← Book details Ragayar Dutse Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 110

Sashe 10

Ragayar Dutse Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abba ya ce, “saka wayar a speaker..”

Jazy ya yi yadda Abba ya ce, daga can ɓangaren Abba ya ce, “Rehaan.”

Rehaan ya gyara zama ya ce, “Abba ina kwana.”

Abba bai amsa gaisuwar ba ya ce, “Yanzu Rehaan baza ka ta ya ni yiwa mahaifiyata biyayya ba? Ashe daman za ka iya ƙin ɗaukar wayata, kamar ni ace ina kiranka kana kallo ka ƙi ɗauka? Kana cikin hankalin ka kuwa?.”

Ray ya ɗan rufe ido amma bai ce komai ba, dan shi kansa ya san bai kyauta ba, amma babu yadda zai yi. Abba ya ce, “kana kallon kirana yana shigowa wayarka baza ka iya ɗauka ba? Ka ga messages ɗina duk ka yi banza saboda na yi maka dole akan abinda ba ka so ko?.”

Ray cikin sanyin murya ya ce, “ka yi Abba, ba haka bane, na kwana bani da lafiya, yanzu haka ma kaina ciwo yake yi.”

“Meyasa ba ka ɗauki wayar ka faɗa min haka ba? Da ka faɗa min zan takura ma ka da kira ne?. Kai ka san halin Daada, kasan yadda ta ɗaukaki auren nan, ka san yadda take son yarinyar nan, ka san yadda ta saka auren a ranta, dole in ba ka zo ba ranta zai ɓaci. Ta ya ina lallaɓata mu rabu lafiya kana neman ɓarar da albarkar da nake tattalinta? In kai ne Mamy ta ke yiwa ɗanka haka za ka ji daɗi ace yana misbehaving kamar yadda ka ke yi min? Ina alƙawarin da ka yi min akan auren nan Rehaan!?.”

Kafin ya yi magana ya ce, “dan ka raina ni ko? Har ina kiran ka a waya ka ƙi ɗauka, da yake ba Nadira ba ce ba ko? Inda itace na tabbata baza ka taɓa ƙin ɗaukar kiranta ba, tunda ita itace ta haife ka ni kuma ka ajjiye ni?.”

Ray jin Abba yana yi masa faɗa sosai sai ya yi sanyi ya ce, “ka yi haƙuri Abba, don Allah ka yi haƙuri.”

“Haƙuri ya zama dole na yi Rehaan, tunda ka ɓatawa mahaifiyata rai nima ka ɓata min rai. Ko dan saboda idanun ƴan bikin da suke gidan ya kamata ace kazo ka kwana a gida, amarya guda aka kawo maka, amarya ce kamar ko wacce amarya, amma sai ka saka waya a dnd dan ka nunawa mutane kai ba sonta ka ke yi ba, ka nunawa mutane nima ɗin ban isa da kai ba, tunda ba Nadira ba ce dole ka ƙi ɗaukar kirana.”

“Ka yi haƙuri Abba, ban yi dan ranka ya ɓaci ba.”

Abba cikin ba da umarni ya ce, “Ka tabbatar da a gida ka yi sallar magrib, ban yarda ka je ajo ko buɗan kan Riyya ba, ka dawo gida ina nan ina jiran ka. Kar ka kawo min wani uzuri, wallahil azim bazan yarda da shi ba Rehaan.”

Ray jin yadda Abba ya rantse ya ce, “in sha Allah, zan zo kamar yadda ka ce.” Daga haka Abba ya kashe wayar, Jazy ya saka wayar a aljihu yana kallonsa.

Rehaan cikin wani irin yanayi ya ce, “wanne tsautsayi ne ya kai ni amincewa da auren nan oho, har an fara bani ciwon kai.”

Jazy ya ce, “laifin ka ne, meye dan ka je gidan ka kwana a inda ka saba kwana? Akwai abinda zai cinye ka ne?.”

