Sashe 14
Alkawarin Masoya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Turus suka tsaya a gabanta suna maida numfashi yanda karnuka keyi ba tare da sun mata kome ba, juyawa tayi tana kallon shayibu sai kuma ta nuna masa da yatsa akan ya tawo su shiga, ba musu ganin babu abinda yan iskan karnukan suka mata, ya karaso wajen Yana mamakin yanda kule yaga kare Amma bai wani razana ba, suma karnukan badu nuna yunwar su ba.
Nnenna ne a gaba hannu tasa ta tura kofar karfen shayibu na binta a baya karnukan ma suka bisu, tsayawa Nnenna tayi a tsakar gidan tana bin koh ina da kallo wai wannan gidan ne zata xauna a ciki?koh a mafarki bata taba tsammani ba.
Kofar falon shayibu ya isa yayi knocking kusan sau uku kafun suka koma gefe suka tsaya, sai da aka jima kafun sukaji ana kokarin bude kofar, ana budewa dukansu suka dubi na bakin kofar mace ce Christian budurwa a kalla zata kusa 25 sanye da zani guntu sai t-shirt koh ba'a fad'aba daga mutum ya ganta yasan yar aiki ce.
Da sauri taja baya tana kallonsu suma da sauri suka gaidata, Amsawa tayi a yangace tare da tambayar su lafiya me suke bukata?
Kallonta shayibu yayi cikin turanci yake ce mata ta musu iso a wajen pastor Coulis Appa wajen sa sukazo, kamar bazata ba sai binsu take da kallo, kafun ta koma ciki sai da ta jima kafun ta dawo tace musu su shigo ciki.
Ba musu Nnenna tabiyo ta a baya shayibu na binsu har suka shigo falon, wow falone mai kyau d'auke da Jere na zamani kujeru da kayan Alatu daidai karfin masu gidan don baza'ace azabebben kyau ba, zama yar aikin tace suyi a falo ita kuma ta wuce kitchen.
Daga Nnenna har shayibu a kasa suka zauna watoh kasan tiles, basu hau kujera ba, sai kallon falon Nnenna keyi daga ka ganta kasan bakauyiya ce.
Sai da suka d'auki akalla 1 hour a zaune duk sun gaji kafun suka ji karan takalmin mutum a upstair's, Gabaki d'aya suka bi matakalar da kallo, wani mutumi ne baki d'an lukuti ga tumbi ke saukowa daga ka gansa kasan lallai irin pastotin nan ne rikako, kamar yanda suka zura masa ido shima haka ya zura musu ido yana kallonsu har ya gama saukowa musamman ma daya ga shayibu don dagani babu tambaya Annurin musulunci daban ne.
Kallon Nnenna yake ganinta babu d'an kwali ga wando a jikinta na gwanjo da t-shirt sai dai basu kamata ba, hakan ya tabbatar masa ba musulma bace kuma yayi matukar mamakin kamarta kyaun nata na taban ne koh nace na musamman.
Zama yayi akan kujera yayi bake-bake yana binsu da kallo da sauri shayibu ya sunkuyar da kai yana gaidashi, Amsawa yayi kamar bayaso, hade da tambayar su lafiya suke neman sa?
Gyara zama shayibu yayi ya koro masa bayanin haduwar sa da Nnenna tare da takardan da ta basa tana neman d'an uwan babanta daga Enugu, rike baki yayi yana kallon Nnenna sai kuma ya nunata da yatsa, kee kece yar Obinna taya kika zama Yar Obinna dubeki fa.
Kuka ne ya kwace wa Nnenna a tunanin ta koh in tazo zata samu tarba mai mutunci itama karshen wahakar ta kenan ta huta da wahalan rayuwa ashe ta gudu ne bata tsira ba.
Mika hannu yayi, ku bani takardan ai zan gane rubutun Obinna duk da shekaru da dama rabona dashi Bana tunanin zan manta?
Ba musu Shayibu ya zaro paper ya basa, ba musu ya karba yana bin rubutun da ido sai kuma ya d'aga kai yana kallon Nnenna, yaren Egbo ya fara mata don tabbatar wa kansa yar d'an uwan sane, tambayoyi yake mata tana basa Amsa harda tambayar ta mahaifiyar ta fa, tace masa bata san taba, amma bata sanar dashi ana mata kazafin maita ba, hade da mamakin halinsa na koh in kula da jin labarin mutuwar Obinna gashi dai ita tunda take bata taba ganinsa a kauyen suba, Amma ga kaman nin papa nan a fuskar sa.
