Sashe 100
Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na daga kai na kalli yadda yake jero min bayanin tafiyaraa kamar ance masa ina da alaka da hakan.
“Allah ya huta gajiya, wanne zan fara daga ciki Yallabai, albishir din zan sanar maka ko kuma labarin zan karasa maka”
“Da dai zaki daina kiran Yallabai din nan wata kila da sai kin fi kima a idona, amman kamin nan bari na yi katsalandan ba ki da lafiya ne? Sannan na kira Ummiter kwanan baya na ce ta baki wayar ina son na tambayeki kina son a gyara muku gidan da aka rusa ne ko kuma a siya muku wani amman baki amsa kiran ba why”
Sai a lokacin na gane dalilinsa na neman Ummiter ta kawo wayar da na yi zaton ko zai min maganar abun da na aikata ne da matarsa, a yanzu na gane wautata tabbas da akan haka ne da yanzu hankalin matarsa ya tashi, ni kuma da yake tsoro yayi min yawa sai na yi zaton ko Sauban ne ya fada masa wani abu.
“Alhamdulillah, lafiyar bata wadace ni ba kamar ba, kuma lokacin da ka kira na aje wayar ne na shiga bandaki shiyasa”
Kafa daya ya dora akan dayar yayi wani zama mai kama da kishingida yana kallona.
“Ina da zumuncin na karasa jin labarin abun da iyayenki suka yi a lokaci da sojojin suka ce za su shigo, tun ganin farko da na yi miki na kalli idonki na fahimci kina da wauta da kiriniya da kuma kurciya a tare dake, sai dai ban dauka a cikin labarinki kin wahalar da iyayenki har haka ba ban yi zaton labarin zai saka ni nishadin da na kwana biyu ban yi irinsa ba, Wallahi har a gurin aikin da na tafi idan na tuna murmushi nake, yau dai kam so nake ki karkare min komai sannan albishir din da Matata ta ce ya biyo baya”
Ashe da sauran murmushi a kumatuna da ba san da zamansa ba sai a yanzu da Mr Bashir yake fadar na saka shi nishadi. Na kara natsuwa a zaunen da nake sannan na cigaba da bashi labarin daga inda na dasa aya.
-Ni kadai suka bari tsaye a kofar gidan, da na ga babu sarki sai Allah sai na juya na fada masa cewar Mama ta shige bandaki Baba kuma ya shige daki ya rufe, sai sojan yayi murmushi ya kara matsowa kusa da kofar ya ce.
“Daman fa ba wani abun zan musu ba, ni da nake neman su zama surukaina ina ni ina yi musu wani abu, kawai dai na zo ne saboda na yi magana da su na fada musu cewar ina son yarsu kuma ina son yi min izinin rika zuwa ina magana da ke har mu daidaitu da juna, amman tun da ba su yarda sun fito ba zaki iya musu wannan bayanin albashi idan na dawo kin ga ba sai na sha wahala ba”
“Toh sai anjima”
“Dan jirani ina zuwa”
Ya nufi gurin motarsa ya bude ya shiga ya zauna, sannan ya fito ya nufo ni ya miko min sabbin kudin yan dari biyar biyar za su yi dubu goma, na saka hannu na karba daman can ni bana tsandar kudi ko a hannun waye suka fito kuwa.
“Ki bawa Baban kuma ki sanar masa zan sake dawowa Inshallah”
“Toh”
Murmushi ya sakar min sannan ya juya ya nufi motarsa ni kuma na gyara rikon tufafin Yaya Maryam dake hannuna da dan kwanon naman da Deen ya ba ni daman shi kullin ledar da na sato a dakinsa tana can cikin zanena na laketa yadda ba zata fado ba, sannan na dawo cikin gidan har lokacin Mama na bandaki Baba kuma yana daki ya rufe kansa, karasawa na yi kofar dakin na kara bakina jikin kofar na ce.
