Sashe 93
Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Kai... Ai da ya gane da yanzu ya rufe mu, musamman ni kara ita matarsa zai iya daga mata kafa amman ni ina dalilinsa na rufa min asiri? Da ya gane da yanzu wani case din ake ba wannan ba, ai da ba zai tsaya yana min dariya ba”
“Idan kuwa ba haka ba ne, to ina tunanin ya fara sonki, cikin biyu dole ayi daya, idan ba shi ba me zai saka yace a hade abinci a can kuma har ya bukaci ki yi musu girki daga karshe yace za a nema miki makarantar koyon girki?”
“Hmmm Mama Wallahi kara ma ki tubarwa Allah miye Mr Bashir zai yi da ni? Kalleni fa”
“Abiey ma da ya fisa kurciya ya so ki balle shi, kuma shi farin jini ba daga nan yake ba, zaki ga mutum mummuna amman ana sonshi wani kuma ga kyaun ga farin jini, wani kuma ga kyaun ba fari jini, amman ke kina da wannan baiwar yana da wahala ki shiga guri ki fita wani be ce yana sonki ba, yanzu ba ki lura da yadda Sauban ya rufe ido ya take abotar dake tsakaninsa da Abiey ba ya dage yana sonki? Haka nake tunanin Alhajin nan ma ya fada”
“Tabb ai Wallahi Hajiya Jamila zata iya kashe ni, daga ganin wannan matar tana da zafin kishi sosai”
Ashe sara na yi akan gaba ina rufe baki Hajiya Jamila ta banko kofar dakin ta shigo babu ko sallama, daga ni har Mama kallonta muke, a take kirjina ya hau bugawa domin alamunta sun nuna ba da alheri ta shigo ba, Mama ce ta yi karfin halin yi mata magana.
“Hajiya Allah ya sa lafiya?”
“Ina lafiya, yarki na kokari kwace min miji? Ai baki fada min cewar haka yarki take ba da ban aje mu a gida ba, daman dan adam haka yake ka yi masa rana yayi maka dare”
Mama ta yi murmushi irin na manyan mutane masu tsayawa su yi tunani kamin yanke hukunci.
“Hajiya Jamila bana son ranki ya bace akan abun da ya faru, kuma bana son ki yanke hukunci cikin fushi, kishi gaskiya ko wace mace dole ta yi kishi akan mijinta balle kuma ke da kike da miji kamar Alhaji Bashir babban mutun, amman idan kin duba a halin da Zahra take ciki a yanzu ba soyayya ce a gabanta ba”
“Ba zan iya gane wannan ba, ke da ita ban san abun da kuke shiryawa ba, so kuke ku mayar da ni shashasha yarki ta aure min miji ku mallake shi saboda na kawo ku a babban gida ido ya bude, to Wallahi tun wuri ki jawa yarki kunne bakin rijiya ba gurin wasan makaho ba ne, akan miji zan iya komai Wallahi ban yarda wata mace ta zauna da miji ba ko na minti daya, daman ai talaka be iya samun guri ba daga kawo ki sai ki saki jiki kina masa magana kala kala har da wani tahirin mijinki ya mutu ciwon hanta ne ya kashe shi? Wai ke ala dole ya kula ki....”
A fusace na mike tsaye ina kallonta rai a bace.
“Ya isheki haka Jamila, kar fa ki manta ke kika nemi mu dawo gidan nan mu zauna saboda bukatarki, kuma a cikin sharudan da muka gindaya miki kika dauka babu cin mutunci ko cin zarafi a ciki, kuma wannan fadan mijinki ya kamata ki yi ma shi ba mu ba, domin idan be kira ni ba, ba zan je ba kuma idan be tambaye wani abun ba ba zan fada masa ba, kishi ba hauka ba ki daina yarda zuciyarki tana fin karfinki akan abun da be taka kara ya karya ba”
“Ke har kin isa ki fada min abun da zan yi da wanda ba zan yi ba akan mijin? Waye ke? Ke kama kanki saka masa gishiri langaɓu tsada yake, na fi karfin ki yi min wannan Wallahi, kuma na miki kadaidi na farko kuma na karshe akan mijina, ko ido kika sake dagawa kika kalli mijina sai na baki mugun mamaki”
Na kada ido na rausayar da kai ina mata kallon rashin mutunci da tsageranci na ce.
