← Book details Ganin Ido Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 154

Sashe 48

Ganin Ido Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"You are ok da hakan right Ms Fammah"

Zubawa SANAAH idanuwanta tayi tana kallanta da karantar yanayinta na budurwan da kai tsaye zaka fahimci tanada class da tsari da wayewa tukuna ta dawo da kallanta akanta tace

"Ok"

SANAAH da bata damu da Fammah din ta bita ko kada ta bita ba firarta tafara da Dad kaman yanda suka saba Dad din na sako fammah sbd yana buqatan sakewanta sosai da SANAAH wanda hakan zai saka taji dadin zama kuma gashi kusan halayensu daya basa wani son hayaniya da damuwa ko kadan ga biyayya da ilimi.

Sun jima sosai acan kafin SANAAH ta miqe suka fito tareda fammah din wadda ta sanar da Imran dake waje yana jiranta zatabi SANAAH bangarensu a kawo mata kayanta can kuma a sanar da Dad dinta grandpa ya turata inda zata zauna.

Imran da kansa yaje har bedroom dinta ya hado mata kayanta ya kawo mata inda sukaje ya fara ganin bangaren batareda ya shiga ba.

SANAAH kuwa koda suka iso bangarensu dayake shima a tsare da kowane jin dadi da kusan tsarin da Fammah din zataso a palo suka tadda mommy da safiya suna kallo.

Da mamaki suka juyo suna kallanta da baquwan data shigo da ita suna nuna sakewa da kulawa sukai mata sannu da zuwa.

Famman ma a dan natse da biyayya ta bude baki ta gaida mommy tana maida kallanta kan safiya ta amsa gaisuwanta da gyada kai.

SANAAH ce ta nuna mata gurin zama tana cewa

"Mommy baquwan Dad ce daga America fa,
Jikarsa daya tak kuma yar gatansa"

Cikin farin ciki da kulawa da kauna mommy ta sake kallan fammah din tana mata sannu da zuwa hakama safiya sake gaidata tayi tana nufar kitchen dan kawo mata ruwa.

Ajiyan zuciya fammah ta sauke tana dan sake fuskanta dan nuna yabawa da yanda mommy ta sake tana sake mata sannu da kulawa sosai.

SANAAH ma kitchen ta nufa itada Safiya suka dan hau hada mata tea mai dadin gaske dayaji kayan qamshi da madara mara zaqi sosai full cream sai snacks dinsu da safiya tayisu ayau masu dadi da qwarewa.

Safiya ce ta dauko tray din ta biyo SANAAH suka iso palon aka ajiye mata a gabanta ta bude baki a natse da kulawa itama tace

"Thank you"

Shan tea din tafara a natse tana dan duba wayarta saiga imran ya kawo mata kayan yayi knocking.

Safiya ce taje ta karbo ta kawo Mommy tace takai mata dakin SANAAH tukuna kafin a gyara mata dayane bedroom din.

Tasha tea din sosai taci snacks din suma taji ta koshi ta samu gamsuwan da bata samu ba ta yunwar cikinta tinda ta iso.
#MAMUH
09033181070
[05/05, 1:42 pm] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

46
*ZUZEAM VENTURES*
08144015291
https://wa.link/l1gcz8
ASSALAMU ALAIKUM
Mata masu abun duniya🔥🔥🔥
*Zuzeam ventures* takawo muku babbar gara basa Duka akan 7k ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki Garabasa gara basa, Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 7k na
1. Sashen kaza
2. Ciccibi
3. Gumba madara da chocolate
4. Gari 7in1
5. Tsimi mallaka 5. Tsimin matar minister
6. Women coffee 3in1 sunada kyauta abubuwa kamar haka:Matsin ba a Fira da wando 1k,Matsin maganin infection 1k,Dripping pills 1k,Turaren mallaka 2k
Total total gift 5k
Kiyi kokari ki kasance aciki Garabasa kan garabasa Da 7k dinki ki mallaki kayan da ko 16k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah 08144015291 Maman yasmeen takuce For more information say hi
Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam ventures tashirya tsaff dominku muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu
*DAHUWAR KAZA*
Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt Akwai kyauta mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya
MASU JEGO DA AMARE
Karku bari wannan dama ta wuceku
Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 2000 kacal.
Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd
Infection set
Sabon budurci set
Niima set
Basir set
Matsi mallaka
Amarya set
Uwar gıda set
Mai jego set.

*******
Mommy dake kokarin nunawa Fammah kulawa janta da yar fira take kokarin yi tana tambayarta Mum dinta da kakarta Dr Mum.

Fammah batada wulaqanta mutane duk da bata wani sakewa dasu hakama tanada iya muaamala da kowa sbd karatun datai na likitaci kowa nasu ne basa qyama ko rashin iya sakewa da kowa dan haka tinda ta koshi taji ta samu nutsuwa da yar sakewa sai tana kokarin bawa mommy amsa sai mommyn na yar dariyar yanda hausarta take suna murmushi.

SANAAH ce ta fara miqewa zata shige sai itama fammah din ta miqe tana cewa tana buqatan hutawa a kaita inda zata huta.

Bedroom din SANAAH suka nufa suka shiga fammah na kallan dakin a natse kamshin SANAAH din daya kama dakin yana tashi a hankali cikin sanyi da nutsuwa,

Komai na dakin take yayiwa fammah sbd komai irin natsa tsarin ne datake buqata ga kuma ba hayaniyar abubuwan Simple sai luxury tako ina.

