan zata buqaci son zama busy sbd kada ta ringa ganinsu.
#MAMUH
09033181070
[22/06, 11:03 am] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee
132
Wuni gabaki daya Al'amin yayi da Fammah a gurin hidima da ita akan class dinta wanda a tare ya zauna da ita sukai attending duk da yanada aiki a gabansa na office harma da meeting sunada amma haka ya dakatar da zuwansa ya tsaya da ita yana hanata shiga kowace kadaici da damuwa ko tinani hakama kulawansa daya saba da tattali ga SANAAH shine ya ringa mata kaman macen datafi kowace mace gata da samun tsaro daga garesa dan kuwa hatta ruwan da zata sha idan zata sha dauka yakeyi a natse batareda jin komaiba ya bude mata ya miqa a mata a natse da kulawa yana waya ko wani abin wanda hakan yake nuna ya saba nuna karshen kulawa da tattali ga duk macen datake a karkashin kulawansa duk da iya SANAAH ne sai mahaifiyarsa a rayuwansa ke samun hakan daga garesa sai kuma ita a yanxu din datake fuskantar wata tattalin da bata saba dasu ba duk da gatan da aka haifeta aciki ta taso a ciki.
Sai yamma sosai suka dawo gida bayan ya biya da ita sunci abinci a wani lafiyayyan gurin cin abincinda acan dinma fara jin kanta tayi kaman bazata iya cigaba da samun wannan kulawa da tattalin nasa ba da suke saka tinaninta da zuciyarta kasa dauka sbd hakan yana sakata kasa iya dena kallansa da idanuwanta da suke mutuwa daga duk abinda yake mata.
A nasa bangaren kuwa shi din mutum ne da kusan koyaushe yake busy dan haka duk kulawan dayake nuna mata da tattali kusan yana waya ne ko duba wani abin dan haka baya wani lura da yanda jikinta yake a mace sedai yasan shi kansa kallanta yana sakasa jin rashin karfin iya gudanar da ayyukansa dan hakan ne yake zabar zama busyn a gabanta batareda ta nema hutu daga kowace aiki ba dan bata cikakkiyar nutsuwansa
Suna dawowa shine riqe da jakarta sbd ta gaji sosai kaman zatai masa kuka dan haka hatta wayarta a hannunsa take ya rakota har cikin palonsu ya tsaya yana dago idanuwansa masu haske da tarin nutsuwa ya sauke mata su ya kalleta yana miqa mata jakarta da wayarta ta dago ta kallesa itama tana dan sauke numfashi da ajiyan zuciya mai sanyi kafin ta daga hannu ta amsa tana bude baki da gajiya da yar yarinta tace
"Thank you and goodnight Ya Al'amin"
Bai bude baki yace komaiba bakinta da yayi maganar ya kalla a natse kafin ya maida idanuwansa akan idanuwanta da suka qi kallansa tana dan kallan gefensa dasu taji tana kasa daukan idanuwansa ta juya ahankali tana sauke ajiyan zuciya da kasa daga kafafunta sbd kunya,
"Goodnight Doc" ya fada yana juyawa yabar gurin kai tsaye yana dan dafe kansa tareda saka hannunsa daya aljihu yana ciro wayarsa dan duba kiran dayake shigowa.
Ajiyan zuciya kawai ta sauke bayan fitarsa kafin ta juyo ahankali ta kalli kofar tukuna ta taka ta wuce daki.
Tana shiga kokarin daidaita sanyin da jikinta yayi tayi dan kada SANAAH ta gane jikinta amace yake amma da alama SANAAH dinma bata gidan bata dawo ba kenan.
Ajiyan zuciya wadda ta sake sanyaya jikinta ta sake ahankali tana zubewa akan kujera da dafe goshinta tana jin tsananin tausayin Mum dinta wadda tabbas bazata iya ganin wannan obsession din na Dad dinta ba ta iya jurewa akan wata gwara ma da suka taho baa gaban mahaifiyarta ake wannan soyayyarba wadda ita kanta haryanxu jin lamarin takeyi wani iri kawai dai tana kokarin korewa da hana shedan shiga zuciya da tinaninta dama bakinta.
