Sashe 30
Ciwon So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na dago kafata na shigo cikin falo sai ya nuna min inda zan aje talkamin kafata, na nufi gurin na cire talkami sai ya nuna wadanda zan saka na taka zuwa cikin falon, abun ka da bakauya kai na daga sama ina karewa katon falon mai kama da wata karamar fada kallo, sam ban lura da mutane na dake falon ba har sai da Dr ya ce.
“Ki gaishe da mutane mana Zahra”
Na bisu daya bayan daya da kallo falon na kasu kusan hudu, kowa da inda ya hakimce kana ganin jama'ar cikinsa kasan mutane ne masu ji da kansu, na gaisa su wasu sun amsa wasu kuma ba su amsa min ba, a cikin wadanda suka amsa har da matar nan da Ammy ta taba zuwa da ita gaisuwa wata kila tana da alaka da yan gidan ko kuma wani ta rako oho. Ina kokarin zama a inda Dr Hamid ya nuna min sai na ji muryar Hajiya Jamila dake sauko downstairs tana min magana cikin tsawa.
“Aa aa zauna a kasa dai”
Na kalleta kamar na ce wani abu sai kuma na zauna a kasan kamar yadda ta umarta, ta sauko tana ta wani yatsina fuska kamar wanda ta yi arba da abun kazanta, ban yi mamaki ba daman wadanda ba su kaita arziki ba ma sun yi wulakancin balle ita da zata yi kashi ta goge da dala idan ta ga dama.
“Ina wuni”
Na gaishe ta cikin girmamawa sai ta amsa min kamar bata son magana, ashe ganin da nake mata ba ina tunanin kamar tana da saukin kai ba haka take ba.
“Wai sabuwar mai kula da baby ce zamu dauka”
“Eh aiko zaki samu mai kula miki da shi yadda ya kamata, amman dai ayi bincike mutane sai a hankali”
Wata mai tsinin baki ta fada, ina kallonta sai ta yi min kama da masu neman gindin zama a gidan masu abun lasa.
“Eh sai da muka yi bincike ai”
“Dr wuce ciki bari na gabatar da ita gurin Hubby”
Ina jin tacewa Dr Hamid dake hakimce yana latsa waya haka na san akwai alaka mai karfi a tsakaninku ba wai ta iya taimako ba ne kawai kamar yadda ya fada, daman kuma ina ganin kamaninta a fuskarta sai dai ban zargi komai ba sai a yanzu. Tashi yayi ya nufi katon upstairs din da ban tana ganinsa a fili ba sai a tv ya haye sama ita kuma ta mike tsaye tana yauki ta nufi wata kofar.
“Biyo ni”
Na mike tsaye na bi bayanta, tana gaba ina biye har muka isa wani katon corridor a kawata dama da hagunsa da fulawoyi sai kamshi ke tashi ga sanyin ac da ban san ta ina yake bullo ba, lallai na yarda a duniya ma akwai wata karamar aljanna.
“Jira ni a nan”
Ta fada sai na yi karaf zan yi magana ta yi min alama da na yi shiru, ta matso kusa da ni.
“Bari sai mun shiga dakina mu yi magana, akwai security cameras da yawa a gidan nan ki yi taka tsantsan”
Na daga mata kai sannan na ja na tsaya, ta shiga wata kofar, bata dade ba ta fito ta shiga dayar dake kusa da ita sannan ta fito ta yi min alama da na shigo, ban sam miyasa ba sai na samu kaina da faduwar gaba katon daki ne da babu komai a cikinsa ai kayan motsa jiki. Wani bangare na dakin ta nufa ni dai ina biye sa ita har muka shiga.
“Hubby motsa jiki da dare? Na shiga dakinka baka ciki”
“Na ci abinci da yawa ne, kuma kin san idan ban motsa jikin ba ba zan jidadin bachi ba saboda ban samu na yi da safe ba”
Ya amsa ni dai kaina na kasa kar na kalli mijin mutane.
