Sashe 212
Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwanaki uku kacal da dawowarta aka fara bikinsu nadra din,iya events din data fada din kusan haka aka yisu. Saidai fa tun ranar bridal shower fu'ad din bai sake barinta taje komai ba,saboda wani irin sassanyan kyau da tayi me daukan hankali cikin wata butter color gown ita da iffa da tayi order dinta tun daga Egypt,tana yawo kuma da tag din bride sister daya sake bata ranshi. Lallaba kayanta kawai takeyi,tasan halinsa sarai a kanta baida sauqi,ta samu ta saukeshi ta kuma kiyaye dukka dokokinsa har aka gama bikin lafiya. Saidai ko bayan bikin still mitar bridal shower day din ya dinga mata,saida ta samu ta bashi wani zazzafan dare guda daya sannan ta wanke kanta.
*_GRADUATION DAY_*
*@KING ABDUL'AZEE INTERNATIONAL SCHOOL*
Triplet din 'yan qasa nigeria kuma haifaffun qasar madeenatul munawwara......wasu irin yara ne da sunansu dasu kansu sukayi fice cikin makaranta dama wajenta. Bawai don kawai farinjinin 'yan uku ba.....aah hatta da kaifin basira da Allah ya zuba musu,matsanancin nutsuwa da sanin ya kamata.....inda daga qarshe kuma suka zama dalibai madiya hazaqa da qoqari cikin daliban da makarantar ta fitar.
Sanda makarantar ta tasosu ta tsaidasu saman stage tana wassafa kyawun dabi'u da hazaqar yaran sai sabreen ta kasa daurewa,ta kifa fuskarta tsakanin tafukan hannayenta tana jin wani irin alfahari da yaran da kuma qaunarsu tana ratsata.......wani irin farinciki da batasan yadda zata misaltashi ba na kyauta da baiwar yaran da Allah yayi mata,wanda a yanzun haka cikin amsa kuwwa ake sanar da kowa cewa su din cikakkun 'yan qasa ne.....gwamantin saudiyya kuma sun dauki nauyin komai da komai nasu saboda girmamawa da jin dadin yadda suka zauna da kowa cikin makarantar dama qasar lafiya.
Da qyar ta iya isa tsakiyar yaran nata don karba musu kyaututtukan karramawa da suka samu,duk da jikinta a lullube yake kirif,baka ganin komai nata sai zagayayyar fuskarta,amma duk da haka wasu sun cika da mamakin cewa itace mamansu. Tun tana iya amsa har gifts din sukafi qarfinta saida jadda dake sanye cikin wata rantsatsiyar shadda ya tako da sanyin nan nasa da nutsuwarsa ya tallafeta da wasu kayayyakin.
Ranar wata rana ce da bazata gushe ba a zukatansu,cike da tarihin da bazai kankaru ba cikin rayuwarsu.
Already sun tsara ana kammala taron zasu koma makka su sauke umra gaba dayansu,saboda nuna godiyarsu ga Allah da kuma sake roqon ubangiji ingantacciyar rayuwa me dorewa.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
*_NACE BA......._*
*_Hajjaju a ina kike siyan turare?....._*
*_NACE A INA KIKE SIYAN TURARE?_*
*_Ga wani fa........TASTED AND TRUSTED ne.......mun gwada munga ingancinsa_*
*_Da yardar Allah saikin godemin_*
*_KUNSAN DUK INDA QAMSHI YAKE ZAKA SAMENI A GURIN,MAGANAR GASKIYA KENAN AHTO_*
Golden oud
Hawi
Sandal balls
Sandal flakes
Cotton bakhoor
Kabbasine mix
Khumra(alba,alsuma,ebony,monarch,musk)
Deep crush (luxury khumra).
Signature oil
Kuleccham
Kabbasine spray
*_YA SUBHANALLAH.....hajiyata dukka wadannan zaki samesu a_*
*_PRIME SCENTS(the scents of royalty_*
*KE DAGA JIN SUNAN KINSAN ZA'A ZUBDA QAMSHI ME AJI DA DAUKAN HANKALI*
*SUNA NAN A*
*_No 3,kabiru sani lawan street,farawa layout,Maiduguri road kano_*
*BA'A KANO KIKE BA?*
*_karki damu,tuntubeta ta nan,TABBAS kayanki zasu iskeki a duk inda kike cikin aminci da yardar Allah,NA BAKI TABBACIN HAKA_*
*DANNA RUBUTUNNAN DON YIN MAGANA DA ITA KAI TSAYE*
wa.me/+2348103155915
KO KI KIRATA TA NAN
08103155915
_Zafafabiyar_
175
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
____________________________
*_PLEASE FOLLOW MY TIKTOK PAGE_*
https://www.tiktok.com/@huguma.closet?_t=ZM-8y1pf9yfIVZ&_r=1
__________________________
175
A maimakon jirgi a babbar lafiyayyar mota suka taho zuwa makka. Wata irin tafiya ce ta iyali me dadin gaske,hirrraki da labarai duka sun cika motar dake dauke da JADDA FAMILY.
Saidai duk da hakan daga can seat din baya ita da fu'ad ne zaune,tadan dora kanta saman kafadarsa tana jin kasala da wani saqe saqe da cikinta yayi mata wanda batasan Meye dalili ba.
A fili kuwa hotunan graduation din take kalla daya bayan daya. Duk inda zata wuce fu'ad da yaran sai tayi zooming ta kallesu sosai,tana jin kaman ba yaranta ba,kaman wani imagination ne a cikin duniyar mafarki ma,har sai da fa'ad daketa sauraron shirmen yaran daga gaban motar yana murmushi kadan kadan ya ankara da ita.
