Sashe 31
Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na mike tsaye kamar yadda ta umarta ta juya ta wuce gaba na bi bayanta, muna fitowa dakin sai ta tsaya tana kallona kamar bata taba ganina ba, sannan ta juya ta cigaba ta tafiyar ni kuwa me zan yi idan ba binta ba. Sai da muka fito falon sannan ta nuna min raben wata kujera.
“Je can ki zauna ki jirani zan nuna miki ďakin da zaki zauna”
“Ba zuwa na yi na zauna gaba daya ba, kawai na zo na bashi nono ne na koma”
“Ban gane ki ba shi nono ki koma? Dr Hamid be fada miki abun da na ce ba?”
“Ya fada min, ni kuma na fada masa ba zan zauna a gidanki ba, sai dai na rika ba shi nonon ina komawa”
“Ke Zahra kalleni da kyau, ke kin san ba dan kaddara ba baki isa ma ki tako kafarki a cikin gidan nan ba balle har ki saka min sharadin abun da zan yi da wanda ba zan yi ba”
Tana gama fadin haka ta wuce a fusace zuwa upstairs din a raina sai addu'ar Allah yasa ta fado nake.
*** *** ***
Sai da ta maida kofar bedroom din ta rufe sannan ta juyo ta kalli dan'uwanta dake rike da waya yana tabawa.
“Dr kasan wai mun yi kitso da kwarkwata?”
Ya dago ya kalleta.
“Miye?”
“Wai zaka iya tuna wani hadari da Mr Bashir ya samu kwanan baya jirginsu ya fada a wani kauye?”
“Yes”
“Matar da ta taimaka masa har na fada maka yana ta nemanta”
“Yes you even told me idan kika ganta zaki mata kyauta mi ta yi?”
“Yarinyar nan ce...! Wai ita ce”
Dr Hamid yayi saurin aje wayarta hannunsa gefen kujerar da yake zaune.
“Wasa dai kike”
“I swear to God, yanzu nan ya ganta ya tabbatar da ita ce kuma ita ta fadi cewar shi ne?”
“Wow....”
Dr ya fada kamin ya kyalkyale da dariyar ba zata.
“Ba abun dariya ba ne Dr ina cikin matsala”
A kokarinsa na gintse dariyar ya daga mata hannu.
“Sorry i mean...”
Sai kuma ya sake fashewa da dariya.
“Na rantse abun ne ya bani mamaki dariyar ce take zuwa min a ba zata, so that's mean mun kawo masa ita har gida?”
“Shi ne abun da yake fada”
Dr Hamid yayi gyaran murya still dariyar bata gama fitarshi ba.
“Yanzu yaya kenan?”
Hajiya Jamila ya zauna bakin gadonta tana sauke ajiyar zuciya duk sanyin ac dakin be hana ta jin zafi ba.
“Ina jin tsoron kar ya mata kyautar da zata iya juya tunaninta ta ce zata karbi ďanta, secondly yanzu take fada min cewar wai ba zata zauna a nan ba sai dai ta rika zuwa tana ba shi nono kuma hakan tonon asirina ne, bayan kuma na riga na fada masa cewar a nan zata zauna gashi Ummiter tana gidan idan tana zuwa tana komawa za a iya samun matsala amman idan a nan zata zauna har sai yaron yayi wayo ka ga kullum tana tare da shi babu wanda zai zage nono take ba shi”
“Yeah ta fada min cewar ba zata zauna zaman gaba daya ba”
“Amman baka fada min haka ba, da ban bari ta zo ba har na gabatarda ita gurin Mijina, bana son na yi magana da ita a cikin mutane ne kar ta fara min hauka dan haka ka yi magana da ita ka fada mata a nan zata zauna”
“No idan tana ra'ayin zama a nan har na wani lokacin zata zauna, idan kuma bata ra'ayi ba dole ba ne”
Dr Hamid ya fada with serious face din dake nuna ba da wasa yake ba.
“Ban fahimta ba”
“Ba hakkinta ba ne shayarda yaron nan, ra'ayinta ne idan tana sha'awa dan haka be zama lalle mu cilasta ba”
“Ra'ayinta zamu bi kenan?”
“Yes”
Wani kallon mamaki Hajiya Jamila ta yi ma dan'uwan nata.