Ray bai ce komai ba, sai kuma ya kalle Jazy suka haÉ—a ido ya sake É—auke kansa daga kallonsa.

Jazy ya ce, “haka kawai ka jawo an ce baza ka je wajan Ajo ba, daman haka ka ke so ai, sai ka je ka zauna da matar ka a ci amarci” ya faɗa yana dariyar shaƙiyanci yana ɗauko magani a aljihunsa.

Jazy ya kalle sa ya ce, “Maleek da Ubaid sun koma Jeddah, sun so su haɗu da kai na ce bacci ka ke yi.”

Bai san dalili ba, bai san meyasa ba, haka kawai ya ji gabansa ya faɗi ambatar sunan Ubaid da Jazy ya yi, ya lumshe ido yana tuna haɗuwarsu ta ƙarshe da Ubaid a ranar dinner Riyya, yana ta sake maimaita masa missing ɗin Islaha da ya yi, yana faɗa masa how sweet she was da sauran su. Ya ja tsaki, ya cize bakinsa bai ce komai ba.

Sai kuma ya kalli Jazy ganin yana shan magani ya ce, “wannan fa?.”

“Na masu aure ne.”

“Meye shi?.”

“Magani.”

“Na meye?.”

“Na gyaran aure.”

“Like how?.”

Jazy ya ce, “kai fa baka gane yare cikin yare ko? To na gyaran hanya ne.”

Ray ya sake yin jim ya ce, “ban gane ba, yi min bayani.”

Jazy ya yi ƴar dariya ya ce, “kai banza ne, ba ka gane magana sai an yi maka filla filla. Ina sha saboda ƙanwar ka Riyya, just for honeymoon.”

Ray sai a lokacin ya ɗau haske ya fahimci inda Jazy ya dosa, sai kuwa ya haɗe rai ya miƙa hannunsa ya buge maganin daga hannun Jazy.

Maganin ya faɗi ƙasa ya zube, Rehaan cikin ɓacin rai ya ce, “ba ka da hankali, kashe ta zaka yi?.”

Jazy ya ƙyalƙyale da dariya ya ce, “sabuwa mota ai sai sa lubraciation, ka taɓa ganin an hau sabuwar mota babu gyara?…..”

Jazy ya kalli maganin ya ce, “Kawai ka zubar min da magani, ka san wahalar da na sha kafin na same sa?.”

Ray ya sake ɗaure fuska alamun babu wasa ya ce, “ba wasa nake yi maka ba, ka daina wannan shirmen, in wani abu ya sanu Riyya sai na yi repoting ɗinka a court, Allah sai na nuna maka kuskuren ka. Ba ka da hankali ashe ban sani ba?.”

Jazy ya yi dariya son ransa sannan ya ce, “Ka ga mai ƙanwa, kai ga big brother ko? Kaima ka sha ko za ka ga amfaninsa a wajan matarka.” Banza ya yi masa bai ce komai ba, Jazy ya cigaba da abinda yake yi.

Ray ya sake kallonsa suka haɗa ido ya ce, “Jazy…” sai kuma ya fasa ya gyaɗa kai bai ce komai ba.

“Malam meye? Matata ce fa, ina ruwan ka da shiga tsakanin mata da miji? Ban da saka ido ina Yayan mata zai dinga sakawa mijinta ido?.”

Bai ce masa komai ba ya sauke numfashi yana girgiza kai, damtabbas sai ya nuna masa kuskurensa in ya cutar masa da ƙanwa, Allah sai y bashi mamaki.

Jazy bai jima ba ya tafi saboda shirye shirye, shima Rehaan sai da ya yi sallar Magrib sannan ya shirya ya fito.

Yana shiga gidan ya tarar duk matan gidan basa nan, gidan shiru duk an watse an tafi gidansu Jazy ana wani bikin a cam. Kai tsaye wajan Abba ya wuce, yana shiga ya same sa a zaune shi kaÉ—ai yana danna waya.

Ray ya ƙarasa ya zauna ya ce, “Abba ina yini.”