“Ko yanzu mijinki ya aiko kirana sai na tafi, idan har kin isa da shi miyasa baki hana shi ba, sai mu da kika raina zamu zo kina mana masifa kamar wasu bayinki? Taimako kika nema kuma aka yi miki ba bara ko roko muka zo gidanki ba, kuma ke arziki yake tsokarewa ido har kike gani wata zata iya neman shiga gurin mijinki saboda ta samu aurensa akan dukiyarsa, dukiyar da saka kika saye dan wani a matsayin nasa, ni kudi baya burge ni”
“Karki kike, kudin da kika siyar da rayuwa saboda shi zaki ce baya burge ki? Kudin da suka saka aka rushe gidan da kuke zauna sanadin haka aurem uwarki ya mutu na buku umarni kuma kuka bi kuka dawo gidan nan da zama saboda kudi? Kudin da ya saka kika zauna a kujerar dinning dina a dazun kina maganar da ban san ta micece ba da mijina? Ko kike cewa ba ki son kudi? Bari ma miki gargadi na karshe akan mijina zan iya hada yakin duniya na uku Wallahi, babu mace da ta isa ta zauna da mijina matukar ina numfashi, ba dan rainon wayo ba taya zaki zauna a kujerata kina fuskartar mijina kina masa labari ke wai tsaya ma me kuke tattauna ne?”
“Yadda zan fitar da ke a gidan na shiga na zauna, ba mallake duk wani abu da kike takama da shi, Jamila ko da kika dauko ni ba a talauci kika gan mu ba”
Na bata amsa cikin tsiwa ina girgiza jiki kamar gaske.
“Karya kike Wallahi, ke kin san matan da na zauna da su suka bar min miji balle ke? Maganin da kika yi ma Sauban mijin kanwata ya kama shi ni ba zai kamani ko ya kama mijina ba, sannan ina son ku tattara komai na ku ku bar gidan nan kamin dare, taimakon na fasa tun da abun ta zama iskanci”
Magana take tana hakki Hajiya Jamila irin matan nan ne marasa mutunci, irin matan da suke manta alheri a take, jikinta har rawa yake tana matso ni kamar zata kai hannu ta dake ni, kuma da zata taba ni da zata iya kai ni a kasa ta danne domin tana da lafiyayyen jiki irin na manya mata, ba kamar ni ba da za a iya sacewa a gudu. Mama ce ta yi hanzarin shiga tsakiyarmu.
“Barin gida Hajiya Jamila zamu bar shi, amman ina son ki tuna cewar ke kika nemi taimakon Zahra ba mu muka nemi haka ba”
“To yanzu bana bukata, waya sani ko wani asirin kuka ma yaro yaki ya kama nonon kowa sai na Zahra, da yardar Allah babu abun da zai same ni, ki ja yarki ku bar mana gida tun wuri”
“Zamu tafi, amman kar wani abun ya same ki ce zaki waiwaye mu, ba ke ba yata daga yau”
“Daman ai hanyar motar dabam da jirgi dabam”
Ta juya a fuce ta fice daga dakin, ni kuwa na hade hannu cikin isa na ce.
“Babu inda zamu je, sai a yanzu da take ganin ta gama amfana da ni zata ce ta wulakanta mu”
“Saboda me? Ai gidanta ne ita ta kawo mu, yanzu kuma ta bukaci mu bar mata gidanta a dole mu bar mata gidanta, amman ki sani baka maciji baya cizon mumini a rame daya har sau uku, ta yi na farko an yi mata uzuri ta yi na biyu mun tausayawa mata to ba za'ayi na uku ba”
“To yanzu Mama ina zamu koma Fisabilillahi, kina ganin Baba har yanzu be sake waiwayarmu, kuma mun yi ma mutane karya cewar ta ba mu guri mu zauna sai kuma yanzu mu ce ta koremu”
Mama ta fita dakin ba tare da ta ce min komai ba, kayan da muka bata na abinci ta hade guri daya, ta dawo ta shiga bandaki ta wanke jikinta ta fito ta shirya ta saka hijabinta ta dauki jakarta sannan ta kalleni ta ce.
