← Book details Manar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 183 OF 184

Sashe 183

Manar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wani ranar Sunday wanda ya zama ranar da familyn Maji Dad'i baza su tab'a mantawa da shi ba,da dare misalin k'arfe biyu da mintuna Hjy Dadda ta amsa kiran mahaliccinmu,bayan gajeran rashin lafiyar da tayi,wanda a lokacin duka bai wuce kwanaki uku da zuwansu Waleed k'asar suka duba jikinta ba,ranan da za su tafi sunzo mata sallama saboda jikin nata ya d'an fara kyau duk da tsufan da tayi,Manar tace "Hjyta za mu tafi sai mun sake zuwa duba jikinki" Dadda dake kwance ta d'aga kai tace "kayya! Dai takwara ni kam dai da wuya na wuce makon nan da muke ciki,ko na samu na tsallakesa tabbas zai yi matuk'ar wahala na tsallake mai biye masa" ranar irin maganganun da suka yi da ita sai da ta karya musu zuciya,duk jikokin ta sasu zubar da kwalla,musamman Manar da take cewa "dukiyarki da yake hannuna tsayin lokaci duk na tattarasa kafin na kwanta jinya na damk'asa hannun mahaifinki,idan ta Allah ta kasance min kafin ku sake zuwa tou,Allah ya sada fuskokinmu da rahamarsa,ya had'amu a jannatul firdausi.." Manar tana kuka ta kwantar da kanta a cinyar Dadda tana cewa "dan Allah Hjyta kada ki tafi ki barni" Dadda tayi murmushi irin na tsofaffin tana shafa kanta tace "kayya dai Manar,mutuwa dole ya zama,ko ba dad'e ko ba jima dole sai ni ko ke d'ayan mu ya tafi.." Haka nan dai suka yi sallama suka tafi suna kuka Dadda na yi. Da asuba kusan tare suka tashi,but kafin Waleed ya fita Masjeed sai da ya mammatseta then ya fita yana murmushin zumbura bakin da take masa,lokacin suna dawowa bayan an idar da sallah a hanyarsu na komawa gida,wayarsa tayi haske kasancewar ya sa ta silent,daf da apartment d'insu suna rabuwa da su Azaan,shi da su Alhassan za su shiga gida yaga kiran Abba,lokacin da ya kalli sunan dake kan wayar sai da yaji gabansa ya fad'i,ya daure dai yace ma yaransa su shiga gida,then ya koma gefe yayi sallama,hankalinsa bai k'ara tashi ba sai da yaji muryar Abba a sanyaye yana cewa "Muh'd!" Waleed yace "na'am Abba,barka da safiya" Abba ya amsa,bayan sun gaisa kafin Abba ya sanar masa maganar da tasa ya kirasa,sai da ya fara masa nasiha mai shiga jiki then yace "Allah ya karb'i rayuwar kakarku yau da misalin k'arfe biyu da mintuna" ai kamar daga sama haka Waleed yaji maganar mutuwar,kawai ji yayi bakinsa ya fara maimaita kalmar "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.." Abba yace "hak'uri za muyi duka.. Allah ya mata rahama" yana jin hawaye suna kawowa idanunsa,Waleed ya amsa cikin raunin murya,a sanyaye ya tsaya ya turama Azaan da Amaar text akan kada su fad'awa su Ameerah,kawai su shirya su tafi idan sun isa Nigeria sa ga ko me yake faruwa,sannan ya shiga gidan cikin mutuwar jiki,ko da ya shiga sai da ya fara sawa maid ta shirya kayan yara,then ya wuce bedroom d'insa,a zaune ya tarar da ita ta idar da sallah tana addu'o'i,bai cema mata komai ba ya wuce ya nufi closet,ta bisa da kallo lokacin da yake had'a kaya cikin luggage,cike da mamaki tace "Master me yake faruwa?" Bai tankata ba sai da ya gama d'aukan iya abunda ya san za su buk'ata ya fitar da kayan yasa maids suka kai mota,then ya dawo yana kallon yanda ta kwanta tayi luff akan kado tana jujjuya idanu ya mik'a mata hannu yace "sakko na shiryaki tafiya za muyi" da sauri ta mik'e tace "ina za muje?" Yace "sakko mana idan munje za ki gani" ajiyar zuciya tayi kafin ta sakko,ya cire mata kaya ya d'aura mata towel shima ya rage na sa,ya d'aura towel a waistband d'insa ya rik'e hannunta suka shiga bathroom,gaba d'ayansu tunda suka shiga tube d'in banda ajiyar zuciya babu abunda suke saukewa,idanunta a lumshe tace "Masterrhhh!" Kasa amsawa yayi jin yanda wani rauni yake ziyartarsa yana taso masa,idan ya tuno wai Hjy Siyama ce ta mutu,kuma ya kasa sanar mata saboda ya san za ta shiga tashin hankali,sai yaji hawaye suna son zubo masa,a haka dai ya daure suka yi wanka,a gurguje suka shirya suka fito,after sunyi breakfast lokacin yaran tuni an fita da su b'angaren Rani Naheed,suna gamawa suma suka fito suka nufi b'angaren Rani,tun daga nan Manar ta fara shan jinin jikinta kan lallai akwai abunda yake faruwa,al'amarin bai k'ara tada mata hankali ba,sai da taga har da Raj da Rani Naheed za ayi tafiyar,a haka dai suka fito zuciyarta sai tsinkewa yake suka shiga motoci hadimai gaba da bayansu suka wuce airport jirgi guda suka yi kwansu da kwarkwata suka dumfari Nigeria,ko cikin jirgin haka nan tayi luff a jikinsa tana jin yanda yaran suke hayaniya,amma ta kasa magana gabanta banda fad'uwa babu abunda yake,a haka jirginsu ya sauka Malam Aminu International airport,nan suka tarar da manyan motoci da drivers da suke jiransu,suka shiga motoci aka wuce da su estate da family house d'insu yake,sanda motarsu yake gangarawa line tun daga farkonsa suka fara cin karo da motoci da mutane,sojoji a ko ina suna kula da masu shige da fice,jikinta a sanyaye ta waiga ta kalleshi bakinta yana b'ari tace "Masterrhhh! Ni ka k'i ce min komai,dan Allah ka fad'a min me yake faruwa,jikina ya jima da sanar min ba lafiya ba,ka fad'a min dan Allah" hawaye har sun fara zubo mata,saurin rungumeta yayi yace "kiyi shiru dan Allah.." Wani irin turasa tayi kuka yana kufce mata ganin yanda aka bud'e get d'in gidansu,abunda bata tab'a gani ba tsayin tashinta,lokacin da motarsu tayi parking a compound d'in gidan da sauri ta bud'e k'ofar gefenta ta fita cikin sauri tana had'awa da sassarfa ta nufi b'angaren Dadda,tun daga bakin k'ofa take kwaloma Dadda kira tana cewa "Hjyta kina ina? Allah sa kina cikin aminci,k'oshin lafiya da kiyayewarsa" su Mother,Aunty da Mama da sauran mutanen da suka cika parlon wanda ya had'a da su Deejah,Diyanah da surukarsu Hjy Aisha suna jiyo muryanta suka fara share hawayen dake musu sintiri a fuskokinsu,duk damuwar da suke ji akan mutuwar Dadda sun sani kuma sun tabbatar ba komai bane idan aka dangantasa da wanda Manar za ta shiga,tana sawo kai cikin parlon tayi turus ganin suna mata wani kallo mai cike da rauni,tsoro da sanyi,hawaye suna kwaranyowa fuskarta tana jujjuya kai ta fara takawa tana ratsawa cikinsu,cikin muryar kuka take cewa "kada kuce min Hjyta ce ta mutu,dan Allah kada ku fad'a min cewa taron mutanen da na gani da kukan da kuke yi saboda itane" Mother ta sunkuyar da kai tana share wasu hawaye masu zafi,haka Aunty da su Deejah,dai² lokacin su Mommella suka shigo,hawaye cike idanunsu suna sharewa,Waleed da ya san za'a samu matsala saboda yanayin da yaga ta fita daga motar ya k'arasa ya rik'eta ya jata zuwa d'akinsu da suka rayu ita da Ameerah na nan b'angaren,sanda ya zaunar da ita bakin gado a nutse ya rungumeta ya lumshe idanunsa,sai lokacin wasu zafafan hawaye suka fara zubo masa