Sashe 127
Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Ni ma ba ni da labarinsu a yanzu, domin Dr Hamid ya yanke alaka da ni, ya daina aiki a asibitin da nake aiki a yanzu, kwana kin baya ma na ji ance yayi gobara har ya rasa yarsa daya, amman dai zan bincika na ji”
Na sauke Nimra daga cinyata ina kallonta.
“Amman kina ganin zai fada miki? Bayan Mr Bashir ya rabu da kanwarsa ko kuma ya maida ta ne?”
“Be maida ta ba, ai ba gurin Dr Hamid zan bincika ba, zan tuntubi Mr Bashir din ne da kaina domin har yanzu muna da contact din juna, sai dai mun dade ba mu yi magana ba”
Tana rufe baki ta dauko wayarta ta duba numbersa.
“Allah sarki...”
Ta fada sannan ta miko min wayarta, hoton Amir ne a dp Mr Bashir din, rabin kamanin fuskarsa na fuskata ne, a yayinda rabin kuma ya so ya dauko Deen kuma be yi kama da Deen din sosai ba. A take na cire hoton na turawa kaina ina sharce kwalla.
A daren na kwana da begen ďana na yi kuka sosai kukan da ban san na me zan kira shi ba, tausayin ďana ko tausayin kaina ko kuma na kaunarsa, ko na rashinsa a kusa da ni, a yanzu na fi jin kaunar Amir fiye da da, duk kuwa da kasancewar a yanzu ina da wasu yayan da za su cire min kewarsa, ina ta kallon hoton da aka yi masa tare da yayan turawa yana sanye da kayan sanyi an rufe masa jiki ruf. Washe gari bayan mun karya nake nunawa Abiey hotonsa ina murmushi hawaye na kwaranya daga idona. Sai ya ki karbar wayar a take yanayinsa ya canja.
“Duk damuwar da zaki shiga bata kai wanda iyayensa Deen za su shiga ba, domin su sun rasa ďa kuma ba su da jikan da za su rika kallo a matsayin ďanta”
Na share hawayen.
“Abban Malik ai su ba su san Amir a matsayin jikansu ba, saboda ba su san zafin rashinsa ba, amman ni na sani domin na zauna da shi na shayar da shi dole na san zafin rashinsa”
A lokacin ne Abiey ya kalli kwayar idona yayi min wani kalami marar dadin ji.
“Zahra baki da godiyar Allah, duk kyautar nan da yayi miki baki gode ba sai kin daga hankalinki a kan wani abu can dabam? Hakan yana kara tabbatar min da cewar kina son Deen har gobe”
Na girgiza kai da sauri.
“Ina dai son ďana kuma ina tausayinsa”
Mikewa yayi tsaye ya saka hannu ya dauki ďansa Malik ya fice daga falon zuwa harabar gida, share hawayena na yi na mike tsaye na bi bayansa sai na tsame shi tsaye yana rike da hannayen Malik yana sumbata, na risina a hankali na kwantar da kaina a bayansa.
“I Love My Son”
“I Love You so Much Abban Malik”
Na tari numfashinsa a lokacin da yake furtawa ďansa cewar yana kaunarsa, sai ya juyo ya kalleni ya sumbanci goshina.
“I love you too, je ki dauko min Twins”
Na mike tsaye na dawo falon na janye plate din da suke rigima akansa na goge musu hannayensu na fito da su waje, sai ya hade su su ukun yana wasa da su, ni kam ina tsaye gefe ina kallo kamin na fara shigarwa Twins har muka yi winning shi da ďansa suka fadi. Tun daga ranar sai na tattara lamarin Amir na aje gefe, ba dan bana kaunar ďana ba sai dan na lura kamar maganarsa ko nuna damuwa akansa ya kan haifar da matsala tsakanina da mijina, sai dai a kullum kaunarsa karuwa take a raina, har ta kai wani lokacin idan ina tsaka da tunaninsa na kan kira Malik da sunan Amir, idan Abiey ya ji ranar ba za mu kwana cikin dadin rai ba. Sai dai na kwana ni kaina shi kuma ya kwana da yaransa.
Kauna da shakuwa ta shiga tsakaninmu sosai da Twins wato Nimra da Namra, har ta kai wani lokacin idan zan fita sai dai na fita da su na bar Malik a gida, ko na yi musu abu na kyale Malik, idan Abiey ya gani sai yace ai daman ba son ďansa na ke ba, mutane har basa sanin ba ni ce mahaifiyarsu ba sai wanda ya sani. Tun bayan haihuwar Malik sai haihuwar ta yi min shiru sai da Malik yayi wayo sosai sannan na sake haihuwar Mace.