“Baba yace ga dubu goma a baka”
“Allah yasa rai yace a kara min Zahra Wallahi ba zan fito dakin nan ba, idan kika ga na fito to safiya ce ta waye a lokacin kam na tabbatar da ya gaji da tsayuwa ya tafi, yaushe kika janyo rigima da mahaukacin nan Fisabilillahi ya zo yayi min tsinannen duka alhalin ban san hawa ba balle sauka, yanzu kuma ki je ki janyo fada da sojoji dungurungun”
“Baba mahaukacin dazun ma shi ya fara fada ni fa, ni kuma na kwashe msa kafafuwa ya fadi shi ne ya biyo ni fa”
“Mahaukaciyar banza, ai kin ma fishi haukar, ni ba zan ma sake magana ba, waya sani ko kina nan tare da shi yana jina”
“Ya tafi fa Baba Wallahi ya tafi”
Baba be sake magana ba, har na gaji na nufi shimfidar da ya tashi na aje tufafin Yaya Maryam na juyo na nufi bandaki na leka Mama da ta yi tsugune ta rafka tagumi idonta narau narau alamar akadan take jira ta yi kuka bayan wanda ta yi dazu.
“Mama ya tafi fa, kuma ba jansa na yi ba Wallahi ganina yayi ya ce yana Son yace na kawo shi gidanmu, yanzu ma da yace a sallamo masa Baba kawai zai nemi izinin hira da ni ne, kalli ma ya bada kudi yace a bawa Baba”
Mama ta dan taso ta leko harabar gidan ganin babu kowa sai ta ce.
“Je ki rufe gidan”
Na nufi gidan na rufe sannan na dawo na mika mata kudin.
“Kin tabbatar da haka ne Zahra karki janyo mana wahala”
“Wallahi gaskiya nake fada miki Mama ai kin san bana miki karya, amman Mama kin san da na tafi gidan Hajiya na tarar tana soya naman kaji da yawa, har tace ba zata sammin ba saboda na ce sai na fada maki Ya Deen ne kawai ya ba ni na shi”
Daga can cikin dakin da Baba yake rufe muka ji yana fadin.
“Ke kam dai Zahra kin shiga uku, yanzu kuma zuwa kika yi ki hada ni da uwarki? Ni Wallahi na san idan na ganki aljanna rahmar Allah ce kawai ta kaiki, amman wannan halin na ki ba zai bari ki shiga aljanna ba, to ba ni na siya mata nama ba ita ta siya da kudinta”
Mama ta tabe baki ta girgiza kai ta fito bandakin.
“To sai ki iya bakinki, kuma ki daina dauko mana magana Zahra na rasa abun da yake cikin kanki kullum magana ake amman kamar ana kara cewa ki yi, wannan lamari na ki Zahra ya isheni ya kai min intaha, dazu fa aka cire miki marin nan saboda rashin jin maganarki, amman har kin sake dauko wata maganar”
Ma dan matsa baya ina kallonta da damuwa a tare da ni, duk na san da cewa mawuyanci abu ne Mama ta saka min hannu da sunan duka sai idan ranta ya bace sosai.
“Mama na daina daga yau, kuma Wallahi dukansu ba wai na ja su ba ne, kin ga wannan so na yake shiyasa ya biyo ni har gida, kuma yayi ya saka yaransa su yi ma Yaya Deen duka sosai”
Mama ta fito da ido waje tana mamaki.
“Saboda me?”
“Wai yayi masa fada ne saboda ya tsaya da ni yana magana”
Mama bata ji dadi ba ba dan komai ba sai dan ta san da cewar Deen zai ya fitar da dukan da aka yi masa a jikina. A lokacin da ta tambaye ni ina na samo tufafi sai na yi mata karyar cewar Yaya Maryam ce ta bani, abu kamar wasa sai ga Baba ya kwana a dakin sai da safe ya fito, ni da Mama muka kwana a dayan dakin. Saboda na san ni mai laifi ce sai na shirya da wuri na tafi makarantar, a ranar aka raba mana jarabawarmu ta English da uka yi, guda daya na fadi a cikin dari, daman can ba dai kokari ba shiyasa Yara da yawa suke son zama a kusa ni domin ni ban iya rowar ilmi ba, kuma indai gurin kokari ne idan ban zo ta daya ba to zan zo ta biyu a ajin, sai dai ace bana jin magana amman akwai fahimtar karatu da saurin ganewa. Ba mu dawo gida ba da muka tsaya ni da kawata Hafsat muka yi abun da muka saba yi kamin mu dawo gida wato tsintar kayan marmari, ko da na iso gida ni dai nawa cikin ya cika ovar abinci rana ma kadan na ci na shiga bandaki, ina tsaka da wanka na ji sallamar Deen sai na daina motsa ruwan da nake ina ta sauraren gaisawar da yake da Mama.
