Sashe 4
Alkawarin Masoya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Free page🤧
*EXQUISITE WRITER'S FARUM*
Page5⃣&6⃣
Lahab ne tsaye yana kallonsu cikin mamakin Abinda Ade yake ma Mubeena, fuska ba walwala ya tako wajen da suke tsaye, Itakam jikinta sai rawa yake don ta tsorata bata d'auka lahab bane.
Karasowa yayi kusa da Adewale a daidai lokacin wani farin matashi bazai wuce sa'ar su lahab ba, sanye da kayan gida a jikinsa wando 3queter da riga duk da kayan da gani sun d'an sha ruwa, kallonsu lahab yayi cikin tuhuma ganin su a tsatsaye harda Addansa ma, kai lafiyarku?
Har suna had'a baki wajen basa Amsa ba kome, da sauri mubeena ta sabi kwandon wanke-wanken ta har lokacin jikinta na bari ta shiga kitchen nasu dake gefe.
Kofar gidan suka nufa har sun iso bakin kofa sukaji muryar inna data fito daga bandaki, kai nabeel!!
Da sauri dukansu suka juyo gareta suna kallonta.
Ina zaka??banaji kace makaranta zaka da safen nan ba? yana ganka a haka sannan dumamen dana aje maka bazaka d'auka bane kaci sai ulcer ya kamaka.
gaskiya Inna ki basar kawai ni bazani makarantan nan ba.
akan me bazaka ba?koh don uban gidanka(lahab) baxaije bane? ai tunda na gansa ba uniform nasan za'a rina, toh ka tsaya na fad'a maka gaskiya, tun duniya bai fad'a maka ba, kaga wannan yaro lahabu da wannan d'an yorobawan?su suna da gata iyayen su nada hali koh basuje makaranta ba, rayuwa bazata musu tsami irin naka ba, Amatsayin ka na maraya ka rike maraicin ka kayi karatu ka samu na tallafawa rayuwar ka damu duka, in bakayi karatuba ka samu madogara wazai zamo gatan mu nida yar uwarka nabeel?
jin kalar fad'arda akema nabeel yasa Su fita a sulale suka bar gidan, suna fita kallon Ade lahab yayi"Adewale menene tsakaninka da mubeena Addar Nabeel"?
shuru ade yayi sai kuma ya ce ba kome.
cin serious lahab yayi, karka fara karka kuskura duk rashin jin mu baikai nan ba, koh zamuyi iskanci banda Ahlin mu a ciki, dangin nabeel tamkar nawa nake ganinsu kuma bazanso wani abin ya samesu ba, haka naka dangin bazan yarda a tuzartasu ba, don haka karka kuskura ka bari nabeel yaga irin abinda kayin nan, don Wallahi nasan karshen relationship naku yazo karshe kenan, kadaisan halinsa"?
Promise u hakan bazai kara faruwa ba, amma fa bada niya nayi ba kawai abinda tamin ne banji dadi ba?
"sai kuma aka.......shuru lahab yayi bai karasa ba ganin nabeel ya fitoh daga gidan fuska a hade.
Ade ne ya kallesa toh ina dumemen(dumame)yake koh bazaka fito mana dashi bane?
daga lahab har Ade dariya suka sake tuno Yanda abokin nasu ya tsane dumamen tuwo.
kallon banza ya musu ya kama tafiyar sa, da sauri sukabi bayansa ganin ya nufi gangaren layinsu, " kai nabeel ina zakane"?
kamar bazai amsa ba sai kuma yace, shago
"wani shagon"?
shagon dinki mana
da mamaki lahab da Ade sukace shagon dinki?har suna had'a baki, don rabon nabeel da shago ai an kwana biyu duk da ya iyya dinki, Amma fa banda had'a kura babu abinda ya iyya inya kakkarba kayan mutane sai ya daina zuwa shago" Amma dai yau mafarki kayi wata zata karka akan kudinta koh"?
kallon Lahab yayi sai kuma yayi murmushi kawai hade dacewa, kun manta kudin jesen jiya da mukayi daku zamu saya.