“No please kar ma ka nuna mata haka, ita kuma ya kamata ta bi mu dole abun da na ce shi za'ayi kar ma ka barta ta dauka kamar tana da wata damar ba mu umarni mu bi, a nan zata zauna and that's final”
Dr Hamid ya mike tsaye.
“Jamila miyasa kike abu baki tunani ne ko tausayi? Yarinyar nan fa ďanta aka raba ta da shi ďan ma ďan fari a haka ta hakura, yanzu kuma mun je neman ta shayar da yaron nan sai ki fara saka mata wani sharadi, yanzu ita ya kamata saka kuma dole mu bi, dazun ma ina ganin kina fada mata ta zauna a kasa kamar idan ta zauna akan kujerun wani kazanta zata saka musu, ba baiwai ba ce kuma ba aiki take nema ba, shayar da yaron nan kawai zata yi, amman baki fahimci halin da take ciki ba saboda baki taba haihuwa ba baki san yadda uwa take ji ba”
Hajiya Jamila ta hade abu da karfi ta dafa zuciyarta.
“Yau ni kake yi ma gori Yaya? Saboda wata banza? Wata da bata kai ta daga kai ma ta kalleni ba?”
“Ba gori nake miki ba, ni ma uba ne yarana biyu na san yadda take ji, yarinyar nan karamar yarinya ce ta rasa miji kuma yanzu ta rasa ďa hakan kadai be isa ya saka a tausaya mata ba? A haka kuma ta kawo kanta ta shayar da yaron nan amman kina kokarin wulakantata?”
Hawaye ne ya sauko a fuskarta Hajiya Jamila tana kallon Dr Hamid da ke tsaye ransa a bace kamin ya duka ya dauki wayarsa.
“Zata kwana a nan ta shayar da yaron da safe zan dawo na maida ita gidansu, zan yi magana ta fahimta da ita idan ta yarda ta zauna, idan kuma ta ce ba zata zauna ba i won't force her”
Yana kaiwa nan ya fice daga dakin ya barta tsaye hawaye na sauko mata. Tun da take a rayuwarta bata taba jin zafin gorin haihuwa ba irin na yau, Ummiter ta sha yi mata gori haka daidaikun mutane daga familyn mijinta amman ba a taba yi mata gorin haihuwa yayi mata zafi kamar na yau ba, wata kila saboda Dr Hamid dan'uwanta ne na jini, faduwa ta yi kwance saman gadon ta fashe da wani irin kuka har lokacin tana dafe da kirjinta.
“Yau ni Ya Hamid yake yi ma gorin haihuwa saboda wannan jahilar yarinyar, da ta san ciwon ďan zata siyar da shi ne, tun tafiya ba ta yi nisa ba an fara haka, ba zan bari ta zauna a garin nan ba, yarona na yin wayo dole za su bar garin nan gaba daya”
Sai kuma ta tashi zaune tana kallon kofar dakinta.
“..... Ko kuma.... ”
Sai kuma ta yi shiru bata karasa ba ta cige baki. Shigowar Ummiter ne ya saka ta yi saurin share hawayenta ta juya fuska. Ummiter ta dan tsaya jikin kofar tana son fahimtar kuka take ko akasin haka.
“Anty Jamila..”
Ta kira sunanta, sai hakam be saka Hajiya Jamila ta juyo ba domin ta san yadda Ummiter ke mata gulma ko abun da be kai kawo ba balle wannan da zata iya zuwa ta fadawa yayanta cewar ta ganta tana kuka, ko kuma ta jidadin ganinta a halin damuwar saboda ba kaunar juna suke ba ita da Ummiter.
“Anyway Yaya yace Yarinyar da kika dauka aiki ita ce ta taimaka masa lokacin da jirginsu ya fadi, ita na zo gani”
Nan ma Hajiya Jamila bata juyo ba kuma bata ce mata komai ba, Ummiter ta tabe baki ta juya ta fice tare da ja mata kofar ďakin.
ZAHRA POV.