“Mama ina Zahra”
Ina jin ya tambaye ni sai gabana ya fadi, Baba ya fara bashi labarin abun da na yi masa na sakawa mahaukaci yayi masa duka sannan kuma na kira masa sojiji har cikin gida. Aiko a ranar jikina ya fada min domin ina fitowa wankan jirana kawai yayi na saka tufafi na dauko jakar islamiya jikina na mazari na fito ina cewa Mama zan tafi islamiya.
“Islamiyar jan magana? Ki je can ki sake dauko Magana?”
A lokacin da na dube shi sai an fahimci dukan da sojan nan yayi masa ba dan karami ba ne, domin ua raunata masa fuska sosai kafarsa ma kamar gurgu haka yake tafiya. A lokacin da Deen ya rika hannu be yi min da sauki ba kamar wanda Allaj ya aiko haka ya rika dukana da bulalar da yayi tanadinta tun kamin ya shigo cikin gidan, zaneni yayi ras babu inda babu yabon bulala a jikina sannan ua buga min warning cewar idan ya sake ganin na tsaya da wani ina magana sai ya kusa kashe ni.
“Deeni da duka na gyara yaro ina kyautata zaton da yanzu Zahra ta daina abun da take, ina ganin addu'a kawai ya kamata a cigaba da yi mata har Allah ya shirya”
Cewar Mama daga inda take zaune ina rike da kafarta kuka na bana iya yi saboda wahalar duka. Baba ya nuna ni da baki yana fadin
“Ai wannan da kike gani bata jin magana shi ne kawai maganinta da ace ma baya dukanta wata kila ni da ke da yanzu ta kashe mu”
“Allah ya huta gajiya, wanne zan fara daga ciki Yallabai, albishir din zan sanar maka ko kuma labarin zan karasa maka”
“Da dai zaki daina kiran Yallabai din nan wata kila da sai kin fi kima a idona, amman kamin nan bari na yi katsalandan ba ki da lafiya ne? Sannan na kira Ummiter kwanan baya na ce ta baki wayar ina son na tambayeki kina son a gyara muku gidan da aka rusa ne ko kuma a siya muku wani amman baki amsa kiran ba why”
Sai a lokacin na gane dalilinsa na neman Ummiter ta kawo wayar da na yi zaton ko zai min maganar abun da na aikata ne da matarsa, a yanzu na gane wautata tabbas da akan haka ne da yanzu hankalin matarsa ya tashi, ni kuma da yake tsoro yayi min yawa sai na yi zaton ko Sauban ne ya fada masa wani abu.
“Alhamdulillah, lafiyar bata wadace ni ba kamar ba, kuma lokacin da ka kira na aje wayar ne na shiga bandaki shiyasa”
Kafa daya ya dora akan dayar yayi wani zama mai kama da kishingida yana kallona.
“Ina da zumuncin na karasa jin labarin abun da iyayenki suka yi a lokaci da sojojin suka ce za su shigo, tun ganin farko da na yi miki na kalli idonki na fahimci kina da wauta da kiriniya da kuma kurciya a tare dake, sai dai ban dauka a cikin labarinki kin wahalar da iyayenki har haka ba ban yi zaton labarin zai saka ni nishadin da na kwana biyu ban yi irinsa ba, Wallahi har a gurin aikin da na tafi idan na tuna murmushi nake, yau dai kam so nake ki karkare min komai sannan albishir din da Matata ta ce ya biyo baya”
Ashe da sauran murmushi a kumatuna da ba san da zamansa ba sai a yanzu da Mr Bashir yake fadar na saka shi nishadi. Na kara natsuwa a zaunen da nake sannan na cigaba da bashi labarin daga inda na dasa aya.