Lumshe idanuwanta tayi tana fidda numfashi mai zafi kafin ta miqe tsaye tana fadawa bathroom ta tube tana sakarwa kanta ruwa sbd tako ina dumi takeji.
Tana fitowa wankan shiryawa tayi ta tayar da sallah tayi tana gamawa Laptop dinta ta dauko ta kunna dan duba karatun data fara din yau.
***A daidai wannan time din kuwa SANAAH da suka gama sallan ishai suna zaune a table na abinci da aka jere abinci da snacks da fruits kallansa tayi bayan ta kalli abincin tana kan kafafunsa ta marairaice fuskanta tana bude baki tace
"Pls pls pls"
Bai kalletaba ya saka hannu ya dauki spoon zai fara cin abincin dake gabansu din ta saka hannu ta karba spoon din tana debo brown pasta din dataji veggies ta kai bakinsa ahankali tana kallan idanuwansa da bai dagoba ya kalleta har lokacin ya bude baki a natse ya karba yana ci hankalinsa kwance.
Sake debowa tayi ta kuma basa yaci kafin ta dan dauki cup din coconut milkshake takai bakinsa ta basa yasha kadan yana dan kallanta.
Murmushi tai masa me kyau tana sake kai abinci bakinsa ta ringa basa da kulawa tana sake rokonsa amma baice mata komaiba sbd babu inda zata tafi din dan kuwa tin jiyan take rokonsa amma babu alaman ma zai tanka ta.
Koshi yayi ta sake basa Coconut milkshake din a bakinsa tana sake bude baki tace
"To zan kira Maamah na fada mata"
Wani wankan ta kuma yi ta fito a shirye itama ta nufi dining din fammah na gurin har lokacin suka kalli juna ta dan dauke idanuwanta tana kokarin rikicewa sbd tsananin kunya duk da tana tsammanin fammah bata gane ba ta saki murmushin karfin hali tana dan qarasowa ta zauna tana rasa abin fada amma dai ta kame sosai sbd riqe steez dinta.
Fammah ma dan murmushin karfin halin kawai ta sake tana cewa
"Kin tashi daga baccin kenan,
Idan kina kwana a sofa jikinki xaiyi ciwo ba bare bansanma yaushe kika fara kwanciya a palo ba"
Wani dan sanyi SANAAH taji da jin kenan Fammah ta yadda da anan ta kwana palo dan haka ta dan sake sakewa sake janyo wata maganar.
Itama sama sama ta sake cin abinci suka gama suna baro dining din Ya Al'amin na shigowa zai fita yana waya a natse da wata kwanciyan hankali da rashin iya wayar hayaniya.
Fammah dake baya ce ta dago idanuwanta tana kallowa daidai yana daqowa a natse lokacinda ya qaraso cikin palon ba tsammani idanuwansu suka shiga na juna ganin hakan a waye da kulawa ya sake mata wani lafiyayyan murmushi yana dan mata gaisuwa da idanuwansa da suka sakata kasa gane komai ta kafesa da idonta dasuke kama sak dana ubanta.
SANAAH ya maida idanuwansa akanta ahankali yana daukesu daga fammah din yana miqa mata hannu suka gaisa tana murmushi da masa ina kwana qasa qasa sbd ganin yana waya.
A natse yake wayarsa da turanci mai tsari na yan qasar ya zauna a gefen Fammah wadda ta gagara tsayuwa ta zauna tana hana kanta sake kallansa sbd wani iri datake ji.
Zamansa a kusa da ita yana wayan ya sakata dan juyowa ahankali da nutsuwa ta kallesa qamshinsa na fitowa da jikinsa mai shiga jiki sosai yana shiga hancinta dan haka taji tana dake jin kasa dena kallansa amma kuma bazata iya hakanba dan haka tana dagowa saita sauke idanuwanta akan SANAAH dake dayan gefensa tana murmushi mai kyau tana kallanta ahankali wanda SANAAH din batama lura da tana hakan ba ita kuwa sai tinanin lokacinda SANAAH ke mata wani lafiyayyan kallo a baya ya fado mata wanda yanzu take gane tsananin son Dad dinta ne yake cinta a lokacin kenan.
Wannan tinanin ya sakata dauke idanuwanta daga kan SANAAH din ahankali tana hana kanta kowace tinanin dazai dameta.