"eh mun tuna"
toh shiyasa yau zanje shago tunda mun fasa shiga school in naga koh Allah zaisa na samu kafun yamma.
amma Nabeel taya zaka samu 10k a rana d'aya kuma a d'inki gaskiya da wuya.
lahab kam baice kome ba jin Amsar da Ade ya bawa nabeel yasa sa ciro 11k innan a Aljuhunsa mikawa Abokin nasa kudin yayi, "gashi 11k ne ka d'auki dubu goma kuje da Ade kusai jese shima kudinsa na hannunsa 1k in ku hau transport"
da mamaki Ade ke kallon lahab daman haka kullum yake mundin D'ayansu baida abu tsakanin shi da Nabeel haka lahab zai d'au nasa ya basu, toh yanzun kai ina zaka?
da sauri Nabeel ma ya jefo masa tambayar sa shima, toh lahab inna karbi kudin nan kai kuma ka saya dame?
"kallonsu yayi toh tambayar wa zan fara amsawa a cikin ku"?
dukan mu suka basa amsa.
" toh gidan mamina zanje koh zaku rakani ne"?
da sauri sukce Ah ah
ok toh sai kuma maganar kudi, ina da wasu kuje kawai da wannan in, kai kuma Ade bani keken nan naka naje dashi a cikin 1k innan Nabeel ya saya abinci tunda bai karya ba.
godiya nabeel ya masa, bai amsa ba sai harara ya dallara masa, cikin wasa yace"babu godiya a tsakanin mu Abokai ai yiwa kaine, ya karasa maganar da hawa kan keken yaja ya kara gaba, suma da ido suka bisa sai kuma suka wuce bakin titi suka tare keke napep zuwa kasuwa.
lahab kam unguwan da maminsa ke aure ya nufa, unguwane mai kyaun gaske packing yayi a kofar wani tangamemen get, gidane mai kyau Amma baikai gidan su kyau ba, hannu yasa ya bubbuga get in hade da danna hon na kekensa.
maigadi dake zaune a d'akinsa jin bugu ba gaggautawa yasa da sauri ya mike takalminsa ya saka cikin sassarfa ya nufi kofar, kokarin bude kofar yake hade da tambayar wanene.
shuru lahab yayi baiyi magana ba, mai gadin nad'an bude kofar zai leka yaga waye ne da gudu lahab yaja keken yayi cikin gidan saura kad'an ya kade maiganin, da sauri ya basa hanya tsayawa kawai yayi yana bin lahab da ido hade da mamakin ganinsa yau don duk da baya ganesu da d'an uwansa, Amma mundin lahab yazo saiya ganesu a d'abi'a da d'an uwansa ne yana zuwa gaidashi zaifara ba kokarin kad'esa ba, komawa kawai yayi ya rufe kofar ya zaune a benchin dake gefen d'akinsa.
lahab bai tsaya da keken saba har ya wuce compound na gidan sai da ya iso har bakin kofar falon in ya tsaya da kekensa, sauka yayi ya jingina keken ya haura baranda, tura kofar falon yayi koh sallama babu ya duro kansa ciki.
mami dake zaune Akan kujera tana shan fruit salad ne ta bisa da ido harya karaso tsakar falon, fuska ta hade tana kallonsa, koma kayi sallama.
tsayawa yayi kikam yana kallonta ganin yanda ta had'a fuska, bazaka fita bane koh yaya?ta sake maimaita wa.
juyawa yayi a hankali wallahi badon bukatar sa bace ta kawosa da inya fitan nan badai ya kara shigowa ba, komawa yayi ya tsaya a bakin kofar, da karfi ya kwala sallama.
Girgiza kai kawai mami tayi jin mannin hauka da lahab yake, amsawa tayi tare da bashi izinin shigowa, ba musu ya shigon, zama yayi a cikin d'aya daga cikin kujerun falon yana kallonta"ina kwana mami"?
