Sashe 89
Manar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
After few minutes mother ta shigo gidan daga unguwa ganin takalman Manar watse a parlor ta kwalo mata kira,jin shiru babu motsinta she thought ko ba ta gidan ma kawai ta shiga ta wuce d'akinta,ta d'aura alwala ta dawo parlor tana kallon agogo,seeing that lokacin sallah har ya yi ta shimfid'a abun sallah ta kabbara sallah,sanda ta idar ta sake kallon k'ofar d'akin Manar,jikinta ya ba ta tana cikin d'akin ta sake kiranta "Manar!" Da sauri Manar da har lokacin take k'udundune cikin duvet bata san ma anyi sallah ba ta fito da kanta daga cikin bargon idanunta sun kumbura,mother ta sake kwalo mata kira,da sauri ta sakko daga kan gadon tana goge idanunta da hawaye ya k'i tsaya mata,ta nufi k'ofa ta bud'e ta fito parlon tana sunkuyar da kanta,mother ta dunga kallonta fuskarta babu alamun wasa tace "wane iskanci yasa kika zubar min takalmanki a nan? Baki ga gurin a gyare yake ba?" Da kyar ta bud'e baki tace "I'm sorry mother" ta wuce ta d'auke su ta nufi hanyar d'akinta,shiru mother tayi tana kallonta with suspicion,har ta kusa shigewa d'akin mother tace "kukan me kike?" Saurin girgiza mata kai tayi tace "babu komai" mother ta mata wani kallo tace "zo nan" sosai zuciyarta ya tsinke ta juya ta tsuguna k'asa ta kasa kallon mother,a sanyaye tace "here i'm mother" cikin fad'a mother tace "what's wrong with u?" Duk yanda ta so dakewa kasawa tayi,wasu hawayen suna bin fuskarta ta sake cewa "nothing mother" muryarta yana cracking ta kai hannunta tana d'auke kwallar data zubo mata,duk yanda mother ta so b'oye damuwarta seeing her first born tana kuka kasawa tayi,ta sassauta muryarta tace "tell me daughter what happened to u? Why are u crying?" Da wani breaking voice tace "babu komai mother" had'e rai mother tayi ta mata wani tsawa tace "c'mon maza ba ni amsa,me aka maki?" Manar ta kasa magana sai hawaye take,tsaki mother tayi tace "shashancin banza tunda baza ki fad'a ba tashi maza ki b'ace min daga gani kafin na fusata na maki shegen duka" bata jira mother ta gama fad'a ba ta tashi da gudu ta bar parlon,sanda ta shige mother ta tuna tace "Manar!" Sakkowa tayi daga gadon data fad'a tana kuka da sauri ta bud'e k'ofar d'akin ta tsaya bakin k'ofar bata yarda ta fita ba,mother dake kallonta cike da mamaki tace "kin ma yi sallah kuwa?" A hankali ta girgiza mata kai,mother ta dunga kallonta tace "kina kukan banzan naki aka yi sallah aka idar baki yi ba?" A hankali tace "zan yi yanzu" mother ta girgiza kai cikin takaici ta d'auke kanta,har ta idar da sallah bata daina jin zuciyarta a cunkushe ba but ta yi k'ok'arin ganin hawayenta sun tsaya,har sannan she is just shock da abunda ya faru tsakaninta da Yayan nata,ranar har dare mother kallonta kawai take bata k'ara tambayarta abunda yake faruwa ba,sai dai sosai ta sa mata ido tana k'ara studying d'inta. Around 9pm mother tana zaune parlor Waleed yayi sallama bakin k'ofa,ta amsa tace "shigo mana Waleed ka tsaya nan kamar bak'o" Waleed ya shigo parlon kansa a k'asa,mother tana kallonsa fuskarta da fara'a tace "sannu da zuwa" ya d'an yi murmushin k'arfin hali ya zauna yace "ina wuni mother?" Mother tace "lafiya lau,ya gida