“Ki zauna a dakin nan karki je ko'ina ko ta sake dawowa tana miki masifa karki kula ta”
“Ina zaki je Mama?”
“Gurin yan'uwana zan tafi, sai na dawo”
“Allah ya kiyaye”
Na mata addu'a ba dan daina ya so tafiyar tata ba. Bata wuce minti talatin da fita ba na dauki waya na kira Sauban na sanar masa ina son ganinsa.
“Amman idan ka zo karka shigo cikin gidan ka tsaya daga waje, zan fito na same ka”
“Amman lafiya?”
“Ina son mu yi magana ne akan wani abun”
“Ni ma ina son magana dake, gani nan zuwa”
“Sai ka iso”
Na dauke wayar daga kunne ina jin bakincikin amincewa da na yi muka dawo gidan da zama tun tashin farko, iyakar kokari mun yi na bin dokarta sai dai na lura Hajiya Jamila mace ce mai son milkin kowa ta juya kowa yadda take so kuma ta murje ido kamar ba ta yi ba, alkwarin da ta dauka da dokokin da muka gindaya mata da yarjejeniyar da muka yi kamin na dawo gidan da zama a yau duk ta matasu.
[11/24, 7:23 PM] Oum_Nuwaira🥰: 5️⃣9️⃣
A waya ya sanar da ni cewar yana waje, sai na saka hijabina na janyo kofar na rufe na fito ina ta tararar bangaren Hajiya Jamila, masu gadin shka bude min kofar na fice. Nesa da gidan ya faka kamar yadda na fada masa tun kamin na karasa inda motar take fake ya bude min front seat. Ina zaunawa sai ya kalleni da murmushi a fuskarsa.
“Kullum kyau kike karawa ban san miye sirrin ba”
Ban shiryawa murmushi ba wannan yasa ban yi murmushin ba, domin ba shi ne a gabana ba yanzu, sai na nade hannayena na juyar da fuska ina kara bayyana fushi. Leko fuskata yayi sai ya aje wayar hannunshi ya gyara zama.
“Zahra akwai wata matsala ne?”
Na daga masa kai ina mara turo bakin gaba.
“Ba Hajiya ba ce ba”
“Wace Hajiya?”
“Jamila mana ba ma zan sake cewa Hajiyar ba”
Yayi murmushi.
“Lemme touch kayan Abiey”
“Idan kuwa ba haka ba ne, to ina tunanin ya fara sonki, cikin biyu dole ayi daya, idan ba shi ba me zai saka yace a hade abinci a can kuma har ya bukaci ki yi musu girki daga karshe yace za a nema miki makarantar koyon girki?”
“Hmmm Mama Wallahi kara ma ki tubarwa Allah miye Mr Bashir zai yi da ni? Kalleni fa”
“Abiey ma da ya fisa kurciya ya so ki balle shi, kuma shi farin jini ba daga nan yake ba, zaki ga mutum mummuna amman ana sonshi wani kuma ga kyaun ga farin jini, wani kuma ga kyaun ba fari jini, amman ke kina da wannan baiwar yana da wahala ki shiga guri ki fita wani be ce yana sonki ba, yanzu ba ki lura da yadda Sauban ya rufe ido ya take abotar dake tsakaninsa da Abiey ba ya dage yana sonki? Haka nake tunanin Alhajin nan ma ya fada”
“Tabb ai Wallahi Hajiya Jamila zata iya kashe ni, daga ganin wannan matar tana da zafin kishi sosai”
Ashe sara na yi akan gaba ina rufe baki Hajiya Jamila ta banko kofar dakin ta shigo babu ko sallama, daga ni har Mama kallonta muke, a take kirjina ya hau bugawa domin alamunta sun nuna ba da alheri ta shigo ba, Mama ce ta yi karfin halin yi mata magana.
“Hajiya Allah ya sa lafiya?”
“Ina lafiya, yarki na kokari kwace min miji? Ai baki fada min cewar haka yarki take ba da ban aje mu a gida ba, daman dan adam haka yake ka yi masa rana yayi maka dare”
Mama ta yi murmushi irin na manyan mutane masu tsayawa su yi tunani kamin yanke hukunci.