Rayuwa ta ci gaba da tafiya kamar yadda na dade ina mafarkin ta kasance a gareni, wato cikin kwanciyar hankali da farinciki, ga yarana sai tasawa suke, soyayya tsakanina da mijina kuma kamar domin mu kawai aka hallicce ta, ba ni da wata matsala ta rayuwa a yanzu, soyayya dama da hagu, ba ta bangaren Ammy ba ba ta gurin Momy ba wato mahaifiyar Yasmin ba kuma ta bangaren Mai Martaba ba, ga kuma Mahaifiyata a gafe.
A ranar da Dr ta turo min video da hotunan Amir da Mr Bashir ya turo mata na sha kuka har na gode Allah, sai dai na jidadi sosai sanin cewar ďana yana cikin farinciki da kwanciyar hankali kuma a gurin da zai samu ingantacciyar rayuwa da tarbiya mai kyau. A gurina Baba ya cancanci alheri domin ko ba ya rike mu har girmanmu kuma ya aurarda mu, saboda haka shi ma ya cancanci cin alfarmata, hakan ya saka na biya masa kujerar makka a shekarar da Abiey yayi rabon na sa kujerun ga yan'uwanshi da nawa, mun kusan sati muna fada da juna saboda abin da na yi, a tunaninsa ina kyautatawa Baba ne saboda yana mahaifin Deen, shi kuma a gurinsa ba shi da babba makiyi kamar shi. Baba ya ji dadi sosai yayi ta godiya yana nuna rashin jindadinsa akan abubuwan da suka faru, a sirrance na siya masa wani gidan a makwafin gidansa da aka rusa a wacan lokacin na baya, ta dalilin abun da na yi masa ya dawo yana neman yafiyar Mama har ya share dattin dake tsakaninsu zamansu ya dawo da jindadi fiye da baya.
*** *** ***
Bayan wadansu shekaru...!
A yanzu na gane iyayenmu sun sha wahala na rayuwa da mu, domin tarbiya yara ba abu ne mai sauki ba ko bari bari kawai ya isheka. Ina risine ina sakawa Mahmud safa Abban Malik ya shigo sai da ya fara kaiwa bayana duka sannan ya zauna ina gama saka masa safar ya janyo ni na fado jikinsa.
“Hiayatee ki daina zancen bude gidan abincin da kike a nan”
Na gyara zamana a jikinsa ina taba hancinsa na ce.
“Saboda me?”
“Saboda za mu koma Abuja da zama, sai ki bude a can”
“Abuja kuma?”
“Yes Mai Martaba ya bukaci haka, saboda kula da abubuwansa da suke can, ni kuma i can't say no”
Kwantawa na yi jikinsa a shagwabe na ce.
“Na saba da nan fa Abiey na”
Na mitsike cikina.
“Can din ma ai sabawa zaki yi da mutane”
“Ni dai gaskiya aa, sai dai ka rika zuwa kana dawowa”
“Aa ba wannan maganar sai dai na kwashe yarana na tafi da su, na bar ki a nan ke kadai idan na samu wata yar shala a can na aureta...”
A take na saka hannu na cire hular kansa na jefar na kama kan nashi na kasa a murkushe.
“Ka ma isa, ai Wallahi daga ni ba kari”
“Inji wa? Na yi alkawari da ke?”
“Kana auro wata zan maka hauka, na tashi hankalinka”
“Ni fa yanzu na gama dake, ba dai kin haifa min carbon copy ba?”
Na yi fuska, sai ya fara kyalkyalata har sai da na yi dariya.
“Wasa fa nake, ni na isa na hada Zahra da kishiya? Ke da yayan na ki ai ba za ku bar kishiya ta jidadin zama ba, shiyasa idan mata suka min signal na ke ce musu ni fa na auru tace bata son kishiya”
Ban san lokacin da dariya ta subuce min ba, na rumgume shi, shi ma dariyar yayi ya shafa bayana.
“I love you so much Hiayatee”
“I love you more Zauji”
Na dago fuskata sai ya hade bakinsa da nawa...
_______________________________
THAMMAT BI HAMDILLAH 😍🙏
Na gode Allah da ya ara min lokaci na kawo yanzu, zan yi amfani da wannan damar na nemi yafiyar wadanda na batawa, ayi hakuri a dubi rahmar Allah da jikansa ayi min afuwa. Ina fatar Allah ya yafe mana gaba daya ya hada mu akarkashin inuwar Al'arshensa tare da Manzonsa masoyinmu Annabi Muhammd Sallalahu Alaihi Wassalam
Idan kika karanta littafin nan ba tare da kin biya ni ba ki sani kina da hakki akanki pay 500 to Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008.
