← Book details Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 91 OF 127

Sashe 91

Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ba su saurare shi ba suka fara dukanshi duka bana wasa ba, a take hankalina ya tashi sosai na fara kuka ina ba su hakuri sai mutumen ya ce su kyale Deen.

“Tashi ka tafi”

Deen ya tashi ya fara tafiya mutane sai kallon mu suke, sai da yayi nisa da su sannan ya daga muryar ya ce.

“Allah ya isa yan iska yan shaye shaye, mazinatan banza”

Har sauran za su bi bayanshi wanda ke tsaye da ni ya hana su, ya kalleni yana murmushi da zai kwantar min da hankali.

“Ba wani abu za a yi miki ba, ina ne gidanku”

“Gidanmu yana gida”

Yayi dariya yanayin yadda na amsa masa shi ma ya san tsoron nake ji.

“Zo ga motata cen shiga na kaiki gidan”

Ya nuna min wata motar dake fake gefen inda sojojin dazun suke tsaye, bana son na masa gardama yace ni ma zai dake ni, kusan zan iya cewa cilas ce da tsoro ya saka ni aminta na wuce gaba muka isa gurin motar, ya shiga ni ma na shiga muka dauki hanyar unguwarmu ina nuna masa ina share hawaye, har muka isa mutane na ganin motar sojoji har biyu aka watse kowa mamakin ganin motocin sun tsaya kofar gidanmu ake, na ina fitowa cikin motar idon kowa sai yayi kaina gashi har lokacin na kasa daina hawaye domin tsoro ya kamani sosai.

“Shiga gida ki min sallama da Babanki ko Mamanki”

Na nufi cikin gidan ina kuka ina daga bakin kofa na tsaya ina rike da kayan Yaya Maryam dana sato da kuma dan kullin ledar da na dauke dakin Deen na ce.

“Baba wai sojoji sun ce suna sallama da kai a waje”

Baba dake kwance da dauri a kafa da hannu ido daya ma an rufe masa da bandeji da alama mahaukacin nan na dazun ba karamin duka ya sha a hannunshi ba, ya kwalo idon daya ya kalleni.

“So....”

“Joji”

“So...”

“Joji gasu nan a waje har mota uku”

Sai ya fashe da kuka.

“Na shiga uku na lalace ba ni da haihuwa ba ni da shan azaba, ki fita ki fada musu Babanki ya dade da rasuwa, ki ce kakanki ne kawai a gidan kuma tsoho ne ba zai iya fita ba, ni dai Na shiga uku Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un”

Na juya na koma ina hawaye na cewa sojan.

“Wai yace na fada muku Babana ya dade da rasuwa, kakana ne kawai kuma tsoho ne yana kwance ba zai iya fita ba”

Sojan yayi murmushi.

“Shiga ki ce masa to ya mana izini ni zan shigo”

Na juya na koma cikin gidan na tsaya daga bakin kofar gidan na fada musu sakonsa, sai ga Baba dake kwance ya tashi zaune daga nan sai ya mike tsaye da kariyar a kafa ya rika bin gini yana fadin.

“Aniyarki ta biki Zahra, wahalarki sai dai ta ganki ke kadai”

Dakin Mama ya shige ya rufo kofar ya saka sakata, Mama da babu abun da take sai ambaton Allah ta tashi ta shige bandaki tana kuka.

“Yariya kamar yar aljannu ki dauko wannan ki dauko wancan, to na gaji ni ma kin dan san su waye sojoji amman kika je kika taba su, ko sun zo ba zan fito ba Wallahi sai dai na kwana a bandakin nan”

Haka suka bar ni ni kadai a bakin kofar...”

“Zahra....”

Ban kai aya ba Hajiya Jamila ta kira sunana a tsawace, kamar wanda aka sakowa rai haka na zabura saboda tsorata da na yi na kalli upstairs din da take tsaye fuska babu annuri. Da sauri na mike tsaye jikina sai bari baya na yi zan fadi har sai da Mr Bashir dake dariyar labarin da na bashi ya riko hannuna sannan na samu na tsaya daidai.

“Ban miki kasheda da kebewa da mijina ba? Ban gargade ki akan mijina ba?”

Mr Bashir ya daga mata hannu wannan karon murmushi yake, Ummiter ma dake kitchen sai da ta leko tana kallonmu.

“Wife listen ba abun fada ba ne magana ce kawai nake da ita”

Saukowa take kamar ana turo ta.

“Daga jiya zuwa yau ban gane maka ba Hubby wannan abubuwa da kake yi ba hakinka ba ne, kuma ka san zuciyata zata iya cewa bugawa akan haka”

Wani shu'umin murmushi na gani a fuskarsa ya kalleni ya kalleta.

“Matar nan da kike gani, ta taimaki rayuwata kamar yadda ta taimaki rayuwarki a yanzu take kula da ďanki, saboda she deserved respect daga garemu”

“Hubby aikin Zahra kula da Amir ne kawai, ya kamata ka san da wannan”

Magana take hawaye na sauko mata kana ganin ta kasan mace ce mai zafin kishi da bata iya controlling kanta. Barin dinning din yayi ya matsa kusa kusa da ita ya kai hannunshi ya dafa ta.

“Haka kuma Zahra ba baiwa bace, saboda na zauna na yi Magana da ita ko na taimaka mata ba wani abu ba ne, ya kamata ki san da wannan”

Yaja ta jikinshi ya rumgume yana murmushin da ban gama fahimtar manufarsa ba. Ita kuma sai wani gunji take kamar wata zakanya.