Yana gama wayar gaisawa yayi dasu yana juyowa ya kalli fammah a natse wadda taqi kallansa gabaki daya shima bai kalleta sosaiba ya musu sallama ya fice.
Yana fita bada jimawa ba suka fita da Ana wadda ta kaisu wata lafiyayyar luxury spa da suka buqata kusan acan suka wuni sai yamma suka dawo suna dawowa wanka da abinci kawai sukaci suka zauna kallo da hayaniya a palo wadda kusan Ana kaman safiya take ta saki jikinta dasu su kuma daman basada wani wulaqantawa.
Sai dare Ya Al'amin ya dawo baima shigo gurinsu ba ya dai kira wayan fammah ya sanar da ita sbd SANAAH taqi waya har lokacin.
Da daddare Fleet yazo daukanta taqi barin ya shigo haka fita da sunan xuwa gurin Ya Al'amin mijinta bai barta ba ya tafi da ita babu ruwansa da kunya da kame kamen datake yi.
Washe gari sam ko ina bai bari ta fito ba dan haka Ya Al'amin dayasan bata nan sbd yaga fitarsu bai bari fammah ta shiga kadaici ko tinanin komaiba da zai dameta ya kira yace ta shirya zasu fara fita program nata.
Taji dadin hakan sbd tinanikan dakeson damunta dan haka ta shirya ta fito sanye da brown kaya masu kyau a jikinta da handbag dinta sai wayarta shi kuma kaman ko yaushe black kaya ne a jikinsa da fcap tana fitowa ya bude motar ya fito a natse yana waya ya bude mata motar ta shiga ya rife ya zagayo ya shiga yana kashe wayar ya juyo ahankali ya kalleta yana bude baki zaiyi magana ta rigasa cikin cikin son hana kunnuwanta jin muryansa dake sakata kasa hana kanta dagowa ta kallesa tace
"Good morning"
Sake kallanta yayi yana tada motar yaja suka fice kafin ya bude baki yace
"Kin tashi lafiya?
Gyada kai tayi ahankali
Ya waiwayo kadan ya kalleta yana sake wani kyakkyawan murmushi mai sauti daya saka fuskansa saka kirjinta nauyi yace
"Are you alright??
Cikin karfin hali da kamewa ta sake murmushin itama tana cewa
"Eh,fuskana ya nuna banda lafiya ne Ya Al'amin???
"No just asking"
Shiru sukai yana parkawa wani tsadadden gurin coffee ya shiga ya siyo mata ya fito yaja suka tafi wanda yau ne na farkonta so dole zai kasance da ita har wunin gabaki daya.
Ya sakata fara zuwa ne yau sbd ya bawa kowa time dinsa musamman su SANAAH da nauyin fammah yake kokarin hanata sakewa da mijinta ita kanta famman yasan zata buqaci son zama busy sbd kada ta ringa ganinsu.
#MAMUH
09033181070
[22/06, 11:03 am] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee
132
Wuni gabaki daya Al'amin yayi da Fammah a gurin hidima da ita akan class dinta wanda a tare ya zauna da ita sukai attending duk da yanada aiki a gabansa na office harma da meeting sunada amma haka ya dakatar da zuwansa ya tsaya da ita yana hanata shiga kowace kadaici da damuwa ko tinani hakama kulawansa daya saba da tattali ga SANAAH shine ya ringa mata kaman macen datafi kowace mace gata da samun tsaro daga garesa dan kuwa hatta ruwan da zata sha idan zata sha dauka yakeyi a natse batareda jin komaiba ya bude mata ya miqa a mata a natse da kulawa yana waya ko wani abin wanda hakan yake nuna ya saba nuna karshen kulawa da tattali ga duk macen datake a karkashin kulawansa duk da iya SANAAH ne sai mahaifiyarsa a rayuwansa ke samun hakan daga garesa sai kuma ita a yanxu din datake fuskantar wata tattalin da bata saba dasu ba duk da gatan da aka haifeta aciki ta taso a ciki.
Sai yamma sosai suka dawo gida bayan ya biya da ita sunci abinci a wani lafiyayyan gurin cin abincinda acan dinma fara jin kanta tayi kaman bazata iya cigaba da samun wannan kulawa da tattalin nasa ba da suke saka tinaninta da zuciyarta kasa dauka sbd hakan yana sakata kasa iya dena kallansa da idanuwanta da suke mutuwa daga duk abinda yake mata.