“Hajiya Jamila bana son ranki ya bace akan abun da ya faru, kuma bana son ki yanke hukunci cikin fushi, kishi gaskiya ko wace mace dole ta yi kishi akan mijinta balle kuma ke da kike da miji kamar Alhaji Bashir babban mutun, amman idan kin duba a halin da Zahra take ciki a yanzu ba soyayya ce a gabanta ba”
“Ba zan iya gane wannan ba, ke da ita ban san abun da kuke shiryawa ba, so kuke ku mayar da ni shashasha yarki ta aure min miji ku mallake shi saboda na kawo ku a babban gida ido ya bude, to Wallahi tun wuri ki jawa yarki kunne bakin rijiya ba gurin wasan makaho ba ne, akan miji zan iya komai Wallahi ban yarda wata mace ta zauna da miji ba ko na minti daya, daman ai talaka be iya samun guri ba daga kawo ki sai ki saki jiki kina masa magana kala kala har da wani tahirin mijinki ya mutu ciwon hanta ne ya kashe shi? Wai ke ala dole ya kula ki....”
A fusace na mike tsaye ina kallonta rai a bace.
“Ya isheki haka Jamila, kar fa ki manta ke kika nemi mu dawo gidan nan mu zauna saboda bukatarki, kuma a cikin sharudan da muka gindaya miki kika dauka babu cin mutunci ko cin zarafi a ciki, kuma wannan fadan mijinki ya kamata ki yi ma shi ba mu ba, domin idan be kira ni ba, ba zan je ba kuma idan be tambaye wani abun ba ba zan fada masa ba, kishi ba hauka ba ki daina yarda zuciyarki tana fin karfinki akan abun da be taka kara ya karya ba”
“Ke har kin isa ki fada min abun da zan yi da wanda ba zan yi ba akan mijin? Waye ke? Ke kama kanki saka masa gishiri langaɓu tsada yake, na fi karfin ki yi min wannan Wallahi, kuma na miki kadaidi na farko kuma na karshe akan mijina, ko ido kika sake dagawa kika kalli mijina sai na baki mugun mamaki”
Na kada ido na rausayar da kai ina mata kallon rashin mutunci da tsageranci na ce.
“Ko yanzu mijinki ya aiko kirana sai na tafi, idan har kin isa da shi miyasa baki hana shi ba, sai mu da kika raina zamu zo kina mana masifa kamar wasu bayinki? Taimako kika nema kuma aka yi miki ba bara ko roko muka zo gidanki ba, kuma ke arziki yake tsokarewa ido har kike gani wata zata iya neman shiga gurin mijinki saboda ta samu aurensa akan dukiyarsa, dukiyar da saka kika saye dan wani a matsayin nasa, ni kudi baya burge ni”
“Karki kike, kudin da kika siyar da rayuwa saboda shi zaki ce baya burge ki? Kudin da suka saka aka rushe gidan da kuke zauna sanadin haka aurem uwarki ya mutu na buku umarni kuma kuka bi kuka dawo gidan nan da zama saboda kudi? Kudin da ya saka kika zauna a kujerar dinning dina a dazun kina maganar da ban san ta micece ba da mijina? Ko kike cewa ba ki son kudi? Bari ma miki gargadi na karshe akan mijina zan iya hada yakin duniya na uku Wallahi, babu mace da ta isa ta zauna da mijina matukar ina numfashi, ba dan rainon wayo ba taya zaki zauna a kujerata kina fuskartar mijina kina masa labari ke wai tsaya ma me kuke tattauna ne?”
“Yadda zan fitar da ke a gidan na shiga na zauna, ba mallake duk wani abu da kike takama da shi, Jamila ko da kika dauko ni ba a talauci kika gan mu ba”
Na bata amsa cikin tsiwa ina girgiza jiki kamar gaske.
“Karya kike Wallahi, ke kin san matan da na zauna da su suka bar min miji balle ke? Maganin da kika yi ma Sauban mijin kanwata ya kama shi ni ba zai kamani ko ya kama mijina ba, sannan ina son ku tattara komai na ku ku bar gidan nan kamin dare, taimakon na fasa tun da abun ta zama iskanci”
Magana take tana hakki Hajiya Jamila irin matan nan ne marasa mutunci, irin matan da suke manta alheri a take, jikinta har rawa yake tana matso ni kamar zata kai hannu ta dake ni, kuma da zata taba ni da zata iya kai ni a kasa ta danne domin tana da lafiyayyen jiki irin na manya mata, ba kamar ni ba da za a iya sacewa a gudu. Mama ce ta yi hanzarin shiga tsakiyarmu.