“Waya kawo maka tea, ai da ka kira sai na kawo maka”
“Ummiter, na ga kina jego ne you need to rest ai tea ne ba wani abu ba”
“Any way i have a surprise and request for you, na san zaka ji ba dadi saboda baka son maid amman wannan zata taimaka min ne na kula da Babynmu”
Na dan dago na kalleshi na yi zaton tsoho zan gani ko dattijo, amman sai idanuwana suka yi arba da wanda ba zan iya kiransa da tsoho ba kuma ba yaro cancan ba, zai girmi abi wata kila da shekara hudu ko biya ko sama da haka kadan, fuskarsa ta yi min kama da wani wanda na sani amman a ina? Kuma waye? Shi ne ba zan iya tunawa ba, fajamas ne jikinsa sai dai gaban rigarsa a bude yake kana iya hango yadda kirjinsa ke cike da kananan gashi, hannunsa na rike da kofin da ya kira da na tea kana ganinsa kaga irin kirar mazan nan yan hutu ga kowane bangare na jikinsa ya amsa kirarsa irin wanda mata da yawa suke son ganin a jikin namiji wata kila saboda motsa jikin da yake.
“Amman kamata yayi ki fara magana dani ba wai ki gabatar min da ita kai tsaye ba”
“Na san idan na fada maka zaka ce aa ne shiyasa, amman ka yi hakuri, bata da yara ko daya mijinta kuma ya rasu tana bukatar aikin ne, kuma ka ga nima zan samu sauki idan mutane sun rage tun da ni kadai za a bari sai Yasmin kuma kaga Yasmin tana zuwa gurin aikinta ba kullun take zama ba”
Ta fada tana karasawa kusa da shi.
“And i promise you kula da Baby kawai zata yi ba zata yi girki ba, na san baka son girkin kowa sai nawa”
Magana take masa shi kuma kamar mai tunani, na sauke kaina kasa saboda kallon da yake min da nake jin kamar ya wuce kima.
“Ke ya sunanki”
Ya tambaya sai na amsa masa cikin girmamawa.
“Zahra yallabai”
“Zahra ko? Zo nan”
Na taho kamar yadda ya bukata ba tare da na kawo komai a raina ba.
“Zauna”
Ya nuna min kujerar dake kusa da wanda yake zaune a kanta, a maimakon na zauna a kai sai na zauna kasa na sadda kaina kasa.
“Zahra dago ki kalleni”
Gabana ya fadi zuciyata na raya min kamar kure karyata zai yi, Hajiya Jamila kuma ta yi shiru tana kallonmu kamar bata gurin. Na dago na kalleshi sai na yi arba da kyau da kuma kwarjini da Allah yayi masa duk kuwa da kasancewar shi baki, sai dai be kai wacan mugun Abiey kyau ba, kuma Abiey zai fi shi kurciya.
“Kin san fuskar nan tawa?”
Na kalli Hajiya Jamila sannan na girgiza masa kai. Hajiya Jamila ta kalleshi da mamaki ta
“Hubby lafiya?”
Ya daga mata hannu.
“Zaki iya tuna wani lokaci da jirgi ya fadi a wani kauye?”
Na dago da sauri na kalleshi ina daga masa kai.
“A ina?”
“A wani kauye dake zaria muna cikin gonar ni ina kwance sauran mutanen kuma suna aikin gona sai jirgi ya fado har har har...”
Gurin saurin fada maganar ta lake min sai na kara tuna fuskarsa tabbas shi ne, ban san lokacin da na nuna shi ba.
“Kai ne wanda karfin jirgin ya fadawa... Kai...kai...”
Ya daga min kai yana murmushi.
“Ni ne”
“Ban fa gane ba miya ke faruwa”
Sai ya kalleta ya ce.
“Wannan yarinyar da kike gani ita ta ceci rayuwata ba dan ita ba da yanzu takaba kike, zaki iya tuna yarinyar da na ce miki ta taimaka min lokacin da jirgina ya fadi? Har na aika mata da hukunci a asibiti aka ce ba a same ta ba? To ita ce wannan”
Kamar a rude Hajiya Jamila ta nuna ni.
“Wannan? Ita din ce dai ko kama?”
“Ai ba zan taba iya mantawa fuakarta ba har a bada, badan yarinyar nan ba da yanzu bana duniya, domin da mai tsaron lafiyata da direban jirgin duk wutar ta kone su sun mutu, amman ita wannan yarinyar ita ta janye min karfin nan na fito lokacin tana da tsoho ciki”
“Damkari....!”
Hajiya Jamila ta fada tare da kaiwa zaune, sai ya kalleni ya kalleta yana murmushi.