Koh godiya baima shayibu ba na kula da Nnenna da yayi jiya sai ma kwalama mai aiki kira yayi, Akan tazo ta nunawa Nnenna d'akin baki dake kasan falon, yana maganar ya haura sama abinsa, da sauri ta fito hade dama Nnenna iso suje ta kaita dakin.
Mikewa shayibu yayi bayan fitan coulis hannu yasa a Aljuhu ya zaro kudin ya mikawa Nnenna girgiza kai tayi a hankali cikin dauriya tace,"Am sory sir da abinda Uncle nawa ya maka nasan bai kyauta ba, kudin nan kuma ka rike a hannunka kayi business dashi na baka rabi kudin nima ka juya mini nawa nima, wata rana in bukatar kudi ya kamani nasan gidan ka zanzo"
Kin karba yayi sai da tayi da gaske kafun ya karba yana mata godiya tare da mata Alkawarin zuwa ya dubata hade da mata nasiha akan hakuri da rayuwa aduk yanda yazo mata.
Rakasa tayi har kofar get in hannunta d'auke da kulenta ta dawo falon, kofar da taga mai aikin ta shiga tun d'azun gun ta nufa ta bude, dakine d'an madaidaici mai d'auke da gado daidai na mutum biyu, sai labulaye da aka zaga d'akin dashi, fita mai aikin tayi, da sauri Nnenna ta matsa jikin labulen ta kama ta yaye sai kuma ta rike baki ashe glass dake wajen nan cikinsa ne, dakin ta tan kallon unguwan baki d'aya daga dakin ta inta yaye labule, sosai taji dadin dakin koh banza zai rage mata kewa.
Turo kofar akayi da sauri ta juya tana kallon mai aikin hannunta d'auke da tiren abinci aje mata tayi akan tiles tare da nuna mata wardrop dake gefe akan tasa kayanta dake laida a ciki, tare da nuna mata bayan gida da yanda zatayi amfani da kayan ciki fuska ba walwala yar aikin ke mata magana, tana gamawa ta fita daman ita Nnenna koh fuska bata sakar mata ba daman ita ba ma'abociyar fara'a bace bare ta damu.
Aje kulen tayi akan gado da sauri ta bude abincin Arish ne da kwai sai bread da tie sosai taji dadi wallahi gyara zama tayi ta fara cin abincin ta har lumshe ido take don ba sabawa tayi da cin suba, daga ita har kulenta sukeci tare a kwano d'aya.
Tana gama ci toilet ta shiga tsintsiya ta d'auko tazo ta share dakin ga basket a ciki ta juye sharan, wanka tayi ta gyara gadon ta kwanta abinta tana maijin dadin sauyin rayuwa data samu da fatan kasancewa cikin kwanciyan Hankali.
Har dare tana d'akin bata tashi ba duk da taji tsayuwar mota a tsakar gidan don duk abinda ke faruwa a waje tana d'anji kad'an-kad'an saboda glass.
Yar aikin ne ta shigo tare da sanar da Nnenna tafito ana nemanta a falo, da sauri ta mike sanye take da dogon riga d'aya daga cikin wanda shayibu ya sai mata, kofa ta nufa zata fita ai da sauri kulenta dake kwance a gadon ya mike zai bita.
Da sauri ta nuna masa gadon cikin yare tace masa ya koma ya kwanta, ba musu kuma ya koma ya kwantan Abinsa kamar yanda tace, bin yar aikin tayi har falo, ji tayi zuciyar ta ya tsinke ganin mutanen dake falon, uncle Coulis ne zaune akan 3sita da wata tasha bleching ga attech akanta, sai wasu yara mata biyu dake zaune da kananun gajerun wanduna d'ayan zata kai shekara 23 sai karamar mai shekara 17, sai namijin dake zaune a 1sita daga ka gansa kaga dan iska bakin nan bakikirim irin na yan kwaya sai ido jajazur zai kai 30, daga ka gansu kaga irin shagwababun yaran nan babu kob'a, gashi tunda Nnenna ta fito yake binta da wani mayace cen kallo yana lasar baki.
Rakuba tayi a gefe cikin rawan jiki take gaida matar"good Evening ma"?