-Ni kadai suka bari tsaye a kofar gidan, da na ga babu sarki sai Allah sai na juya na fada masa cewar Mama ta shige bandaki Baba kuma ya shige daki ya rufe, sai sojan yayi murmushi ya kara matsowa kusa da kofar ya ce.
“Daman fa ba wani abun zan musu ba, ni da nake neman su zama surukaina ina ni ina yi musu wani abu, kawai dai na zo ne saboda na yi magana da su na fada musu cewar ina son yarsu kuma ina son yi min izinin rika zuwa ina magana da ke har mu daidaitu da juna, amman tun da ba su yarda sun fito ba zaki iya musu wannan bayanin albashi idan na dawo kin ga ba sai na sha wahala ba”
“Toh sai anjima”
“Dan jirani ina zuwa”
Ya nufi gurin motarsa ya bude ya shiga ya zauna, sannan ya fito ya nufo ni ya miko min sabbin kudin yan dari biyar biyar za su yi dubu goma, na saka hannu na karba daman can ni bana tsandar kudi ko a hannun waye suka fito kuwa.
“Ki bawa Baban kuma ki sanar masa zan sake dawowa Inshallah”
“Toh”
Murmushi ya sakar min sannan ya juya ya nufi motarsa ni kuma na gyara rikon tufafin Yaya Maryam dake hannuna da dan kwanon naman da Deen ya ba ni daman shi kullin ledar da na sato a dakinsa tana can cikin zanena na laketa yadda ba zata fado ba, sannan na dawo cikin gidan har lokacin Mama na bandaki Baba kuma yana daki ya rufe kansa, karasawa na yi kofar dakin na kara bakina jikin kofar na ce.
“Baba yace ga dubu goma a baka”
“Allah yasa rai yace a kara min Zahra Wallahi ba zan fito dakin nan ba, idan kika ga na fito to safiya ce ta waye a lokacin kam na tabbatar da ya gaji da tsayuwa ya tafi, yaushe kika janyo rigima da mahaukacin nan Fisabilillahi ya zo yayi min tsinannen duka alhalin ban san hawa ba balle sauka, yanzu kuma ki je ki janyo fada da sojoji dungurungun”
“Baba mahaukacin dazun ma shi ya fara fada ni fa, ni kuma na kwashe msa kafafuwa ya fadi shi ne ya biyo ni fa”
“Mahaukaciyar banza, ai kin ma fishi haukar, ni ba zan ma sake magana ba, waya sani ko kina nan tare da shi yana jina”
“Ya tafi fa Baba Wallahi ya tafi”
Baba be sake magana ba, har na gaji na nufi shimfidar da ya tashi na aje tufafin Yaya Maryam na juyo na nufi bandaki na leka Mama da ta yi tsugune ta rafka tagumi idonta narau narau alamar akadan take jira ta yi kuka bayan wanda ta yi dazu.
“Mama ya tafi fa, kuma ba jansa na yi ba Wallahi ganina yayi ya ce yana Son yace na kawo shi gidanmu, yanzu ma da yace a sallamo masa Baba kawai zai nemi izinin hira da ni ne, kalli ma ya bada kudi yace a bawa Baba”
Mama ta dan taso ta leko harabar gidan ganin babu kowa sai ta ce.
“Je ki rufe gidan”
Na nufi gidan na rufe sannan na dawo na mika mata kudin.
“Kin tabbatar da haka ne Zahra karki janyo mana wahala”
“Wallahi gaskiya nake fada miki Mama ai kin san bana miki karya, amman Mama kin san da na tafi gidan Hajiya na tarar tana soya naman kaji da yawa, har tace ba zata sammin ba saboda na ce sai na fada maki Ya Deen ne kawai ya ba ni na shi”
Daga can cikin dakin da Baba yake rufe muka ji yana fadin.
“Ke kam dai Zahra kin shiga uku, yanzu kuma zuwa kika yi ki hada ni da uwarki? Ni Wallahi na san idan na ganki aljanna rahmar Allah ce kawai ta kaiki, amman wannan halin na ki ba zai bari ki shiga aljanna ba, to ba ni na siya mata nama ba ita ta siya da kudinta”
Mama ta tabe baki ta girgiza kai ta fito bandakin.