Ajiyan zuciya ta sake saukewa sbd komai anan yanzu yayi mata.

SANAAH dayake ta riga tayi shirin bacci rigar saman kayanta ta zare ta nufi toilet tayo brush da alwala ta fito ta nemi gado ta haye a natse cikin kayan baccinta masu kyau riga da wando da suka maidata kaman baby gashinta a daure tsakiyar kanta bata matse sosai ba ta janyo wayarta tana dan chatting a natse da murmushi akan fuskanta.

Fammah ma toilet din ta nufa tayo duk abubuwan da zatai a sake ta fito daure da sabon towel data gani a jere sabbi tazo ta zauna a gaban mirror tayi shirinta tsaf tana gamawa ta saka kayan bacci itama riga da wando tazo gadon ta hau a natse tana kashe wayarta gaba daya ta kwanta ba jimawa bacci ya dauketa.

Da asuba a tare suka tashi sukai sallah da adduoinsu suka koma bacci hankali kwance.

Da safe sai karfe kusan 10 SANAAH tafara tashi tayi wanka ta shiya cikin simple wear na boubou din silk material mai kyau da tsada ta fita tayi breakfast tana dawowa daki ta tadda Fammah ta tashi tana zaune a tsakiyar gado tana waya da Mum dinta.

Gaisawa sukai ta dauki abinda zata dauka na key da handbag dinta sai wayarta ga fice tana ce mata ta tafi school.

Bayan tafiyanta school wanka Fammah tayi ta fito a shirye da qananun kaya marasa kama jiki anan suka gaisa da mommy suka hau table tare anan ne mommy ta fahimci bata iya cin komai nasa dan haka da kanta ta shiga kitchen ta soya mata chips da bata sakawa gishiri ba sosai kadan ta saka sai garlic chicken da milk tea mai dadi da qamshin Nescafe.

Cikin jin dadi sosai Fammah taci breakfast din kuwa sosai ta koshi ta buqaci hada mata irin hakan takaiwa Dad dinta sbd zainci irin hakan shima sosai.

Cikin tsari mai kyau da lafiyayyun set na abinci mommy ta hada masa komai harda qarin fruits masu sanyi da tsafta a guri mai kyau Safiya ta dauka tabi bayan fammah din suka tafi.

Koda suka je bai fito ba dan haka safiya na gama jerewa a table bayan ta kwashe breakfast din da suka tadda juyawa tayi ya fice tabar fammah jiran saida ya fito suka gaisa ta gabatar masa da breakfast din kuma yaji sosai shima sbd shine ya basu daidai da cimarsu.

Koda fammah ta dawo ta nunawa mommy jin dadinta sosai harma ta bawa mum dinta labari saigashi data sake kira tace a bawa mommyn su gaisa.

A mutumce da kulawa sosai gaisa da dan kokarin taba fira kafin ta bawa fammah.

Sai yamma sosai SANAAH ta dawo lokacin Fammah na tareda mommy sunata kokarin sabawa sbd fammah batada son takura shiyasa ta saki jiki dasu dan ta ji dadin zaman.

SANAAH da kulawa tai musu sannu tana zaunawa cikinsu taci abinci ta koshi tukuna ta wuce daki dan wanka da kimtsawa.

Da daddare haka da zata tafi Fammah ta bita sukaje tare sukasha firarsu suka dawo fammah ta wuce gurin dad dinta ita kuma ta wuce.

Ayau dinma sam dad bai basa daman ganinsa ba wanda ya sakasa fahimtar ya taba Dad din sosai dan haka washe gari ma da kansa yaje amma babu kowace hanya ko fuskan ganinsa da Dad din ya bada sedai su hadu masallaci ya gaidasa ya amsa amma bayan hakan babu fuska ko kadan daga garesa.

Cikin ruwan sanyi da nutsuwa da nasa tsarin Dad ya nuna masa irin fushim dayayi dashi dan kuwa tafiyar da yayi wadda bazata wuce sati biyu ba sai gashi ya qarar da kwana goma batareda Dad ya basa daman ganinsa ba wanda qarshen fushinsa kenan akansa dan haka ya tabbatarda ko wacece wannan matsayinta a gurin Dad din ba qarami bane..

Imran dayaga alaman tafiyarsu ayanzu babu ta kwata kwata sai yanda Allah yayi take ya samar da duka sauran abubuwan zaman ubangidan nasu a qasar.

Fammah kuwa zama yafara mata dadi a cikinsu SANAAH sbd mommy ta jata a jiki sosai hakama SANAAH duk da bata zama sbd karatu suna sabawa da sakewa dan kuwa hatta Mum dinta tafara kokarin sabawa dasu da sake musu tinda suna bawa yarta kulawa da jim dadin zama Nigeria.

Shi kansa Dad ganin yanda fammah ta fara sakewa da SANAAH suna shaquwa sai ya sassauto ya bawa mahaifinta damar ganinsa ayau da Daddare.

Ita kuwa fammah yau tafara fita dan bin SANAAH tayi wadda yau lectures daya ne da ita dan haka daga can suna gamawa Spa sukaje sai yamma suka dawo gida.
Chapter 48 · 0% Book details