Lafiya lahab ashe ana ganin ku?
"Eh mami bagani ba"
Ah ah bukatar ka dai ta kawoka ba zuwan Allah Annabi bane wannan, yasu Addayiya da sauran yan uwan naka da iyaye?
"Suna lafiya mami sun mace suna gaidake"
kadaiji tsoron Allah wallahi taima ma babu wanda yasan kayi hanyar gidan nan, gashidai safiyar jumma'a ce kowani yaro yana makaranta war haka amma kai kana gantali da abokan shashancin nan naka?
"Wallahi mami yaune na tashi kafad'ata na ciwo shiyasa Abbu yace kar naje makaranta"
rufemini baki shashasha kawai Abbun kake ma karya koh sa'anka ne taya za'ace kai kullum cikin case kake, kai ba zuwa makaranta ba kai ba sana'ar baki ba bare fari, sai yawon kamar kare, da ball kai koh kishi bakaji yanda kowa ke yabon yalin d'an uwanka Rahab.
Had'a fuska yayi don shi a duniya ya tsani in za'a masa fad'a ace ya kwaikwayi Rahab abin haushi yake basa.
Ka had'a fuska da kyau, gaskiya na fad'a ai yaron nan ya fika hankali babu ranan jumma'a da yamma daba zaizo wajena ba ya gaidani, yanzun kai tsakani da Allah rabonka da gidan nan tun yaushe?
Fuska a hade yatsungunar da kai, shuru yayi baice kome ba shidai sai Allah Allah yake kartazo ta hanasa kudin nan,"kiyi hakuri mami zanna zuwa kullum insha Allah"
ALKAWARIN KA ai ba Alkawari bane sau nawa kana mini Alkawari kana karyawa, Yanzun sau nawa kanace mini xaka daina saka Addayiya surutu Amma ka daina inne? hatta jiya da Umaimah tazo gidan nan saida ta bani labarin abubuwan da kake musu a gida anya lahab zakayi hankali kuwa, shekara 18 ace mutum baisan inda ke masa ciwo ba?
Shuru yayi yaki tanka mata don shi irin mutanen nan ne da holo baya damunsu sam ga rashin zuciya, koh fad'a kukayi da lahab zuwa anjima ya watsar abinsa, ya cigaba da rayuwar sa baya sakawa kansa tention.
Ganin yanda yayi zuru yana sauraronta kamar radio yasa ta yin shuru kawai, tana kallonsa.
Shima d'aga ido yayi ya kalleta jin ta daina fad'ar had'a ido sukayi da sauri ya sunkuyar da kai yana kaikaya gashin geyarsa"uhmm ayya mamina my only mother ki taimaka mini da 20k mana momcy"ya karasa maganar cikin Alamun a tausaya masa.
Kama baki mami tayi tana kallonsa, uban me zakayi da 20k lahab?
"Wallahi mami so nake na sayi wasu kayane"
Kaya lahab?wani irin kayane baka dashi a gidan ku?daga na banza harda na kirki sanan kazo kace na baka kudi, badai kaya bakam kadaisan me zakayi da kudin, toh bara na fad'a maka lahab bazan baka koh sisi ba kaji na fad'a maka, bazaiyu Yayan ka yana kirana yana mini masifa ina bata ka da kudi b, a badani ba kaji na fad'a maka.
Mikewa lahab yayi tunda yaji mami tace bazata bayar ba toh fa magana ya kare kenan, tafiya ya fara cikin jin ba dadi.
Dawo nan lahab, ba musu ya dawo ya tsaya ka karya kuwa?
"Ah ah"
Toh wuce kitchen akwai abinci ka iba.
Girgiza kai kawai lahab yayi alamun bazaici ba.
Ina wasa da kai?
"Ah ah mami"
Toh karkasa na maimaita kalamaina wuce akwai abinci a kitchen ka iba kazo ka zauna kaci nasan tunda ka fito ba uniform toh nasan baka karya ba, Shiyasa nake Allah Allah muzammil ya dawo shine daidai da kai wuce ka bani waje...
