← Book details Alkawarin Masoya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 122

Sashe 21

Alkawarin Masoya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kyalesa yaje ya kashe sa addayiya koh an bar lahab baxai hana gobe yayi abinda yafi haka ba, tunda dai zai iyya kwakwayon d'an uwan sa har ana gallaza masa, mami tace tana share hawaye bawai abinda xa'ama lahab ne yasata kuka ba sai tuna mahaifin su lahab, da ace yana raye babu wanda ya isa ya d'aura hannu akan 'ya'yan sa.

Muzammil koh kulasu baiyi ba kawai ya bude kofar zai tura lahab, da gudu Rahab yazo ya kama kafar sa tare da dukar da gwuwar sa a kasa cikin kuka yake magana don Allah uncle kayi hakuri na rokeka ka taimaka, wallahi ni naje na fad'awa mami ne badon a buge lahab ba, kuma nayi farin ciki daya gyara halin sa a kwana d'aya ya zama kamata, dan Allah uncle kayi hakuri karka bugesa gobe nama Alkawari zaije makaranta.

Tsayawa muzammil yayi yana kallon lahab dake tsaye ya wani lonkosu ya rike kwankwaso da hannu d'aya, d'aya hannun kuma ya dafa jikin gini, kana ganin sa kaga taceccen gagare koh alamun nadama babu a fuskar sa, duk da akwai tsoro aran sa amma sam baima bari an gane ba..

A gaskiya Rahab yau in ban ma lahab duka ba zan zame hannu na a lamarin yaron nan, don naga duk abinda yake kuke d'aure masa gindi yake duk abinda yaso.

Shuru duka falon sukayi don wallahi sun san mundin sukace a kyale lahab toh muzammil ya daina saka sa a gaba kenan don sun san muzammil kaifi d'aya ne, basu san wazai jawa lahab birki ba.

Mami ce ta kalli mijin ta Alhaji muje koh tana maganar tana nufar kofar falon, koh kallon muxammil batayi ba tanajin wani irin zafi a ranta, daman haka uwa keji mundin za'a taba lafiyar d'anta koh da kuwa shine da laifi sai dai ta danne xuciyar ta a hukunta shi.

Binta mijinta yayi a baya suka bar gidan uncle jafar ma tafiyar sa yayi Rshab kam sai kuka yake a falo, ganin muzammil yaja lahab zuwa sashen sa.

Extra room na falon sa yakai lahab bell ya d'auka ya dinga laftar sa, amma abin bakin ciki lahab baya kuka kuma baya bada hakuri sai dai kare kansa da yake, sosai Muzammil ya bubuge lahab bana wasa ba ga sashi tsallen kwado da ya ringayi da machine in yamasa taurin kai ya rufasa da duka.

Lahab fa iyya jikita ya jinkita amma taurin rai bai bari ya nuna nadamar sa ba, ruwan sanyi muzammil yaje ya ciko a boket yazo ya kwara masa a jiki cikin daren nan, haka yana zaune bayan wahalar dashi da yayi a haka lahab ya kwana a zaune kuma a jike bashi ya sake saba sai kusan 4 na asuba.

Kasa tashi lahab yayi da rarafe ya ke tafiya kamar yaro mai tete , a haka ya fita a falon ga jikin sa duk ya farfashe amma fuskar sa bai samu kome ba sai idanun sa da suka kumbura na wahala da rashin bacci, a haka har ya ido kofar falon su duk a bude aka bari sanin da akayi yana wajen muxammil, a zaune yasa hannu ya bude kofar da rarrafe ya isa kofar falon su, yana shiga yaga Rahab zaune har lokacin kuka yake d'aga fuskar sa yayi da yayi mugun kumbura ya kalli Lahab da sauri ya mike ya isa garesa.

Lahab sannu wallahi tunda uncle ya wuce da kai ban samu bacci ba, gashi mami ma sai kira take akan ya barka ka dawo amma bai barka ba sai dukan ka yake koh?

"Kamani muje d'aki"lahab yace ba tare daya basa amsa ba, da sauri Rahab ya kamasa da taimakon sa suka shiga dakin daman ba kaya a jikinsa sai wando muzammil ya kwabe jallabiyar.

Har toilet Rahab ya kaisa, " jona mini kettle Rahab"

Da sauri Rahab ya d'au butan ya cika ruwa a ciki ya jona, wandon jikin lahab ya taimaka masa ya cire, ya rage daga shi dai gajeren wando, ganin yanda jikin sa ya zama yasa Rahab kara fashewa da kuka yana d'aukar wayar sa dake ring mami ce.

Hello mami rahab yace cikin muryar kuka

Da sauri mami tace Rahab lahab in ya dawo ne?

Eh mami gashinan wallahi duk uncle ya faffasa masa jiki koh tafiya baya iyyawa mami.

Bashi wayar, mami tace tana hawaye.

Mika ma lahab wayar yayi amma kememen lahab yaki amsar wayan sai ma mugun kallo daya watsawa Rahab.

Kashe wayar kawai lahab yayi yana zare socket na ruwan zafin ajewa yayi ya zaro karamin towel ya aje a gefe, tura kofar yayi ya fita da sauri ya nufi babban falo, Yana shiga kitchen boket ya d'auko a store da roba karami sai gishiri, yana fitowa sukayi kicibis da addayiya.

Da sauri take tambayar sa lahab ya dawo? gyada mata kai kawai yayi ya cigaba da tafiyar sa,itama da sauri tabi bayan sa har dakin su lahab, rahab ya tura kofar toilet in suka shiga.

Ganin jikin lahab yasa addayiya kama baki ta fara kuka tana dafa kirjinsa, wayyo na bonu amanar umar ne haka, amma muzammil anyi azzalumi haka yayi maka lahab tana maganar tana had'a ruwan zafi.