Abba ya bi shi da kallo sannam ya ce, “Ka kyauta Rehaan, na gode da abinda ka yi min, ka nunawa mutanen gidan nan ban isa na saka ka ka yi ba, ka nunawa duniya ba ka son auren nan.”

“Ka yi haƙuri.”

“Dole ka ba ni haƙuri, tunda ka riga ka aikata.”Bai ce komai ba kansa dai yana ƙasa dan ya san ya ɓatawa Abba rai.

Abba ya ce, “ka je ka taho da matar taka, ku same ni a ɓangaren Daada.”

Ya ɗaga kai dan babu damar yi masa musu, yadda ran Abba ya ɓaci bazai musa masa akan abinda ya ce ba. Bai ce komai ba ya miƙe ya nufi ɓangarensa, yana tunanin yadda zai kira Islaha ya ce ta zo in ji Abba, da wannan tunanin ya shiga jikinsa babu daɗi.

Nana Haleema.

RDB3P08
Nana Haleema.

Islaha tana zaune tana kuka wayarta tana kusa da ita ta saka a speaker tana jin duk abinda Safeera take faÉ—a mata akan halin da Hamma yake ciki. Safeera ta ce, "Don Allah ki bar wannan kukan, na faÉ—a miki ya samu lafiya har sun dawo gida."

Cikin kuka ta ce, "Safeera in mutuwa Hamma ya yi ki faɗa min, ku daina ɓoye min don Allah."

"Wallahi yana nan da rai, kuma ya samu lafiya sosai, ki daina kukan nan don Allah."

Islaha ta ce, "yana jin haushina, yana gani kamar na ci amanarsa, yana gani kamar na zaɓi kuɗi na bar sa. Wallahi zuciyata cike take da danasanin auren nan, danasani nake yi sau babu adadi. Na gaji Safeera, kawai ina so a yi ta ta ƙare, kowa ya kama gabansa. Haba!Ina so na ga Hamma amma wannan ƙaddarreen auren ya ɗaure ni tamau a gidan nan, wanne irin halacci ne Hamma bai yi ba, wacce irin soyayya da ƙauna ce Hamma bai gwafa min ba? Kuma a ce da abinda zan saka masa kenan? Wallahi da ban cika ƴar halak ba......." ta dakata da maganar tana kuka.

Sai kuma ta dakata da kukan ta ce, "Ko dai daman ni ba Æ´ar halak É—in bace ba Safeeta?."

A tausahe ta ce, "Haba Islaha! Ki daina wannan maganar don Allah, duk abinda ki ka aikata kin yi ne saboda shi, kin yi ne dan ki kuɓutar dashi daga hannun masu garkuwa da mutane. Ki nutsu don Allah, na tabbatar zai saurare ki komai ya dawo daidai."

"Aure fa na yi Safira, wani daban na aura ba shi ba. Kar ki manta ranar da ya dawo gida ranar na taho gidan nan, ko gaisawar kirki ba mu yi ba. Ga wahalar da ya sha a hannun kidnappers, ga rashin lafiyar da ya yi, kuma yana dawowa gida ya tarar na yi aure zan tafi gidan wani ba shi ba. Wallahi ina tantama a kan asalina, ina tantama sosai."

"Tantamar me ki ke yi?."

"Ina ji a zuciyata anya ta hanyar aure aka same ni?."

"A'uzubillahu! Wannan wanne irin ƙazamin tunani ki ke yi?."

"Safeera gaskiya ce, duk ɗan halak bazai yi abinda na yiwa Hamma ba, shiyasa nake tantamar anya ni ƴar halak ce?. Ke kin san waye Hamma a wajena, kin san irin ɗawainiyar da ya yi dani a rayuwarsa ba sai na faɗa ba, ranar da dawo daga wajen kidnappers ranar na bar gidan. Abin ya yi yawa, ban kyauta masa ba wallahi.”
Chapter 10 · 0% Book details