*EXQUISITE WRITER'S FARUM*
Page5⃣&6⃣
Lahab ne tsaye yana kallonsu cikin mamakin Abinda Ade yake ma Mubeena, fuska ba walwala ya tako wajen da suke tsaye, Itakam jikinta sai rawa yake don ta tsorata bata d'auka lahab bane.
Karasowa yayi kusa da Adewale a daidai lokacin wani farin matashi bazai wuce sa'ar su lahab ba, sanye da kayan gida a jikinsa wando 3queter da riga duk da kayan da gani sun d'an sha ruwa, kallonsu lahab yayi cikin tuhuma ganin su a tsatsaye harda Addansa ma, kai lafiyarku?
Har suna had'a baki wajen basa Amsa ba kome, da sauri mubeena ta sabi kwandon wanke-wanken ta har lokacin jikinta na bari ta shiga kitchen nasu dake gefe.
Kofar gidan suka nufa har sun iso bakin kofa sukaji muryar inna data fito daga bandaki, kai nabeel!!
Da sauri dukansu suka juyo gareta suna kallonta.
Ina zaka??banaji kace makaranta zaka da safen nan ba? yana ganka a haka sannan dumamen dana aje maka bazaka d'auka bane kaci sai ulcer ya kamaka.
gaskiya Inna ki basar kawai ni bazani makarantan nan ba.
akan me bazaka ba?koh don uban gidanka(lahab) baxaije bane? ai tunda na gansa ba uniform nasan za'a rina, toh ka tsaya na fad'a maka gaskiya, tun duniya bai fad'a maka ba, kaga wannan yaro lahabu da wannan d'an yorobawan?su suna da gata iyayen su nada hali koh basuje makaranta ba, rayuwa bazata musu tsami irin naka ba, Amatsayin ka na maraya ka rike maraicin ka kayi karatu ka samu na tallafawa rayuwar ka damu duka, in bakayi karatuba ka samu madogara wazai zamo gatan mu nida yar uwarka nabeel?
jin kalar fad'arda akema nabeel yasa Su fita a sulale suka bar gidan, suna fita kallon Ade lahab yayi"Adewale menene tsakaninka da mubeena Addar Nabeel"?
shuru ade yayi sai kuma ya ce ba kome.
cin serious lahab yayi, karka fara karka kuskura duk rashin jin mu baikai nan ba, koh zamuyi iskanci banda Ahlin mu a ciki, dangin nabeel tamkar nawa nake ganinsu kuma bazanso wani abin ya samesu ba, haka naka dangin bazan yarda a tuzartasu ba, don haka karka kuskura ka bari nabeel yaga irin abinda kayin nan, don Wallahi nasan karshen relationship naku yazo karshe kenan, kadaisan halinsa"?
Promise u hakan bazai kara faruwa ba, amma fa bada niya nayi ba kawai abinda tamin ne banji dadi ba?
"sai kuma aka.......shuru lahab yayi bai karasa ba ganin nabeel ya fitoh daga gidan fuska a hade.
Ade ne ya kallesa toh ina dumemen(dumame)yake koh bazaka fito mana dashi bane?
daga lahab har Ade dariya suka sake tuno Yanda abokin nasu ya tsane dumamen tuwo.
kallon banza ya musu ya kama tafiyar sa, da sauri sukabi bayansa ganin ya nufi gangaren layinsu, " kai nabeel ina zakane"?
kamar bazai amsa ba sai kuma yace, shago
"wani shagon"?
shagon dinki mana
da mamaki lahab da Ade sukace shagon dinki?har suna had'a baki, don rabon nabeel da shago ai an kwana biyu duk da ya iyya dinki, Amma fa banda had'a kura babu abinda ya iyya inya kakkarba kayan mutane sai ya daina zuwa shago" Amma dai yau mafarki kayi wata zata karka akan kudinta koh"?
kallon Lahab yayi sai kuma yayi murmushi kawai hade dacewa, kun manta kudin jesen jiya da mukayi daku zamu saya.