Ina tsaye a inda ta bar ni har ta haye sama, bayan wani lokaci na ga Dr Hamid ya sauko da saurinsa ba dan dai kar ace na yi gulma ba da sai na ce ransa kamar a bace yake wata kila fada suka yi ko kuma wani abun ta fada masa marar dadi oho domin na lura ita ma ba wani dadin zama ne da ita ba. Ina ganin na doshi kofar fita ya fice daga falon na yi hanzarin cira kafa na taka na bi sawunsa, ko da na fita yana daf da bude motarsa sai na kira shi muryar kasa kasa.
“Dr Hamid”
Ya juyo ya kalleni sai ya sakar min murmushi ya rufe motar ni kuma na taka a hankali na karasa kusa da shi.
“Tace wai dole sai na zauna a gidan”
Kai na ga ya daga sama yana kallon ko'ina sannan ya matso kusa da ni kamar zai taba ni.
“Shiga mota mu yi magana gidan nan zagaye yake da security cameras”
Na daga kai ina kallon ko wane kusurwa ta gidan amman ban ga wata alama ta camera ba, na lake kafada alamar ba zan shiga ba, sai yayi murmushi ya kara matsowa kusa da ni ni kuma na dan matsa baya.
“Idan baki bukutar zama ba zan cilasta ki ba, kin fada min ai ba zaki zauna ba ko?”
Na daga masa kai.
“Okay zaki ba shi nonon ne kawai gobe zan zo na maida ke gida, amman dai zamanki zai fi a nan Zahra saboda rufin asirinmu mu duka”
“Jego fa nake yi, sai kuma na bar gidanmu na zauna a nan ai mutane za su min gulma kuma zasu iya ganewa”
“Shikenan idan an yi sati fa? Ko kwana goma?”
“Ni dai ban sani ba”
Na fada ina hade hannayena, murmushi ya sake yi.
“Shikenan idan kin yanke shawara zaki iya fada min a waya ai, and ki yi hakuri da abun da Jamila ta yi miki dazun, ta yi hakan ne saboda muma gaban mutane kuma ta riga ta gabatar da ke a matsayin yar aiki kinji”
Na daga mishi.
“Kin yafe mata”
“Ba wani abu ba ne, daman masu kudi suna hantarar talaka ai, kuma basa son rabarsa talaka kuma ya saba da wannan rayuwar so it's not a big deal”
“Some... Rich people... ”
Ya furta sannan yayi one two three step backwards yana murmushi ya saka hannunsa aljihu yana kallona.
“Good Night”
“Good night”
“Je can ki zauna ki jirani zan nuna miki ďakin da zaki zauna”
“Ba zuwa na yi na zauna gaba daya ba, kawai na zo na bashi nono ne na koma”
“Ban gane ki ba shi nono ki koma? Dr Hamid be fada miki abun da na ce ba?”
“Ya fada min, ni kuma na fada masa ba zan zauna a gidanki ba, sai dai na rika ba shi nonon ina komawa”
“Ke Zahra kalleni da kyau, ke kin san ba dan kaddara ba baki isa ma ki tako kafarki a cikin gidan nan ba balle har ki saka min sharadin abun da zan yi da wanda ba zan yi ba”
Tana gama fadin haka ta wuce a fusace zuwa upstairs din a raina sai addu'ar Allah yasa ta fado nake.
*** *** ***
Sai da ta maida kofar bedroom din ta rufe sannan ta juyo ta kalli dan'uwanta dake rike da waya yana tabawa.
“Dr kasan wai mun yi kitso da kwarkwata?”
Ya dago ya kalleta.
“Miye?”
“Wai zaka iya tuna wani hadari da Mr Bashir ya samu kwanan baya jirginsu ya fada a wani kauye?”
“Yes”
“Matar da ta taimaka masa har na fada maka yana ta nemanta”
“Yes you even told me idan kika ganta zaki mata kyauta mi ta yi?”
“Yarinyar nan ce...! Wai ita ce”
Dr Hamid yayi saurin aje wayarta hannunsa gefen kujerar da yake zaune.
“Wasa dai kike”
“I swear to God, yanzu nan ya ganta ya tabbatar da ita ce kuma ita ta fadi cewar shi ne?”
“Wow....”
Dr ya fada kamin ya kyalkyale da dariyar ba zata.
“Ba abun dariya ba ne Dr ina cikin matsala”
A kokarinsa na gintse dariyar ya daga mata hannu.
“Sorry i mean...”