And send the evidence of payment to 08036126660
Na sauke Nimra daga cinyata ina kallonta.
“Amman kina ganin zai fada miki? Bayan Mr Bashir ya rabu da kanwarsa ko kuma ya maida ta ne?”
“Be maida ta ba, ai ba gurin Dr Hamid zan bincika ba, zan tuntubi Mr Bashir din ne da kaina domin har yanzu muna da contact din juna, sai dai mun dade ba mu yi magana ba”
Tana rufe baki ta dauko wayarta ta duba numbersa.
“Allah sarki...”
Ta fada sannan ta miko min wayarta, hoton Amir ne a dp Mr Bashir din, rabin kamanin fuskarsa na fuskata ne, a yayinda rabin kuma ya so ya dauko Deen kuma be yi kama da Deen din sosai ba. A take na cire hoton na turawa kaina ina sharce kwalla.
A daren na kwana da begen ďana na yi kuka sosai kukan da ban san na me zan kira shi ba, tausayin ďana ko tausayin kaina ko kuma na kaunarsa, ko na rashinsa a kusa da ni, a yanzu na fi jin kaunar Amir fiye da da, duk kuwa da kasancewar a yanzu ina da wasu yayan da za su cire min kewarsa, ina ta kallon hoton da aka yi masa tare da yayan turawa yana sanye da kayan sanyi an rufe masa jiki ruf. Washe gari bayan mun karya nake nunawa Abiey hotonsa ina murmushi hawaye na kwaranya daga idona. Sai ya ki karbar wayar a take yanayinsa ya canja.
“Duk damuwar da zaki shiga bata kai wanda iyayensa Deen za su shiga ba, domin su sun rasa ďa kuma ba su da jikan da za su rika kallo a matsayin ďanta”
Na share hawayen.
“Abban Malik ai su ba su san Amir a matsayin jikansu ba, saboda ba su san zafin rashinsa ba, amman ni na sani domin na zauna da shi na shayar da shi dole na san zafin rashinsa”
A lokacin ne Abiey ya kalli kwayar idona yayi min wani kalami marar dadin ji.
“Zahra baki da godiyar Allah, duk kyautar nan da yayi miki baki gode ba sai kin daga hankalinki a kan wani abu can dabam? Hakan yana kara tabbatar min da cewar kina son Deen har gobe”
Na girgiza kai da sauri.
“Ina dai son ďana kuma ina tausayinsa”
Mikewa yayi tsaye ya saka hannu ya dauki ďansa Malik ya fice daga falon zuwa harabar gida, share hawayena na yi na mike tsaye na bi bayansa sai na tsame shi tsaye yana rike da hannayen Malik yana sumbata, na risina a hankali na kwantar da kaina a bayansa.
“I Love My Son”
“I Love You so Much Abban Malik”
Na tari numfashinsa a lokacin da yake furtawa ďansa cewar yana kaunarsa, sai ya juyo ya kalleni ya sumbanci goshina.
“I love you too, je ki dauko min Twins”
Na mike tsaye na dawo falon na janye plate din da suke rigima akansa na goge musu hannayensu na fito da su waje, sai ya hade su su ukun yana wasa da su, ni kam ina tsaye gefe ina kallo kamin na fara shigarwa Twins har muka yi winning shi da ďansa suka fadi. Tun daga ranar sai na tattara lamarin Amir na aje gefe, ba dan bana kaunar ďana ba sai dan na lura kamar maganarsa ko nuna damuwa akansa ya kan haifar da matsala tsakanina da mijina, sai dai a kullum kaunarsa karuwa take a raina, har ta kai wani lokacin idan ina tsaka da tunaninsa na kan kira Malik da sunan Amir, idan Abiey ya ji ranar ba za mu kwana cikin dadin rai ba. Sai dai na kwana ni kaina shi kuma ya kwana da yaransa.
Kauna da shakuwa ta shiga tsakaninmu sosai da Twins wato Nimra da Namra, har ta kai wani lokacin idan zan fita sai dai na fita da su na bar Malik a gida, ko na yi musu abu na kyale Malik, idan Abiey ya gani sai yace ai daman ba son ďansa na ke ba, mutane har basa sanin ba ni ce mahaifiyarsu ba sai wanda ya sani. Tun bayan haihuwar Malik sai haihuwar ta yi min shiru sai da Malik yayi wayo sosai sannan na sake haihuwar Mace.