Amsa mata tayi hade da sanar da ita ba ma zatace ba mom yaranta ke kiranta, ta karasa maganar cikin yanga kai kawai Nnenna ta daga mata alamun taji gaida sauran yaran tayi harda uncle nata.
Kallon ta Dady yayi cikin yare ya nuna mata mom, ga wife ina sunan ta chidimma Doctor ce, sai wannan ya nuna na mijin sunan sa ibraham yana karatu a kasar waje Amma yanzun ya dawo hutu, my first born.
Nuna yaran matan yayi wannan sunan ta Sarah ta kusan kammala digree inta sai mai binta jennifer tana sss 3, ni kuma pastor ne, na fada miki ne don ki san mu da kyau, kuma zansa a je amin bincike a kauye kamar yanda Dr tace saboda na tabbatar dake din yar uwa tace, ganinki da nayi da muslim nan hankali na bai kwanta dake ba?
Gyada kai tayi hawaye na taruwa a idanunta tsoro take ji kar yaje yaji zancen mayyace ita shima ya korata a gidan nasa, bata dawo daga tunaninta ba mom ta kalleta cikin gatse tace ke tashi kije ki jera mana abinci a daining ba zaman banza zakiyi a gidan nan ba dole yanzun na sallame Lakwanti ke ki maye gurbinsa a ayyuka, keda peace kun isa tayi na kitchen kiyi na gida.
Gaskiya ne mom bazayu tana yar kauye muci mu kwanta ita ma haka ba, sarah tace tana yamutsa fuska cikin rigima, guy innan kam maida Nnenna yayi madubi sai kallonta yake yayin da jennifer taji wani irin tsanar Nnenna a ranta ganin yarinya yar kauye tazo ta fita kome da kome gata kyakkyawa, bare ma yanzun dataji dad na cewa bayan anyi bincike ya tabbtar yar obinna ce har makaranta zai saka ta.
Da murna Nnenna kece masa takardun ta na gidan su pls in za'aje garin nasu a d'auko mata.
Tsawa mom ta daka mata ke yar kauye dakata menaji kike cewa? ta tambaya tana nuna Nnenna, yaushe kika samu waje har zaki bada order shege ya.
Sosai Nnenna ta razana don itakam harga Allah batason tsawa, nuna mata kitchen mom tayi wuce kije ki taya Peace aiki, ba musu ta mike a hankali take tafiya Ibraham sai binta yake da ido kamar tsohon maye.
Nnenna ne a gaba hannu tasa ta tura kofar karfen shayibu na binta a baya karnukan ma suka bisu, tsayawa Nnenna tayi a tsakar gidan tana bin koh ina da kallo wai wannan gidan ne zata xauna a ciki?koh a mafarki bata taba tsammani ba.
Kofar falon shayibu ya isa yayi knocking kusan sau uku kafun suka koma gefe suka tsaya, sai da aka jima kafun sukaji ana kokarin bude kofar, ana budewa dukansu suka dubi na bakin kofar mace ce Christian budurwa a kalla zata kusa 25 sanye da zani guntu sai t-shirt koh ba'a fad'aba daga mutum ya ganta yasan yar aiki ce.
Da sauri taja baya tana kallonsu suma da sauri suka gaidata, Amsawa tayi a yangace tare da tambayar su lafiya me suke bukata?
Kallonta shayibu yayi cikin turanci yake ce mata ta musu iso a wajen pastor Coulis Appa wajen sa sukazo, kamar bazata ba sai binsu take da kallo, kafun ta koma ciki sai da ta jima kafun ta dawo tace musu su shigo ciki.
Ba musu Nnenna tabiyo ta a baya shayibu na binsu har suka shigo falon, wow falone mai kyau d'auke da Jere na zamani kujeru da kayan Alatu daidai karfin masu gidan don baza'ace azabebben kyau ba, zama yar aikin tace suyi a falo ita kuma ta wuce kitchen.
Daga Nnenna har shayibu a kasa suka zauna watoh kasan tiles, basu hau kujera ba, sai kallon falon Nnenna keyi daga ka ganta kasan bakauyiya ce.
Sai da suka d'auki akalla 1 hour a zaune duk sun gaji kafun suka ji karan takalmin mutum a upstair's, Gabaki d'aya suka bi matakalar da kallo, wani mutumi ne baki d'an lukuti ga tumbi ke saukowa daga ka gansa kasan lallai irin pastotin nan ne rikako, kamar yanda suka zura masa ido shima haka ya zura musu ido yana kallonsu har ya gama saukowa musamman ma daya ga shayibu don dagani babu tambaya Annurin musulunci daban ne.