“Abun mamaki ko? Kin ga Allah ya kawo mana ita har gida”
“Aiko ni na ga mamaki Hubby, ni san mamaki hmmmmm.... ”
Ta karasa tana girgiza kai, kana ganinta kasan mamaki ne ya cika ta, kamar yadda ni ma ya cika ni domin ban taba zaton mijinta ne ba, ban kawo a raina cewa zan taba haduwa da wanda na ceta ba.
“Ina cikin?”
“Na haihu be zo da rai ba yallabai”
“Subhanallahi Allah yasa ba sanadin abun da ya faru ba?”
Na kalli Hajiya Jamila sannan na kalleshi na amsa min.
“Sanadin haka ne”
“Daman sai da na ji tsoron haka, saboda kin zubar da jini da yawa a lokacin nan, kuma na san nawa da aka saka miki a lokacin ba zai isheki ba a lokacin I'm sorry...”
Na sauke kaina kasa ba tare da na amsa ba.
“Welcome Zahra....”
Ya fada yana murmushin dake nuna ya jidadin ganina.
“Damkari...! Makari....!”
Hajiya Jamila ta fada tana kallona sai na dago nima na kalleta wata kila mamaki ne be gama fitarta ba.
____________
#Team Deen
#Team Abiey
[10/19, 5:23 PM] Oum_Nuwaira🥰: 2️⃣8️⃣
“A ina take da zama?”
Ya tambayi Hajiya Jamila sai ta kalleni.
“A nan take Kano”
Ya juyo ya kalleni.
“Wani abu ya kai ki a can kauyen ne”
“Na tafi gurin kawata ne”
“Allah sarki, na aika miki da sako a lokacin sai aka tarar baki nan a asibitin, kuma na saka a bibiye ki aa ce ba a san inda za a same ki ba”
Na sauke kaina kasa.
“Zaki iya aikin kula da Baby?”
“Haba Hubby sai da na yi magana da ita kamin na kawo ta nan, sai da na bincika komai”
“To Maa Shaa Allah, Allah ya bata ikon rike mana Babyn da amana, nice to meet you”
“Inshallah, na maka alkawari zan kula da Baby kamar ni na haife ta, ba zaka taba samuna da wata matsala ba”
Hajiya Jamila ta sauke numfashi da karfi sannan ta mike tsaye.
“Tashi mu shiga ciki”
“Ki gaishe da mutane mana Zahra”
Na bisu daya bayan daya da kallo falon na kasu kusan hudu, kowa da inda ya hakimce kana ganin jama'ar cikinsa kasan mutane ne masu ji da kansu, na gaisa su wasu sun amsa wasu kuma ba su amsa min ba, a cikin wadanda suka amsa har da matar nan da Ammy ta taba zuwa da ita gaisuwa wata kila tana da alaka da yan gidan ko kuma wani ta rako oho. Ina kokarin zama a inda Dr Hamid ya nuna min sai na ji muryar Hajiya Jamila dake sauko downstairs tana min magana cikin tsawa.
“Aa aa zauna a kasa dai”
Na kalleta kamar na ce wani abu sai kuma na zauna a kasan kamar yadda ta umarta, ta sauko tana ta wani yatsina fuska kamar wanda ta yi arba da abun kazanta, ban yi mamaki ba daman wadanda ba su kaita arziki ba ma sun yi wulakancin balle ita da zata yi kashi ta goge da dala idan ta ga dama.
“Ina wuni”
Na gaishe ta cikin girmamawa sai ta amsa min kamar bata son magana, ashe ganin da nake mata ba ina tunanin kamar tana da saukin kai ba haka take ba.
“Wai sabuwar mai kula da baby ce zamu dauka”
“Eh aiko zaki samu mai kula miki da shi yadda ya kamata, amman dai ayi bincike mutane sai a hankali”
Wata mai tsinin baki ta fada, ina kallonta sai ta yi min kama da masu neman gindin zama a gidan masu abun lasa.
“Eh sai da muka yi bincike ai”
“Dr wuce ciki bari na gabatar da ita gurin Hubby”
Ina jin tacewa Dr Hamid dake hakimce yana latsa waya haka na san akwai alaka mai karfi a tsakaninku ba wai ta iya taimako ba ne kawai kamar yadda ya fada, daman kuma ina ganin kamaninta a fuskarta sai dai ban zargi komai ba sai a yanzu. Tashi yayi ya nufi katon upstairs din da ban tana ganinsa a fili ba sai a tv ya haye sama ita kuma ta mike tsaye tana yauki ta nufi wata kofar.