Sai kuma ya sake fashewa da dariya.
“Na rantse abun ne ya bani mamaki dariyar ce take zuwa min a ba zata, so that's mean mun kawo masa ita har gida?”
“Shi ne abun da yake fada”
Dr Hamid yayi gyaran murya still dariyar bata gama fitarshi ba.
“Yanzu yaya kenan?”
Hajiya Jamila ya zauna bakin gadonta tana sauke ajiyar zuciya duk sanyin ac dakin be hana ta jin zafi ba.
“Ina jin tsoron kar ya mata kyautar da zata iya juya tunaninta ta ce zata karbi ďanta, secondly yanzu take fada min cewar wai ba zata zauna a nan ba sai dai ta rika zuwa tana ba shi nono kuma hakan tonon asirina ne, bayan kuma na riga na fada masa cewar a nan zata zauna gashi Ummiter tana gidan idan tana zuwa tana komawa za a iya samun matsala amman idan a nan zata zauna har sai yaron yayi wayo ka ga kullum tana tare da shi babu wanda zai zage nono take ba shi”
“Yeah ta fada min cewar ba zata zauna zaman gaba daya ba”
“Amman baka fada min haka ba, da ban bari ta zo ba har na gabatarda ita gurin Mijina, bana son na yi magana da ita a cikin mutane ne kar ta fara min hauka dan haka ka yi magana da ita ka fada mata a nan zata zauna”
“No idan tana ra'ayin zama a nan har na wani lokacin zata zauna, idan kuma bata ra'ayi ba dole ba ne”
Dr Hamid ya fada with serious face din dake nuna ba da wasa yake ba.
“Ban fahimta ba”
“Ba hakkinta ba ne shayarda yaron nan, ra'ayinta ne idan tana sha'awa dan haka be zama lalle mu cilasta ba”
“Ra'ayinta zamu bi kenan?”
“Yes”
Wani kallon mamaki Hajiya Jamila ta yi ma dan'uwan nata.
“No please kar ma ka nuna mata haka, ita kuma ya kamata ta bi mu dole abun da na ce shi za'ayi kar ma ka barta ta dauka kamar tana da wata damar ba mu umarni mu bi, a nan zata zauna and that's final”
Dr Hamid ya mike tsaye.
“Jamila miyasa kike abu baki tunani ne ko tausayi? Yarinyar nan fa ďanta aka raba ta da shi ďan ma ďan fari a haka ta hakura, yanzu kuma mun je neman ta shayar da yaron nan sai ki fara saka mata wani sharadi, yanzu ita ya kamata saka kuma dole mu bi, dazun ma ina ganin kina fada mata ta zauna a kasa kamar idan ta zauna akan kujerun wani kazanta zata saka musu, ba baiwai ba ce kuma ba aiki take nema ba, shayar da yaron nan kawai zata yi, amman baki fahimci halin da take ciki ba saboda baki taba haihuwa ba baki san yadda uwa take ji ba”
Hajiya Jamila ta hade abu da karfi ta dafa zuciyarta.
“Yau ni kake yi ma gori Yaya? Saboda wata banza? Wata da bata kai ta daga kai ma ta kalleni ba?”
“Ba gori nake miki ba, ni ma uba ne yarana biyu na san yadda take ji, yarinyar nan karamar yarinya ce ta rasa miji kuma yanzu ta rasa ďa hakan kadai be isa ya saka a tausaya mata ba? A haka kuma ta kawo kanta ta shayar da yaron nan amman kina kokarin wulakantata?”
Hawaye ne ya sauko a fuskarta Hajiya Jamila tana kallon Dr Hamid da ke tsaye ransa a bace kamin ya duka ya dauki wayarsa.
“Zata kwana a nan ta shayar da yaron da safe zan dawo na maida ita gidansu, zan yi magana ta fahimta da ita idan ta yarda ta zauna, idan kuma ta ce ba zata zauna ba i won't force her”
Yana kaiwa nan ya fice daga dakin ya barta tsaye hawaye na sauko mata. Tun da take a rayuwarta bata taba jin zafin gorin haihuwa ba irin na yau, Ummiter ta sha yi mata gori haka daidaikun mutane daga familyn mijinta amman ba a taba yi mata gorin haihuwa yayi mata zafi kamar na yau ba, wata kila saboda Dr Hamid dan'uwanta ne na jini, faduwa ta yi kwance saman gadon ta fashe da wani irin kuka har lokacin tana dafe da kirjinta.