Kala lahab baice ba kansa na sunkuye koh d'agowa baiyi ya ganta ba don itama yau wani mugu-mugun haushin ta yake ji.

Addayiya da rahab su sukayi ta wanke lahab suna gasa masa jiki zuwa 5 na asuba jikin ya d'anyi sauki, Alwala sukayi dukan su a dakin Rahab ya sanyawa lahab wando 3quater addayiya ta shimfida masa sallaya ta fita a dakin.

Daga Rahab har lahab ranan kin zuwa masallaci sukayi a daki sukayi sallah abbu na dawowa sallah ya shigo dakin nasu, a yanayin da yaga jikin lahab yasa sa saurin kiran likita, yazo ya basa maganguna da allurai a take bacci ya d'auke sa, shima Rahab baccin ya koma don jiya baiyi bacci ba kuma yasha Alwashin koh kashesa za'ayi yau bazashi makaranta ba sai lahab yaji sauki.

Gari na waye wa muzammil ya nufo dakin nasu da niyar ya korasu makaranta, yana budewa ya gansu kwakwance a kan katifa, sai addayiya dake gefe a zaune tana gyangyadi jin an budo kofa yasa ta saurin zabura ganin muzammil ne yasa ta mikewa tsaye tana masa nuni da hannu akan ya fita a dakin, fuska a d'aure shima baija zancen ba ya juya ya tafi abinsa.

****************
Ta bangaren Nnenna yau ta tashi a sab'ule koh d'okin zuwa school in batayi ba, tana tashi tayi ayyukan ta kamar ko yaushe kayan makarantan ma bata saka ba sai da Abraham ya shigo ya kara jaddada mata yau zata school.

shiryawa tayi jiki ba kwari ta ibi abinci taci kad'an Dady da kansa ya d'auke ta xuwa school, , jennifer kam kin binsu ma tayi tace bazata bi dady ba mom zata kaita.

Nnenna tunda suka nufi makaranta zuciyar ta ke tsinkewa, wanda bata san dalili ba tana ji kamar akwai wani abu mai muhimmanci dake tinkaro rayuwar ta anan gaba.

Makaranta ne na manya in akace manya ana nufin yayan masu akwai sosai, makaranta mai kyau da tsada daga yanayin ginin makarantan da uniform inda ke sanye a jikin su kome clean ne, ajujuwa ne sama da kasa bini mai hawa uku gashi reshe-reshe gefen science daban Art ban, Amma senior ne kawai babu primary koh jenior.

Packing Dad yayi a packing space na makarantan a hankali Nnenna ta bude marfin motar ta fita Dad ma fita yayi, yana kallon ta tare da sakar mata murmushi, daughter muje koh yanzun fa Almost 7:39pm gyada kai tayi tabi bayan sa har office in principal.

An gama kome harda interview aka mata kuma sun yaba da kokarin ta, ga speak a bakin ta, a take Dad ya mata registration, aka bata takardun makaranta tare da sanar da ita akwai Labrary basai an bata textbook ba, sai da aka gama mata kome kafun aka mikata a sss 3 A.

Tunda Nnenna ta shigo ajin gabaki d'aya 'yan ajin suka bita da kallo sosai suke kallon ta kamar sun samu wata sabuwar halitta, a bench na gaba aka ajeta itama karan kanta ta sargu ganin yanda yara keta binta da ido daga maza har mata.

Wata yar inyamura ce ta matso bench da take cikin yare ta soma mata magana ganin ta Christian kuma kykkyawa haka, atunanin ta Egbo ce, duk da kyawun nata yayi yawa sosai, cikin yare take sanar da ita sunan ta Amarachi?

Gyada kai Nnenna kawai tayi tana kallon yarinyar amma batace kome ba, don dad yau saida ya kara ja mata warning sosai akan mu'amala da mutane ta kuma iyye bakin ta.

Sake tambayar ta yarinyar tayi ita kuma menene sunan ta? mikawa yarinyar takardan ta tayi, ba musu yarinyar ta karba ta duba, sai kuma ta d'ago tana kallon Nnenna, ok ur name is Nnenna obinna from Enugu state abie?

Gyada kai again Nnenna tayi batace kome ba itama Amarachi bata damu ba koh banza zatayi kawance da kyakkyawa,wasu yara biyu ma duk suka zo sukayi joining na Amarachi sai hira suke ma Nnenna, tana binsu da ido kawai duk cikin turanci suke wasu har takardu suka fiffitar, note nasu suka bata wai ta copy aiko da sauri ta karba tana copy abinta.

A haka Jennifer ta shigo class in fuska ba walwala kallon Nnenna tayi dake rubutu sai yara dake gefen ta mata uku maza biyu sai hira suka mata sosai, ranta ya baci ganin daga zuwan Nnenna zata kwace mata jama'a a ajin su,tsawa ta dakawa Nnenna tare da nunata da hannu ke yar kauye tashi mana a bench banza mabaraciya kawai.

Mikewa Nnenna tayi yayin da d'aya daga cikin mazan yace ma Jennifer amma dai ke mahaukaciya ce, ya daga zuwan yarinya zaki wani fara zaginta ubanki yazo da benchi daga gidan kune.

Badai gidan mu ba sai dai gidan ubanka.

Ai kankace me fad'a ya barke tsakanin Jennifer da yaron , sosai yake bugun jennifer kafun aje akira teacher tayi laushi sosai, kafun akazo aka jidesu dukansu akayi staff room dasu.

Ranan koh darasi d'aya jennifer bata samu ba saboda hukunta su da akai a staff aka barsu wuni kas don su school in basa duka sai dai su horar.
Chapter 21 · 0% Book details