“Barin gida Hajiya Jamila zamu bar shi, amman ina son ki tuna cewar ke kika nemi taimakon Zahra ba mu muka nemi haka ba”
“To yanzu bana bukata, waya sani ko wani asirin kuka ma yaro yaki ya kama nonon kowa sai na Zahra, da yardar Allah babu abun da zai same ni, ki ja yarki ku bar mana gida tun wuri”
“Zamu tafi, amman kar wani abun ya same ki ce zaki waiwaye mu, ba ke ba yata daga yau”
“Daman ai hanyar motar dabam da jirgi dabam”
Ta juya a fuce ta fice daga dakin, ni kuwa na hade hannu cikin isa na ce.
“Babu inda zamu je, sai a yanzu da take ganin ta gama amfana da ni zata ce ta wulakanta mu”
“Saboda me? Ai gidanta ne ita ta kawo mu, yanzu kuma ta bukaci mu bar mata gidanta a dole mu bar mata gidanta, amman ki sani baka maciji baya cizon mumini a rame daya har sau uku, ta yi na farko an yi mata uzuri ta yi na biyu mun tausayawa mata to ba za'ayi na uku ba”
“To yanzu Mama ina zamu koma Fisabilillahi, kina ganin Baba har yanzu be sake waiwayarmu, kuma mun yi ma mutane karya cewar ta ba mu guri mu zauna sai kuma yanzu mu ce ta koremu”
Mama ta fita dakin ba tare da ta ce min komai ba, kayan da muka bata na abinci ta hade guri daya, ta dawo ta shiga bandaki ta wanke jikinta ta fito ta shirya ta saka hijabinta ta dauki jakarta sannan ta kalleni ta ce.
“Ki zauna a dakin nan karki je ko'ina ko ta sake dawowa tana miki masifa karki kula ta”
“Ina zaki je Mama?”
“Gurin yan'uwana zan tafi, sai na dawo”
“Allah ya kiyaye”
Na mata addu'a ba dan daina ya so tafiyar tata ba. Bata wuce minti talatin da fita ba na dauki waya na kira Sauban na sanar masa ina son ganinsa.
“Amman idan ka zo karka shigo cikin gidan ka tsaya daga waje, zan fito na same ka”
“Amman lafiya?”
“Ina son mu yi magana ne akan wani abun”
“Ni ma ina son magana dake, gani nan zuwa”
“Sai ka iso”
Na dauke wayar daga kunne ina jin bakincikin amincewa da na yi muka dawo gidan da zama tun tashin farko, iyakar kokari mun yi na bin dokarta sai dai na lura Hajiya Jamila mace ce mai son milkin kowa ta juya kowa yadda take so kuma ta murje ido kamar ba ta yi ba, alkwarin da ta dauka da dokokin da muka gindaya mata da yarjejeniyar da muka yi kamin na dawo gidan da zama a yau duk ta matasu.
[11/24, 7:23 PM] Oum_Nuwaira🥰: 5️⃣9️⃣
A waya ya sanar da ni cewar yana waje, sai na saka hijabina na janyo kofar na rufe na fito ina ta tararar bangaren Hajiya Jamila, masu gadin shka bude min kofar na fice. Nesa da gidan ya faka kamar yadda na fada masa tun kamin na karasa inda motar take fake ya bude min front seat. Ina zaunawa sai ya kalleni da murmushi a fuskarsa.
“Kullum kyau kike karawa ban san miye sirrin ba”
Ban shiryawa murmushi ba wannan yasa ban yi murmushin ba, domin ba shi ne a gabana ba yanzu, sai na nade hannayena na juyar da fuska ina kara bayyana fushi. Leko fuskata yayi sai ya aje wayar hannunshi ya gyara zama.
“Zahra akwai wata matsala ne?”
Na daga masa kai ina mara turo bakin gaba.
“Ba Hajiya ba ce ba”
“Wace Hajiya?”
“Jamila mana ba ma zan sake cewa Hajiyar ba”
Yayi murmushi.
“Lemme touch kayan Abiey”