“Yau ni Ya Hamid yake yi ma gorin haihuwa saboda wannan jahilar yarinyar, da ta san ciwon ďan zata siyar da shi ne, tun tafiya ba ta yi nisa ba an fara haka, ba zan bari ta zauna a garin nan ba, yarona na yin wayo dole za su bar garin nan gaba daya”
Sai kuma ta tashi zaune tana kallon kofar dakinta.
“..... Ko kuma.... ”
Sai kuma ta yi shiru bata karasa ba ta cige baki. Shigowar Ummiter ne ya saka ta yi saurin share hawayenta ta juya fuska. Ummiter ta dan tsaya jikin kofar tana son fahimtar kuka take ko akasin haka.
“Anty Jamila..”
Ta kira sunanta, sai hakam be saka Hajiya Jamila ta juyo ba domin ta san yadda Ummiter ke mata gulma ko abun da be kai kawo ba balle wannan da zata iya zuwa ta fadawa yayanta cewar ta ganta tana kuka, ko kuma ta jidadin ganinta a halin damuwar saboda ba kaunar juna suke ba ita da Ummiter.
“Anyway Yaya yace Yarinyar da kika dauka aiki ita ce ta taimaka masa lokacin da jirginsu ya fadi, ita na zo gani”
Nan ma Hajiya Jamila bata juyo ba kuma bata ce mata komai ba, Ummiter ta tabe baki ta juya ta fice tare da ja mata kofar ďakin.
ZAHRA POV.
Ina tsaye a inda ta bar ni har ta haye sama, bayan wani lokaci na ga Dr Hamid ya sauko da saurinsa ba dan dai kar ace na yi gulma ba da sai na ce ransa kamar a bace yake wata kila fada suka yi ko kuma wani abun ta fada masa marar dadi oho domin na lura ita ma ba wani dadin zama ne da ita ba. Ina ganin na doshi kofar fita ya fice daga falon na yi hanzarin cira kafa na taka na bi sawunsa, ko da na fita yana daf da bude motarsa sai na kira shi muryar kasa kasa.
“Dr Hamid”
Ya juyo ya kalleni sai ya sakar min murmushi ya rufe motar ni kuma na taka a hankali na karasa kusa da shi.
“Tace wai dole sai na zauna a gidan”
Kai na ga ya daga sama yana kallon ko'ina sannan ya matso kusa da ni kamar zai taba ni.
“Shiga mota mu yi magana gidan nan zagaye yake da security cameras”
Na daga kai ina kallon ko wane kusurwa ta gidan amman ban ga wata alama ta camera ba, na lake kafada alamar ba zan shiga ba, sai yayi murmushi ya kara matsowa kusa da ni ni kuma na dan matsa baya.
“Idan baki bukutar zama ba zan cilasta ki ba, kin fada min ai ba zaki zauna ba ko?”
Na daga masa kai.
“Okay zaki ba shi nonon ne kawai gobe zan zo na maida ke gida, amman dai zamanki zai fi a nan Zahra saboda rufin asirinmu mu duka”
“Jego fa nake yi, sai kuma na bar gidanmu na zauna a nan ai mutane za su min gulma kuma zasu iya ganewa”
“Shikenan idan an yi sati fa? Ko kwana goma?”
“Ni dai ban sani ba”
Na fada ina hade hannayena, murmushi ya sake yi.
“Shikenan idan kin yanke shawara zaki iya fada min a waya ai, and ki yi hakuri da abun da Jamila ta yi miki dazun, ta yi hakan ne saboda muma gaban mutane kuma ta riga ta gabatar da ke a matsayin yar aiki kinji”
Na daga mishi.
“Kin yafe mata”
“Ba wani abu ba ne, daman masu kudi suna hantarar talaka ai, kuma basa son rabarsa talaka kuma ya saba da wannan rayuwar so it's not a big deal”
“Some... Rich people... ”
Ya furta sannan yayi one two three step backwards yana murmushi ya saka hannunsa aljihu yana kallona.
“Good Night”
“Good night”