A nasa bangaren kuwa shi din mutum ne da kusan koyaushe yake busy dan haka duk kulawan dayake nuna mata da tattali kusan yana waya ne ko duba wani abin dan haka baya wani lura da yanda jikinta yake a mace sedai yasan shi kansa kallanta yana sakasa jin rashin karfin iya gudanar da ayyukansa dan hakan ne yake zabar zama busyn a gabanta batareda ta nema hutu daga kowace aiki ba dan bata cikakkiyar nutsuwansa
Suna dawowa shine riqe da jakarta sbd ta gaji sosai kaman zatai masa kuka dan haka hatta wayarta a hannunsa take ya rakota har cikin palonsu ya tsaya yana dago idanuwansa masu haske da tarin nutsuwa ya sauke mata su ya kalleta yana miqa mata jakarta da wayarta ta dago ta kallesa itama tana dan sauke numfashi da ajiyan zuciya mai sanyi kafin ta daga hannu ta amsa tana bude baki da gajiya da yar yarinta tace
"Thank you and goodnight Ya Al'amin"
Bai bude baki yace komaiba bakinta da yayi maganar ya kalla a natse kafin ya maida idanuwansa akan idanuwanta da suka qi kallansa tana dan kallan gefensa dasu taji tana kasa daukan idanuwansa ta juya ahankali tana sauke ajiyan zuciya da kasa daga kafafunta sbd kunya,
"Goodnight Doc" ya fada yana juyawa yabar gurin kai tsaye yana dan dafe kansa tareda saka hannunsa daya aljihu yana ciro wayarsa dan duba kiran dayake shigowa.
Ajiyan zuciya kawai ta sauke bayan fitarsa kafin ta juyo ahankali ta kalli kofar tukuna ta taka ta wuce daki.
Tana shiga kokarin daidaita sanyin da jikinta yayi tayi dan kada SANAAH ta gane jikinta amace yake amma da alama SANAAH dinma bata gidan bata dawo ba kenan.
Ajiyan zuciya wadda ta sake sanyaya jikinta ta sake ahankali tana zubewa akan kujera da dafe goshinta tana jin tsananin tausayin Mum dinta wadda tabbas bazata iya ganin wannan obsession din na Dad dinta ba ta iya jurewa akan wata gwara ma da suka taho baa gaban mahaifiyarta ake wannan soyayyarba wadda ita kanta haryanxu jin lamarin takeyi wani iri kawai dai tana kokarin korewa da hana shedan shiga zuciya da tinaninta dama bakinta.
Lumshe idanuwanta tayi tana fidda numfashi mai zafi kafin ta miqe tsaye tana fadawa bathroom ta tube tana sakarwa kanta ruwa sbd tako ina dumi takeji.
Tana fitowa wankan shiryawa tayi ta tayar da sallah tayi tana gamawa Laptop dinta ta dauko ta kunna dan duba karatun data fara din yau.
***A daidai wannan time din kuwa SANAAH da suka gama sallan ishai suna zaune a table na abinci da aka jere abinci da snacks da fruits kallansa tayi bayan ta kalli abincin tana kan kafafunsa ta marairaice fuskanta tana bude baki tace
"Pls pls pls"
Bai kalletaba ya saka hannu ya dauki spoon zai fara cin abincin dake gabansu din ta saka hannu ta karba spoon din tana debo brown pasta din dataji veggies ta kai bakinsa ahankali tana kallan idanuwansa da bai dagoba ya kalleta har lokacin ya bude baki a natse ya karba yana ci hankalinsa kwance.
Sake debowa tayi ta kuma basa yaci kafin ta dan dauki cup din coconut milkshake takai bakinsa ta basa yasha kadan yana dan kallanta.
Murmushi tai masa me kyau tana sake kai abinci bakinsa ta ringa basa da kulawa tana sake rokonsa amma baice mata komaiba sbd babu inda zata tafi din dan kuwa tin jiyan take rokonsa amma babu alaman ma zai tanka ta.
Koshi yayi ta sake basa Coconut milkshake din a bakinsa tana sake bude baki tace
"To zan kira Maamah na fada mata"