"eh mun tuna"
toh shiyasa yau zanje shago tunda mun fasa shiga school in naga koh Allah zaisa na samu kafun yamma.
amma Nabeel taya zaka samu 10k a rana d'aya kuma a d'inki gaskiya da wuya.
lahab kam baice kome ba jin Amsar da Ade ya bawa nabeel yasa sa ciro 11k innan a Aljuhunsa mikawa Abokin nasa kudin yayi, "gashi 11k ne ka d'auki dubu goma kuje da Ade kusai jese shima kudinsa na hannunsa 1k in ku hau transport"
da mamaki Ade ke kallon lahab daman haka kullum yake mundin D'ayansu baida abu tsakanin shi da Nabeel haka lahab zai d'au nasa ya basu, toh yanzun kai ina zaka?
da sauri Nabeel ma ya jefo masa tambayar sa shima, toh lahab inna karbi kudin nan kai kuma ka saya dame?
"kallonsu yayi toh tambayar wa zan fara amsawa a cikin ku"?
dukan mu suka basa amsa.
" toh gidan mamina zanje koh zaku rakani ne"?
da sauri sukce Ah ah
ok toh sai kuma maganar kudi, ina da wasu kuje kawai da wannan in, kai kuma Ade bani keken nan naka naje dashi a cikin 1k innan Nabeel ya saya abinci tunda bai karya ba.
godiya nabeel ya masa, bai amsa ba sai harara ya dallara masa, cikin wasa yace"babu godiya a tsakanin mu Abokai ai yiwa kaine, ya karasa maganar da hawa kan keken yaja ya kara gaba, suma da ido suka bisa sai kuma suka wuce bakin titi suka tare keke napep zuwa kasuwa.
lahab kam unguwan da maminsa ke aure ya nufa, unguwane mai kyaun gaske packing yayi a kofar wani tangamemen get, gidane mai kyau Amma baikai gidan su kyau ba, hannu yasa ya bubbuga get in hade da danna hon na kekensa.
maigadi dake zaune a d'akinsa jin bugu ba gaggautawa yasa da sauri ya mike takalminsa ya saka cikin sassarfa ya nufi kofar, kokarin bude kofar yake hade da tambayar wanene.
shuru lahab yayi baiyi magana ba, mai gadin nad'an bude kofar zai leka yaga waye ne da gudu lahab yaja keken yayi cikin gidan saura kad'an ya kade maiganin, da sauri ya basa hanya tsayawa kawai yayi yana bin lahab da ido hade da mamakin ganinsa yau don duk da baya ganesu da d'an uwansa, Amma mundin lahab yazo saiya ganesu a d'abi'a da d'an uwansa ne yana zuwa gaidashi zaifara ba kokarin kad'esa ba, komawa kawai yayi ya rufe kofar ya zaune a benchin dake gefen d'akinsa.
lahab bai tsaya da keken saba har ya wuce compound na gidan sai da ya iso har bakin kofar falon in ya tsaya da kekensa, sauka yayi ya jingina keken ya haura baranda, tura kofar falon yayi koh sallama babu ya duro kansa ciki.
mami dake zaune Akan kujera tana shan fruit salad ne ta bisa da ido harya karaso tsakar falon, fuska ta hade tana kallonsa, koma kayi sallama.
tsayawa yayi kikam yana kallonta ganin yanda ta had'a fuska, bazaka fita bane koh yaya?ta sake maimaita wa.
juyawa yayi a hankali wallahi badon bukatar sa bace ta kawosa da inya fitan nan badai ya kara shigowa ba, komawa yayi ya tsaya a bakin kofar, da karfi ya kwala sallama.
Girgiza kai kawai mami tayi jin mannin hauka da lahab yake, amsawa tayi tare da bashi izinin shigowa, ba musu ya shigon, zama yayi a cikin d'aya daga cikin kujerun falon yana kallonta"ina kwana mami"?
Lafiya lahab ashe ana ganin ku?