Rayuwa ta ci gaba da tafiya kamar yadda na dade ina mafarkin ta kasance a gareni, wato cikin kwanciyar hankali da farinciki, ga yarana sai tasawa suke, soyayya tsakanina da mijina kuma kamar domin mu kawai aka hallicce ta, ba ni da wata matsala ta rayuwa a yanzu, soyayya dama da hagu, ba ta bangaren Ammy ba ba ta gurin Momy ba wato mahaifiyar Yasmin ba kuma ta bangaren Mai Martaba ba, ga kuma Mahaifiyata a gafe.
A ranar da Dr ta turo min video da hotunan Amir da Mr Bashir ya turo mata na sha kuka har na gode Allah, sai dai na jidadi sosai sanin cewar ďana yana cikin farinciki da kwanciyar hankali kuma a gurin da zai samu ingantacciyar rayuwa da tarbiya mai kyau. A gurina Baba ya cancanci alheri domin ko ba ya rike mu har girmanmu kuma ya aurarda mu, saboda haka shi ma ya cancanci cin alfarmata, hakan ya saka na biya masa kujerar makka a shekarar da Abiey yayi rabon na sa kujerun ga yan'uwanshi da nawa, mun kusan sati muna fada da juna saboda abin da na yi, a tunaninsa ina kyautatawa Baba ne saboda yana mahaifin Deen, shi kuma a gurinsa ba shi da babba makiyi kamar shi. Baba ya ji dadi sosai yayi ta godiya yana nuna rashin jindadinsa akan abubuwan da suka faru, a sirrance na siya masa wani gidan a makwafin gidansa da aka rusa a wacan lokacin na baya, ta dalilin abun da na yi masa ya dawo yana neman yafiyar Mama har ya share dattin dake tsakaninsu zamansu ya dawo da jindadi fiye da baya.
*** *** ***
Bayan wadansu shekaru...!
A yanzu na gane iyayenmu sun sha wahala na rayuwa da mu, domin tarbiya yara ba abu ne mai sauki ba ko bari bari kawai ya isheka. Ina risine ina sakawa Mahmud safa Abban Malik ya shigo sai da ya fara kaiwa bayana duka sannan ya zauna ina gama saka masa safar ya janyo ni na fado jikinsa.
“Hiayatee ki daina zancen bude gidan abincin da kike a nan”
Na gyara zamana a jikinsa ina taba hancinsa na ce.
“Saboda me?”
“Saboda za mu koma Abuja da zama, sai ki bude a can”
“Abuja kuma?”
“Yes Mai Martaba ya bukaci haka, saboda kula da abubuwansa da suke can, ni kuma i can't say no”
Kwantawa na yi jikinsa a shagwabe na ce.
“Na saba da nan fa Abiey na”
Na mitsike cikina.
“Can din ma ai sabawa zaki yi da mutane”
“Ni dai gaskiya aa, sai dai ka rika zuwa kana dawowa”
“Aa ba wannan maganar sai dai na kwashe yarana na tafi da su, na bar ki a nan ke kadai idan na samu wata yar shala a can na aureta...”
A take na saka hannu na cire hular kansa na jefar na kama kan nashi na kasa a murkushe.
“Ka ma isa, ai Wallahi daga ni ba kari”
“Inji wa? Na yi alkawari da ke?”
“Kana auro wata zan maka hauka, na tashi hankalinka”
“Ni fa yanzu na gama dake, ba dai kin haifa min carbon copy ba?”
Na yi fuska, sai ya fara kyalkyalata har sai da na yi dariya.
“Wasa fa nake, ni na isa na hada Zahra da kishiya? Ke da yayan na ki ai ba za ku bar kishiya ta jidadin zama ba, shiyasa idan mata suka min signal na ke ce musu ni fa na auru tace bata son kishiya”
Ban san lokacin da dariya ta subuce min ba, na rumgume shi, shi ma dariyar yayi ya shafa bayana.
“I love you so much Hiayatee”
“I love you more Zauji”
Na dago fuskata sai ya hade bakinsa da nawa...
_______________________________
THAMMAT BI HAMDILLAH 😍🙏
Na gode Allah da ya ara min lokaci na kawo yanzu, zan yi amfani da wannan damar na nemi yafiyar wadanda na batawa, ayi hakuri a dubi rahmar Allah da jikansa ayi min afuwa. Ina fatar Allah ya yafe mana gaba daya ya hada mu akarkashin inuwar Al'arshensa tare da Manzonsa masoyinmu Annabi Muhammd Sallalahu Alaihi Wassalam
Idan kika karanta littafin nan ba tare da kin biya ni ba ki sani kina da hakki akanki pay 500 to Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008.
And send the evidence of payment to 08036126660