Kallon Nnenna yake ganinta babu d'an kwali ga wando a jikinta na gwanjo da t-shirt sai dai basu kamata ba, hakan ya tabbatar masa ba musulma bace kuma yayi matukar mamakin kamarta kyaun nata na taban ne koh nace na musamman.
Zama yayi akan kujera yayi bake-bake yana binsu da kallo da sauri shayibu ya sunkuyar da kai yana gaidashi, Amsawa yayi kamar bayaso, hade da tambayar su lafiya suke neman sa?
Gyara zama shayibu yayi ya koro masa bayanin haduwar sa da Nnenna tare da takardan da ta basa tana neman d'an uwan babanta daga Enugu, rike baki yayi yana kallon Nnenna sai kuma ya nunata da yatsa, kee kece yar Obinna taya kika zama Yar Obinna dubeki fa.
Kuka ne ya kwace wa Nnenna a tunanin ta koh in tazo zata samu tarba mai mutunci itama karshen wahakar ta kenan ta huta da wahalan rayuwa ashe ta gudu ne bata tsira ba.
Mika hannu yayi, ku bani takardan ai zan gane rubutun Obinna duk da shekaru da dama rabona dashi Bana tunanin zan manta?
Ba musu Shayibu ya zaro paper ya basa, ba musu ya karba yana bin rubutun da ido sai kuma ya d'aga kai yana kallon Nnenna, yaren Egbo ya fara mata don tabbatar wa kansa yar d'an uwan sane, tambayoyi yake mata tana basa Amsa harda tambayar ta mahaifiyar ta fa, tace masa bata san taba, amma bata sanar dashi ana mata kazafin maita ba, hade da mamakin halinsa na koh in kula da jin labarin mutuwar Obinna gashi dai ita tunda take bata taba ganinsa a kauyen suba, Amma ga kaman nin papa nan a fuskar sa.
Koh godiya baima shayibu ba na kula da Nnenna da yayi jiya sai ma kwalama mai aiki kira yayi, Akan tazo ta nunawa Nnenna d'akin baki dake kasan falon, yana maganar ya haura sama abinsa, da sauri ta fito hade dama Nnenna iso suje ta kaita dakin.
Mikewa shayibu yayi bayan fitan coulis hannu yasa a Aljuhu ya zaro kudin ya mikawa Nnenna girgiza kai tayi a hankali cikin dauriya tace,"Am sory sir da abinda Uncle nawa ya maka nasan bai kyauta ba, kudin nan kuma ka rike a hannunka kayi business dashi na baka rabi kudin nima ka juya mini nawa nima, wata rana in bukatar kudi ya kamani nasan gidan ka zanzo"
Kin karba yayi sai da tayi da gaske kafun ya karba yana mata godiya tare da mata Alkawarin zuwa ya dubata hade da mata nasiha akan hakuri da rayuwa aduk yanda yazo mata.
Rakasa tayi har kofar get in hannunta d'auke da kulenta ta dawo falon, kofar da taga mai aikin ta shiga tun d'azun gun ta nufa ta bude, dakine d'an madaidaici mai d'auke da gado daidai na mutum biyu, sai labulaye da aka zaga d'akin dashi, fita mai aikin tayi, da sauri Nnenna ta matsa jikin labulen ta kama ta yaye sai kuma ta rike baki ashe glass dake wajen nan cikinsa ne, dakin ta tan kallon unguwan baki d'aya daga dakin ta inta yaye labule, sosai taji dadin dakin koh banza zai rage mata kewa.
Turo kofar akayi da sauri ta juya tana kallon mai aikin hannunta d'auke da tiren abinci aje mata tayi akan tiles tare da nuna mata wardrop dake gefe akan tasa kayanta dake laida a ciki, tare da nuna mata bayan gida da yanda zatayi amfani da kayan ciki fuska ba walwala yar aikin ke mata magana, tana gamawa ta fita daman ita Nnenna koh fuska bata sakar mata ba daman ita ba ma'abociyar fara'a bace bare ta damu.