"Eh mami bagani ba"
Ah ah bukatar ka dai ta kawoka ba zuwan Allah Annabi bane wannan, yasu Addayiya da sauran yan uwan naka da iyaye?
"Suna lafiya mami sun mace suna gaidake"
kadaiji tsoron Allah wallahi taima ma babu wanda yasan kayi hanyar gidan nan, gashidai safiyar jumma'a ce kowani yaro yana makaranta war haka amma kai kana gantali da abokan shashancin nan naka?
"Wallahi mami yaune na tashi kafad'ata na ciwo shiyasa Abbu yace kar naje makaranta"
rufemini baki shashasha kawai Abbun kake ma karya koh sa'anka ne taya za'ace kai kullum cikin case kake, kai ba zuwa makaranta ba kai ba sana'ar baki ba bare fari, sai yawon kamar kare, da ball kai koh kishi bakaji yanda kowa ke yabon yalin d'an uwanka Rahab.
Had'a fuska yayi don shi a duniya ya tsani in za'a masa fad'a ace ya kwaikwayi Rahab abin haushi yake basa.
Ka had'a fuska da kyau, gaskiya na fad'a ai yaron nan ya fika hankali babu ranan jumma'a da yamma daba zaizo wajena ba ya gaidani, yanzun kai tsakani da Allah rabonka da gidan nan tun yaushe?
Fuska a hade yatsungunar da kai, shuru yayi baice kome ba shidai sai Allah Allah yake kartazo ta hanasa kudin nan,"kiyi hakuri mami zanna zuwa kullum insha Allah"
ALKAWARIN KA ai ba Alkawari bane sau nawa kana mini Alkawari kana karyawa, Yanzun sau nawa kanace mini xaka daina saka Addayiya surutu Amma ka daina inne? hatta jiya da Umaimah tazo gidan nan saida ta bani labarin abubuwan da kake musu a gida anya lahab zakayi hankali kuwa, shekara 18 ace mutum baisan inda ke masa ciwo ba?
Shuru yayi yaki tanka mata don shi irin mutanen nan ne da holo baya damunsu sam ga rashin zuciya, koh fad'a kukayi da lahab zuwa anjima ya watsar abinsa, ya cigaba da rayuwar sa baya sakawa kansa tention.
Ganin yanda yayi zuru yana sauraronta kamar radio yasa ta yin shuru kawai, tana kallonsa.
Shima d'aga ido yayi ya kalleta jin ta daina fad'ar had'a ido sukayi da sauri ya sunkuyar da kai yana kaikaya gashin geyarsa"uhmm ayya mamina my only mother ki taimaka mini da 20k mana momcy"ya karasa maganar cikin Alamun a tausaya masa.
Kama baki mami tayi tana kallonsa, uban me zakayi da 20k lahab?
"Wallahi mami so nake na sayi wasu kayane"
Kaya lahab?wani irin kayane baka dashi a gidan ku?daga na banza harda na kirki sanan kazo kace na baka kudi, badai kaya bakam kadaisan me zakayi da kudin, toh bara na fad'a maka lahab bazan baka koh sisi ba kaji na fad'a maka, bazaiyu Yayan ka yana kirana yana mini masifa ina bata ka da kudi b, a badani ba kaji na fad'a maka.
Mikewa lahab yayi tunda yaji mami tace bazata bayar ba toh fa magana ya kare kenan, tafiya ya fara cikin jin ba dadi.
Dawo nan lahab, ba musu ya dawo ya tsaya ka karya kuwa?
"Ah ah"
Toh wuce kitchen akwai abinci ka iba.
Girgiza kai kawai lahab yayi alamun bazaici ba.
Ina wasa da kai?
"Ah ah mami"
Toh karkasa na maimaita kalamaina wuce akwai abinci a kitchen ka iba kazo ka zauna kaci nasan tunda ka fito ba uniform toh nasan baka karya ba, Shiyasa nake Allah Allah muzammil ya dawo shine daidai da kai wuce ka bani waje...