da office?" Yace "Alhamdulillah" tace "kwana biyu ba ka shigowa?" Ya d'an yi k'asa da idanunsa saboda wani nauyinta da yaji ya kasa amsawa,mother tana kallonsa tace "ba ka da lafiya ne?" Y'ar dariya yayi yana shafa backhead d'insa yace "i'm fine mother,me kika gani?" Ta girgiza kai tace "ba haka na saba ganinka ba" ya daure yace "lafiya na k'alau mother stress ne kawai yasa kika ga kamar ba ni da lafiya" mother dai bata yarda ba ta dunga kallonsa,shi da kansa ya tsargu ya dunga tunanin ko dai Manar ta sanar ma mother abunda ya faru tsakaninsu,can ya d'ago ya kalli mother yace "Manar fa mother?" Mother tace "tana ciki tun d'azun but let me call her" ya kalleta cike da fargaba yace "ba ta da lafiya ne?" Girgiza kai mother tayi tace "she's okay but ban san me aka mata ba tayi camping kanta tun d'azun na yi tambayar duniya ta k'i cemin komai,har yi nayi kamar zan daketa bata fad'a min ba,bari na turo ta maybe idan ka tambayeta ta iya fad'a maka" mother ta kalli k'ofar d'akin ta kira ta yayi sau biyar amma shiru,ta mik'e ta nufi d'akin,a kwance ta ganta ta lullub'a da duvet,ta k'arasa ta yaye duvet d'in,da sauri Manar ta rufe idanunta,mother dai sai kallonta take,ta kai hannu ta girgiza ta tace "Manar na san ba bacci kike ba think Hjy ta aiko a kira ki,ki tashi kije Yayanki yana jiranki a parlor.. Tunda haka kika zab'a baza ki iya gaya min damuwarki ba shi kenan" k'in yarda Manar tayi su had'a ido ta mik'e zaune a hankali tace "mother kiyi hak'uri ni fa na ce miki babu komai" mother tace "ai shi kenan tashi kije yana parlor yana jiranki" mother ta juya ta fita d'akin,parlor ta koma ta zauna tana kallon Waleed tace "i don't know what's wrong with her,tun d'azu take cikin d'aki ko abinci ta k'i fitowa ta ci,na yi fad'an duk a banza" Waleed ya kalli mother yace "me aka mata?" Dai² nan Manar ta bud'e k'ofar d'akin ta fito kanta a k'asa,Waleed ya zuba mata idanu sai kallonta yake har ta k'araso cikin parlon,tana ganinsa ta d'auke kanta za ta fita,wani tsawa mother tayi mata tace "iskancin ki har ya kai kiga Yayanki ki wucesa?" Kamar za ta d'ora hannu aka ta fasa ihu,ta juya ta masa wani kallo daga inda take tsaye tace "ina wuni?" Wani ajiyar zuciya yayi a hankali though ya san fushi take da shi amma ya ji sanyi sosai a ransa da ya ganta yace "lafiya lau,what's wrong?" K'in cewa komai tayi,mother sai kallonta take cike da takaici tayi k'wafa ta wuce d'aki ta barsu a parlon,Manar tana ganin haka ta had'e rai,cikin sanyin jiki Waleed ya mik'e ya matsa kusa da ita yana kallonta fuskarsa tana bayyana damuwa yace "Manar what happened?" 'Dago kanta tayi tana kallonsa hawaye cike a idanunta tace "babu komai" yayi shiru yana kallonta,can yace "mu je waje muyi magana?" Nan ma bata ce masa komai ba ta juya ta fara tafiya ya bi bayanta suka nufi k'ofa tare,da suka fita har ta nufi hanyar gidan Dadda ya tsayar da ita,yana kallonta yace "saboda abunda ya faru d'azun kike kuka?" Girgiza masa kai tayi,yace "what happened to?" A hankali tana goge hawayen da suka zubo mata tace "babu komai" bata jira ya sake cewa komai ba tayi wucewarta ya bi ta da ido,can ya bi bayanta da sauri ya rik'ota ya nufi backyard da ita,ta dunga binsa ta kasa