“To sai ki iya bakinki, kuma ki daina dauko mana magana Zahra na rasa abun da yake cikin kanki kullum magana ake amman kamar ana kara cewa ki yi, wannan lamari na ki Zahra ya isheni ya kai min intaha, dazu fa aka cire miki marin nan saboda rashin jin maganarki, amman har kin sake dauko wata maganar”
Ma dan matsa baya ina kallonta da damuwa a tare da ni, duk na san da cewa mawuyanci abu ne Mama ta saka min hannu da sunan duka sai idan ranta ya bace sosai.
“Mama na daina daga yau, kuma Wallahi dukansu ba wai na ja su ba ne, kin ga wannan so na yake shiyasa ya biyo ni har gida, kuma yayi ya saka yaransa su yi ma Yaya Deen duka sosai”
Mama ta fito da ido waje tana mamaki.
“Saboda me?”
“Wai yayi masa fada ne saboda ya tsaya da ni yana magana”
Mama bata ji dadi ba ba dan komai ba sai dan ta san da cewar Deen zai ya fitar da dukan da aka yi masa a jikina. A lokacin da ta tambaye ni ina na samo tufafi sai na yi mata karyar cewar Yaya Maryam ce ta bani, abu kamar wasa sai ga Baba ya kwana a dakin sai da safe ya fito, ni da Mama muka kwana a dayan dakin. Saboda na san ni mai laifi ce sai na shirya da wuri na tafi makarantar, a ranar aka raba mana jarabawarmu ta English da uka yi, guda daya na fadi a cikin dari, daman can ba dai kokari ba shiyasa Yara da yawa suke son zama a kusa ni domin ni ban iya rowar ilmi ba, kuma indai gurin kokari ne idan ban zo ta daya ba to zan zo ta biyu a ajin, sai dai ace bana jin magana amman akwai fahimtar karatu da saurin ganewa. Ba mu dawo gida ba da muka tsaya ni da kawata Hafsat muka yi abun da muka saba yi kamin mu dawo gida wato tsintar kayan marmari, ko da na iso gida ni dai nawa cikin ya cika ovar abinci rana ma kadan na ci na shiga bandaki, ina tsaka da wanka na ji sallamar Deen sai na daina motsa ruwan da nake ina ta sauraren gaisawar da yake da Mama.
“Mama ina Zahra”
Ina jin ya tambaye ni sai gabana ya fadi, Baba ya fara bashi labarin abun da na yi masa na sakawa mahaukaci yayi masa duka sannan kuma na kira masa sojiji har cikin gida. Aiko a ranar jikina ya fada min domin ina fitowa wankan jirana kawai yayi na saka tufafi na dauko jakar islamiya jikina na mazari na fito ina cewa Mama zan tafi islamiya.
“Islamiyar jan magana? Ki je can ki sake dauko Magana?”
A lokacin da na dube shi sai an fahimci dukan da sojan nan yayi masa ba dan karami ba ne, domin ua raunata masa fuska sosai kafarsa ma kamar gurgu haka yake tafiya. A lokacin da Deen ya rika hannu be yi min da sauki ba kamar wanda Allaj ya aiko haka ya rika dukana da bulalar da yayi tanadinta tun kamin ya shigo cikin gidan, zaneni yayi ras babu inda babu yabon bulala a jikina sannan ua buga min warning cewar idan ya sake ganin na tsaya da wani ina magana sai ya kusa kashe ni.
“Deeni da duka na gyara yaro ina kyautata zaton da yanzu Zahra ta daina abun da take, ina ganin addu'a kawai ya kamata a cigaba da yi mata har Allah ya shirya”
Cewar Mama daga inda take zaune ina rike da kafarta kuka na bana iya yi saboda wahalar duka. Baba ya nuna ni da baki yana fadin
“Ai wannan da kike gani bata jin magana shi ne kawai maganinta da ace ma baya dukanta wata kila ni da ke da yanzu ta kashe mu”