Aje kulen tayi akan gado da sauri ta bude abincin Arish ne da kwai sai bread da tie sosai taji dadi wallahi gyara zama tayi ta fara cin abincin ta har lumshe ido take don ba sabawa tayi da cin suba, daga ita har kulenta sukeci tare a kwano d'aya.
Tana gama ci toilet ta shiga tsintsiya ta d'auko tazo ta share dakin ga basket a ciki ta juye sharan, wanka tayi ta gyara gadon ta kwanta abinta tana maijin dadin sauyin rayuwa data samu da fatan kasancewa cikin kwanciyan Hankali.
Har dare tana d'akin bata tashi ba duk da taji tsayuwar mota a tsakar gidan don duk abinda ke faruwa a waje tana d'anji kad'an-kad'an saboda glass.
Yar aikin ne ta shigo tare da sanar da Nnenna tafito ana nemanta a falo, da sauri ta mike sanye take da dogon riga d'aya daga cikin wanda shayibu ya sai mata, kofa ta nufa zata fita ai da sauri kulenta dake kwance a gadon ya mike zai bita.
Da sauri ta nuna masa gadon cikin yare tace masa ya koma ya kwanta, ba musu kuma ya koma ya kwantan Abinsa kamar yanda tace, bin yar aikin tayi har falo, ji tayi zuciyar ta ya tsinke ganin mutanen dake falon, uncle Coulis ne zaune akan 3sita da wata tasha bleching ga attech akanta, sai wasu yara mata biyu dake zaune da kananun gajerun wanduna d'ayan zata kai shekara 23 sai karamar mai shekara 17, sai namijin dake zaune a 1sita daga ka gansa kaga dan iska bakin nan bakikirim irin na yan kwaya sai ido jajazur zai kai 30, daga ka gansu kaga irin shagwababun yaran nan babu kob'a, gashi tunda Nnenna ta fito yake binta da wani mayace cen kallo yana lasar baki.
Rakuba tayi a gefe cikin rawan jiki take gaida matar"good Evening ma"?
Amsa mata tayi hade da sanar da ita ba ma zatace ba mom yaranta ke kiranta, ta karasa maganar cikin yanga kai kawai Nnenna ta daga mata alamun taji gaida sauran yaran tayi harda uncle nata.
Kallon ta Dady yayi cikin yare ya nuna mata mom, ga wife ina sunan ta chidimma Doctor ce, sai wannan ya nuna na mijin sunan sa ibraham yana karatu a kasar waje Amma yanzun ya dawo hutu, my first born.
Nuna yaran matan yayi wannan sunan ta Sarah ta kusan kammala digree inta sai mai binta jennifer tana sss 3, ni kuma pastor ne, na fada miki ne don ki san mu da kyau, kuma zansa a je amin bincike a kauye kamar yanda Dr tace saboda na tabbatar dake din yar uwa tace, ganinki da nayi da muslim nan hankali na bai kwanta dake ba?
Gyada kai tayi hawaye na taruwa a idanunta tsoro take ji kar yaje yaji zancen mayyace ita shima ya korata a gidan nasa, bata dawo daga tunaninta ba mom ta kalleta cikin gatse tace ke tashi kije ki jera mana abinci a daining ba zaman banza zakiyi a gidan nan ba dole yanzun na sallame Lakwanti ke ki maye gurbinsa a ayyuka, keda peace kun isa tayi na kitchen kiyi na gida.
Gaskiya ne mom bazayu tana yar kauye muci mu kwanta ita ma haka ba, sarah tace tana yamutsa fuska cikin rigima, guy innan kam maida Nnenna yayi madubi sai kallonta yake yayin da jennifer taji wani irin tsanar Nnenna a ranta ganin yarinya yar kauye tazo ta fita kome da kome gata kyakkyawa, bare ma yanzun dataji dad na cewa bayan anyi bincike ya tabbtar yar obinna ce har makaranta zai saka ta.
Da murna Nnenna kece masa takardun ta na gidan su pls in za'aje garin nasu a d'auko mata.
Tsawa mom ta daka mata ke yar kauye dakata menaji kike cewa? ta tambaya tana nuna Nnenna, yaushe kika samu waje har zaki bada order shege ya.
Sosai Nnenna ta razana don itakam harga Allah batason tsawa, nuna mata kitchen mom tayi wuce kije ki taya Peace aiki, ba musu ta mike a hankali take tafiya Ibraham sai binta yake da ido kamar tsohon maye.