ce masa komai,sai da suka zagaya ya tsaya yana kallonta da idanunsa da suka birkice yace "Manar da gaske ba kya so na?" Kasa cewa komai tayi sai kanta da ta sunkuyar k'asa playing with her fingers,ya kai hannunsa ya d'ago fuskarta ya zuba mata idanunsa,cikin sanyin maganarsa yace "I'm very sorry Manar,abunda ya faru d'azun it's.." Kafin yace wani abu ta girgiza masa kai tace "i knew it's not intentional,this is what u want to say,right?" Ajiyar zuciyar yayi bai ce komai ba sai kallonta da yake yi zuciyarsa tana wani bugawa b'im²,tace "shi kenan Yaya na yarda it's not intentional,but if something happens nan gaba ba zan k'ara maka uzuri ba,ka yarda?" Kallonta ya dunga yi da mamaki ya d'aga mata kai da sauri yace "sure" tayi d'an murmurshi a hankali ta juya za ta tafi,yayi sauri ya rik'o hannunta,ta juya ta kallesa,ya langab'ar da kansa a hankali yace "I'm really sorry.." Tace "ya wuce Yaya na hak'ura ai" yace "thank u.. Now tell me what do u want for ur Qur'anic grad?" Shiru tayi kafin tayi murmushi tana girgiza masa kai tace "ni dai ba na son komai" ya dunga kallonta yace "baza dai ki fad'a ba,saboda kina fushi da ni" ta kalleshi da sauri suka had'a idanu,tayi saurin d'auke na ta,tace "zanje hjy tana kira na" strictly yace "ni nake nemanki ba hjy ba" sake d'aga kanta tayi ta kalleshi ya lumshe mata idanunsa a hankali yace "kiyi hak'uri please" ta gyad'a masa kai,ya sake yin ajiyar zuciya yace "thank u" daga haka ya saketa,yana tsaye yana kallonta tayi masa sai da safe ta juya ta bar gurin,ya bi ta da ido har ta b'acewa ganinsa,bata koma part d'insu ba ta shige gidan Dadda,tana saka kayanta za ta kwanta text ya shigo wayarta ta kalli screen d'in,ta d'auke kanta ganin Azaan ne,haka kawai taji baza ta iya d'auka ba ta k'arasa shirinta ta bar wayar nan gaban mirror ta kashe wutan d'akin tayi kwanciyarta,ta jima sosai kafin bacci ya d'auketa. Washe gari Friday duk yanda ta dunga jin kanta yana ciwo haka ta daure tayi shirin tafiya skul,har lokacin kuma bata wani koma normal ba don scene d'in abunda ya faru jiya ya k'i gogewa daga mind d'inta,motsi kad'an tayi sai ta kai hannunta kan lips d'inta ta shafa,ji take kamar har lokacin Waleed bai daina kissing d'inta ba,duk sanda ta tuna sai gabanta yayi mummunan fad'uwa,sanda Nusy da Ameerah suka gaji da ganin abunda take yi a skul,Nusy ta tab'a ta tace "what's wrong dear?" Manar tayi mata murmushi tace "nothing" da suka yi haka sai bata k'ara tambayarta ba,sanda ta sake kai hannunta kan lips ameerah ta kalli Nusy tace "anya kuwa ba wani abu ya faru ba?" Nusy tace "i don't know" ranar ba wani sosai ta mayar da hankalinta kan lesson ba,sanda aka tashi sun fito suna tafiya Nusy tace "wai me ya faru ne yau duk kin zama wani so quite,tell us me yake damunki?" D'an murmushin yak'e tayi za ta ce babu komai Ameerah tace "don't tell us nothing,wallahi ko qur'ani za ki had'iye yau bazan yarda dake ba.." Kallonta Manar ta dunga yi can ta turo baki tana harararta tace "kada Allah sa ki yarda d'in" Ameerah ta kalli Nusy tace "friend i just told u dama akwai abunda ya faru,fad'a ne kawai baza ta yi ba saboda bata yarda da mu ba" wani kallo Manar tayi mata kamar za tayi kuka ta zayyana