“Biyo ni”
Na mike tsaye na bi bayanta, tana gaba ina biye har muka isa wani katon corridor a kawata dama da hagunsa da fulawoyi sai kamshi ke tashi ga sanyin ac da ban san ta ina yake bullo ba, lallai na yarda a duniya ma akwai wata karamar aljanna.
“Jira ni a nan”
Ta fada sai na yi karaf zan yi magana ta yi min alama da na yi shiru, ta matso kusa da ni.
“Bari sai mun shiga dakina mu yi magana, akwai security cameras da yawa a gidan nan ki yi taka tsantsan”
Na daga mata kai sannan na ja na tsaya, ta shiga wata kofar, bata dade ba ta fito ta shiga dayar dake kusa da ita sannan ta fito ta yi min alama da na shigo, ban sam miyasa ba sai na samu kaina da faduwar gaba katon daki ne da babu komai a cikinsa ai kayan motsa jiki. Wani bangare na dakin ta nufa ni dai ina biye sa ita har muka shiga.
“Hubby motsa jiki da dare? Na shiga dakinka baka ciki”
“Na ci abinci da yawa ne, kuma kin san idan ban motsa jikin ba ba zan jidadin bachi ba saboda ban samu na yi da safe ba”
Ya amsa ni dai kaina na kasa kar na kalli mijin mutane.
“Waya kawo maka tea, ai da ka kira sai na kawo maka”
“Ummiter, na ga kina jego ne you need to rest ai tea ne ba wani abu ba”
“Any way i have a surprise and request for you, na san zaka ji ba dadi saboda baka son maid amman wannan zata taimaka min ne na kula da Babynmu”
Na dan dago na kalleshi na yi zaton tsoho zan gani ko dattijo, amman sai idanuwana suka yi arba da wanda ba zan iya kiransa da tsoho ba kuma ba yaro cancan ba, zai girmi abi wata kila da shekara hudu ko biya ko sama da haka kadan, fuskarsa ta yi min kama da wani wanda na sani amman a ina? Kuma waye? Shi ne ba zan iya tunawa ba, fajamas ne jikinsa sai dai gaban rigarsa a bude yake kana iya hango yadda kirjinsa ke cike da kananan gashi, hannunsa na rike da kofin da ya kira da na tea kana ganinsa kaga irin kirar mazan nan yan hutu ga kowane bangare na jikinsa ya amsa kirarsa irin wanda mata da yawa suke son ganin a jikin namiji wata kila saboda motsa jikin da yake.
“Amman kamata yayi ki fara magana dani ba wai ki gabatar min da ita kai tsaye ba”
“Na san idan na fada maka zaka ce aa ne shiyasa, amman ka yi hakuri, bata da yara ko daya mijinta kuma ya rasu tana bukatar aikin ne, kuma ka ga nima zan samu sauki idan mutane sun rage tun da ni kadai za a bari sai Yasmin kuma kaga Yasmin tana zuwa gurin aikinta ba kullun take zama ba”
Ta fada tana karasawa kusa da shi.
“And i promise you kula da Baby kawai zata yi ba zata yi girki ba, na san baka son girkin kowa sai nawa”
Magana take masa shi kuma kamar mai tunani, na sauke kaina kasa saboda kallon da yake min da nake jin kamar ya wuce kima.
“Ke ya sunanki”
Ya tambaya sai na amsa masa cikin girmamawa.
“Zahra yallabai”
“Zahra ko? Zo nan”
Na taho kamar yadda ya bukata ba tare da na kawo komai a raina ba.
“Zauna”
Ya nuna min kujerar dake kusa da wanda yake zaune a kanta, a maimakon na zauna a kai sai na zauna kasa na sadda kaina kasa.
“Zahra dago ki kalleni”
Gabana ya fadi zuciyata na raya min kamar kure karyata zai yi, Hajiya Jamila kuma ta yi shiru tana kallonmu kamar bata gurin. Na dago na kalleshi sai na yi arba da kyau da kuma kwarjini da Allah yayi masa duk kuwa da kasancewar shi baki, sai dai be kai wacan mugun Abiey kyau ba, kuma Abiey zai fi shi kurciya.