cike da rauni yake rad'amata sanyayyan kalamai masu taushi,kafin yace "hak'uri za muyi duka Lily,ubangijin da ya fimu son Hajiya yau ya amshi abarsa.." Sai kuma ya d'ora mata da nasiha,inda yake cewa "Hadith ya inganta daga Abdullahi d'an mas'ud,daga Annabi (S.A.W) yace:ba ya tare da mu,wanda yake marin fuskarsa,kuma yake yaga tufafinsa (a lokacin da wata musiba ta samesa) ko kuma yake addu'ah da irin addu'ar jahiliyya.. A yanzun babu abunda Hajiya tafi buk'ata sama da addu'o'inmu,su ne kad'ai za su kasance garkuwa a gareta,kada mu mata kuka irin na jahilan farko.." Nasiha sosai ya mata yana janyo mata ayoyi da hadisai,har ya samu ta nutsu,sai hawaye kawai suke zirya a idanunta,wannan kam bai hana ta ba saboda shima kansa hawayen yake saboda ya san Annabi (S.A.W) bai hana ba,a haka suka zauna rungume da juna tsayin lokacin da aka gama had'a gawan,Aunty tazo tayi knocking ta kirasa cikin dashewan murya tace "Waleed kuzo kuyi bankwana za'a fita da gawan" ya amsa yace "tou Aunty ga mu nan fitowa" da kyar ya lallab'a Manar suka fita saboda kukan da take,a parlor suka tarar da ahalinsu kaf sun zagaye gawan Hjy Dadda dake cikin makara,tun daga nesa Manar da ta hango makaran ta b'oye fuskarta a jikin Waleed tana hana kanta yin ihu,hawaye suna sauka fuskasa ya rik'eta yana bata hak'uri suka k'arasa,tun daga d'an nesa kadan Manar ta zube kan guiwoyinta tana toshe bakinta da duka hannuwanta,wani irin sanyayyan kuka take tana jan zuciya,a hankali ta rarrafo jikin makaran ta kwantar da kanta saman gawar Dadda,Aunty da Mother suka dafa kafad'unta suna tausarta,su kansu hawaye suke while suna fad'a mata tayi mata addu'ah,da kyar ta daure ta dunga mata addu'o'i suna amsawa da ameen,Waleed da ya jinginar da bayanta a k'irjinsa shima yana mata addu'o'i,har dai lokacin da su Daddy suka shigo tare da Abba da su Amaar,a nan suka kama makaran su shida (Abba,Daddy,Waleed,Azaan,Amaar da Dad mijin Mommella) sai Raj Jarood da hadimai da suke biye da su,aka fita da gawan,sanda aka mata sallah aka rakata gidanta na gaskiya,a nan su Waleed sukai kuka na gaske ganin duk sun juyo za su barta ita kad'anta sai halinta na gari da zai zame mata abokin zama daga nan har zuwa lokacin da Ubangiji (S.W.T) ya k'addara za'a nad'e k'asar. Bayan dawowarsu lokacin har an saka manyan tent suka zauna karb'an gaisuwa,Mai martaba sarkin Kano da wasu sarakunan yankin arewacin Nigeria,president da manyan governor's da wasu cikin ministers d'insa da akayi jana'izar Dadda da su nan suka fara musu sallama,bayan sun shiga ciki sun ma matan ta'aziyya suka tafi. Ak'alla sai da akayi sadakar bak'wai kafin aka tashi daga zaman makokin,tun daga ranar da akayi rasuwar kullum Manar cikin kuka take,musamman idan ta shiga b'angaren Dadda,sai take ganin kamar idan ta kirata za ta ganta ko taji ta amsa mata,wannan dalilin yasa Abba yasa aka rufe b'angaren,suka koma b'angaren Aunty,while a gefe d'aya kuwa tsakaninta da Waleed tun da suka zo sai dai idan sun shigo gidan ta hangesa daga nesa,wani lokacin ma ba ta ganinsa sai dai yaranta suce sunga Pappy ya shigo,washe garin bakwai Rani Naheed da Raj Jarood da yaran suka koma suka barsu a Nigeria. Cikin haka lokaci yayi ta tafiya,ranan da Dadda tayi kwana arba'in da rasuwa bayan anyi addu'ar arba'in,Abba yace ya kamata suyi shirin komawa saboda aiki da kuma yaransu da Rani suka tafi
Chapter 183 · 0% Book details