“Ummiter idan kin gama ki zubawa Zahra da Mama na ta, mu kuma ki kawo mana na mu”

“Toh”

Ta amsa tana kallon da mamaki sannan ta juya ta shiga kitchen, shi kuma ya kara rumgume matarsa yana aiko min da sakon kyakkyawan murmushi. Ina tsaye a gurin Ummiter ta zuba min nawa ta kawo min na karba da hannu biyu na fice jiki a sanyaye.

ABIEY POV.

“Really Sauban”

Ya fada bayan ya gama sauraren wayar da Sauban yayi da Zahra dazun da safe, bacin rai na biyu kenan Sauban ya saka masa bayan na farkon da ki yarda ya bi umarninsa har yake nuna masa kamar ya fi damuwa da Zahra, gashi har yanzu be kira shi ba be kuma zo ya same shi, and now ya saurari yadda yake kokarin tunkude shi a gurin Zahra. Can kuma yayi murmushi kalaman Zahra sun masa dadi cewar ta kwana da begensa a ranta.

“Soon dear soon zaki zama tawa”

Ya mike tsaye ya fito daga dakinshi ya sauko kasa, Dr Zainab da Ammy dake zaune a kujera daya suka dago suna kallonshi.

“Ammy akwai yadda za'ayi a matso da auren mu da Yasmin kusa?”

Da mamaki Dr Zainab ta ce

“Da gaske?”

“Yes, ina son a rage wata daya din nan a saka shi time din da Mai Martaba yace zai nada ni sarautar Galadima”

“Kana sonta kenan?”

Ammy ta tambaya, sai ya daga kafadunsa ya nufi kofar fita yana amsa mata.

“Daman bana kinta”

Da kallon mamaki suka bishi har ya fice, kai tsaye gurin motarshi ya nufa tun kan ya karasa ya matsa key hannunsa ta yi horn hakan ya sanar da masu gadin gidan fitar gaggawa zai yi, kamin ya juyo har an bude masa gate din yana isa ya fita @360 ya kama hanyar gidan Sauban, ya san by time shi da Sauban basa nisa da gida idan basa tare to ko wannensu yana gida. Abiey na isa gidan Sauban aka bude gate din Sauban ya fito. Sai suka samu gurin gaban gidan suka faka motocinsa, Abiey dake ji da isar Izzar bs fito cikin motar ba sai Sauban ne ya fito ya same shi a motar.

“Gurinka zan tafi”

Abiey be ce masa komai ba, sai kallon gidajen dake gaban na Sauban yake.

“Ban yi abun da ka bukata ba saboda tana cikin damuwa sosai”

Nan ma Abiey be ce masa uffan ba.

“I think something is wrong amman bata fada min ko miye ba”

Abiey ya hade yawu ba tare da ya kalli Sauban ba ya ce.

“Yaushe zaka mata magana?”

“I need to know minene za a mata Barazanar da shi tukuna because bana son na zama silar tashin hankalinta, and ka daina yin abu kamar kana ba ni umarni I'm your friend Abiey not your boy, I'm just helping you”

Abiey yayi wani dan iskan murmushi.

“Idan haka ne ka bi umarnina kawai, so nake a daura auren cikin satin nan”

“Ko da an daura aure akan kudirinka, idan Zahra bata so dole a rabu”

Sai a lokacin Abiey ya kalleshi.

“I have dia every day waiting for this, and you look in to my face and telling idan Zahra bata so dole a rabu?”

“Yes saboda ka yi amfani da ni ka yaudareta, ni zata kalla a matsayin mayaudarin ba kai ba, domin zaka cika na cilastata amincewa ta aure ni a bisa shadin neman mafita i think ba dan tana so na ba”

“Daman ai ba zata so ka ba, Zahra ba zata taba son wani ba sai Abiey da Abiey da Abiey and Abiey only, Man get out of my car”

“You forced me to do this, and now kana kishi? I understand why ka rasa ta da farko because of your foolishness”

Sauban na fada masa haka ya bude motar ya fita, Abiey ya daga kai sama ya runtse ido ya cije baki ya girgiza kai, kamar wanda ya shiryawa mutuwa haka ya fisgi motar ya isa gida cikin bacin rai, ya fito motarsa a daidai lokacin da Dr Zainab take kokarin bude tata motar ta shiga.

“Are you okay?”

Ya nufi inda take tana fadin.

“Wai ni Sauban zai kalla yace min na rasa Zahra because of my foolishness?”

Dr Zainab ta rufe motarta tana kallon bacin rai da kishin dake cin kanenta.

“Maybe he's right, sai da na so hukunta Deen a wacan lokacin ka hana haka ka zuba ido har suka yi zaman aurensu, and now ka dauki kishin Sauban ka saka a zuciyarka bayan duk abun da Sauban yake yi yana yi saboda kai, Abiey karka bari mace ya shiga tsakanku, saboda kar Sauban yayi aure ya barka ka shiga damuwa ya saka yin auren da wuri, kullum cewa yake kai yake jira har sai ka mu matar da kake so, daker familyn suka yi convinced dinsa ya yarda yayi aure, and now ka kawo shawara kana ganin hakan mafita ne a gare but kana son dora masa laifi”
Chapter 91 · 0% Book details