“Kin san fuskar nan tawa?”
Na kalli Hajiya Jamila sannan na girgiza masa kai. Hajiya Jamila ta kalleshi da mamaki ta
“Hubby lafiya?”
Ya daga mata hannu.
“Zaki iya tuna wani lokaci da jirgi ya fadi a wani kauye?”
Na dago da sauri na kalleshi ina daga masa kai.
“A ina?”
“A wani kauye dake zaria muna cikin gonar ni ina kwance sauran mutanen kuma suna aikin gona sai jirgi ya fado har har har...”
Gurin saurin fada maganar ta lake min sai na kara tuna fuskarsa tabbas shi ne, ban san lokacin da na nuna shi ba.
“Kai ne wanda karfin jirgin ya fadawa... Kai...kai...”
Ya daga min kai yana murmushi.
“Ni ne”
“Ban fa gane ba miya ke faruwa”
Sai ya kalleta ya ce.
“Wannan yarinyar da kike gani ita ta ceci rayuwata ba dan ita ba da yanzu takaba kike, zaki iya tuna yarinyar da na ce miki ta taimaka min lokacin da jirgina ya fadi? Har na aika mata da hukunci a asibiti aka ce ba a same ta ba? To ita ce wannan”
Kamar a rude Hajiya Jamila ta nuna ni.
“Wannan? Ita din ce dai ko kama?”
“Ai ba zan taba iya mantawa fuakarta ba har a bada, badan yarinyar nan ba da yanzu bana duniya, domin da mai tsaron lafiyata da direban jirgin duk wutar ta kone su sun mutu, amman ita wannan yarinyar ita ta janye min karfin nan na fito lokacin tana da tsoho ciki”
“Damkari....!”
Hajiya Jamila ta fada tare da kaiwa zaune, sai ya kalleni ya kalleta yana murmushi.
“Abun mamaki ko? Kin ga Allah ya kawo mana ita har gida”
“Aiko ni na ga mamaki Hubby, ni san mamaki hmmmmm.... ”
Ta karasa tana girgiza kai, kana ganinta kasan mamaki ne ya cika ta, kamar yadda ni ma ya cika ni domin ban taba zaton mijinta ne ba, ban kawo a raina cewa zan taba haduwa da wanda na ceta ba.
“Ina cikin?”
“Na haihu be zo da rai ba yallabai”
“Subhanallahi Allah yasa ba sanadin abun da ya faru ba?”
Na kalli Hajiya Jamila sannan na kalleshi na amsa min.
“Sanadin haka ne”
“Daman sai da na ji tsoron haka, saboda kin zubar da jini da yawa a lokacin nan, kuma na san nawa da aka saka miki a lokacin ba zai isheki ba a lokacin I'm sorry...”
Na sauke kaina kasa ba tare da na amsa ba.
“Welcome Zahra....”
Ya fada yana murmushin dake nuna ya jidadin ganina.
“Damkari...! Makari....!”
Hajiya Jamila ta fada tana kallona sai na dago nima na kalleta wata kila mamaki ne be gama fitarta ba.
____________
#Team Deen
#Team Abiey
[10/19, 5:23 PM] Oum_Nuwaira🥰: 2️⃣8️⃣
“A ina take da zama?”
Ya tambayi Hajiya Jamila sai ta kalleni.
“A nan take Kano”
Ya juyo ya kalleni.
“Wani abu ya kai ki a can kauyen ne”
“Na tafi gurin kawata ne”
“Allah sarki, na aika miki da sako a lokacin sai aka tarar baki nan a asibitin, kuma na saka a bibiye ki aa ce ba a san inda za a same ki ba”
Na sauke kaina kasa.
“Zaki iya aikin kula da Baby?”
“Haba Hubby sai da na yi magana da ita kamin na kawo ta nan, sai da na bincika komai”
“To Maa Shaa Allah, Allah ya bata ikon rike mana Babyn da amana, nice to meet you”
“Inshallah, na maka alkawari zan kula da Baby kamar ni na haife ta, ba zaka taba samuna da wata matsala ba”
Hajiya Jamila ta sauke numfashi da karfi sannan ta mike tsaye.
“Tashi mu shiga ciki”