"Kina mamaki ne?" Kai ta daga ta kalleshi sannan ta maida saman kafadarsa.
"Ina mamaki mana hamma......yau sabreen da kowa ke mata kallon KARUWA da yara irin wannan?,sabreen din da kowa ya gaza janta a jiki yaji meye damuwarta,meye kuma uzurinta yau ita keda yarannan?......sabreen din da tafi kowacce yarinya nutsuwa da hankali saboda ita din rainon ummee ce yau ta zama haka meye sila?,ba hujja ba dalili sai yanke hukunci babu bincike". Bata tsaya jin ta bakinsa ba ta dora.
"Alhaji ahmad me citta shine asalin sunan mahaifina,wanda ya shahara da sana'ar saida citta kanunfari da sauran kayan da suka danganci wannan da wasunsu ma daga qasar larabawa ake shigo musu dasu. Abbana ya auri ummeena ne a sanda yake da matan aure biyu da yara mata goma sha biyar,ummena ce ta uku,mace me tsananin haquri da kawaicin daya sanyata taci nasarar zama da sauran matan abbana,wanda cikin su take da babbar abokiyr adawa wato bibo,wadda ita ummee ke bi. Abban mu ya tsaya sosai a kanmu,shanmu cinmu tarbiyya da iliminmu,don har yanzu tasirin dagewarsa ce a jikina na ilimin dana samu daga private school daya sakamu me tsada,tun daga matakin free nursery har secondry,duk da cewa ina js 3 abbanmu ya koma ga Allah,ummenmu itace ta jajirce naci gaba da wannan makarantar har na shiga ss3 second semester,a lokacinne Allah yayi mata rasuwa,a lokacinne asirinmu ya tonu,maraici kuma ya afko.mana gadan gadan,ummenmu ba 'yar qasar nan bace,don haka bamu da kowa a kusa damu da zai tallafemu. Sh momma sunso tafiya damu amma kawu ya saka kuka,wai ya za'a tafi da zuri'ar ahmadu yana raye?,shi yayi alqawarin kula damu kaman yadda abbanmu ya kula da rayuwarsa. Abbanmu ne ya riqeshi bayan rasuwar iyayensu tun auren abban ma na fari,bai kuma qyale kawu ba sai daya aurar dashi ya hadashi da jari yana saka ran wasu halayensa da bayaso zuwa sannan kawun ya dainasu. Da wannan yaqinin suka barmu hannunsa,ashe kuma lokaci lokaci suna masa aike da sunanmu,amma ko labari bai taba bamu ba bare muga abinda suka kawo.
....... Tom ko bayan mutuwar abba kowacce mace ita ta koma hidimar kanta da kanta,to yanzun da bamu da uwa sai ya zamana ba wanda ya damu damu,ba wanda yake dubamu,ba wanda yake damuwa da munci bamu ci ba,munsha ko bamu sha ba,mun tashi lafiya?,waye baida lafiyar?,dukka ba wanda ya saka hakan a tsarinsa. Da farko na dauka abun na wasa ne,na dauka zasuji qanmu,saina fara nema mana abinci daga dakunansu kafin na fahimci ba wanda zai iya cida mu,don da zagi nake fita a dakin da qyama da tsangwama,daga bisani dole na koma roqarwa su huda a maqota,donni ban damu naci ba,muddin sukaci shikenan tawa me sauqi ce,zan iya kwana uku ma banci komai ba,saidai nasha baqin ruwa na kwanta. Sannu a hankali suma maqotan suka fara hanani,sai ya zamana mun qarasa galabaicewa,ciwon yunwa yanason kama huda da haneefa da bata gama sanin ma me ake ba idan yunwar taji ba. Ba wanka ba wanki don ba wanda zai bamu sabulu,saidai da yake ummenmu ta saba mana da tsafta hakanan mukeyi da zallar ruwa.
Maqociyarmu kuma qawa ga bibo ita ta fara bani shawara.
"Kina da kyau sosai sabreen,kaf gidanku ba yaro me kyanki.....me zai hana ki tallata hajar jikinki?,wallahi abinci ma saikun bawa wani" A ranar hankalina yayi mugun tashi,mukayi uwaka ubaka da ita,kaf kimarta ta zube a ido na,ita kuma ta kamani tamin shegen duka akan na mata sata kuma na mata rashin kunya. Ba wanda ya damu yaji ba'asi saboda basa sonmu bamu da gata,saima tayata da bibo tayi,haka nayi kwana uku kwance ina zazzabi ba magani a dole na warke. Sanda naga yunwa na neman rayuwarmu saina fara da tambayar alhaji baqo,aboki na kusa ga mahaifinmu wanda nake kyautata zaton zai iya taimaka mana" Shuru tayi tana hadiyar wani abu me ciwo.
"Saidai abun mamaki abinda kuma ko yau na tuna yakemin ciwo,ya nemi yaci amanar amintaka,ya nemi na bashi mutuncina yaci gaba da ciyar damu duka. A nan ne naci masa mutunci saboda mamakin daya bani,kamar yadda mukayi da waccar matar shima duka yayimin ya hadamin da sharri,abu na farko daya fara qeqasarmin da zuciya,na fahimci kaman ba wanda zaiji tausayinmu a unguwar,binda yasa na kasa mantawa ko yafewa,na koma na kunna masa gobara a dakinsa data jaza masa asara me yawa,ya gano nice,yace zai kaini ga 'yan sanda,na gaya masa ina da shaidar cewa muddin ya aikata haka ni kuma nizan babbake gidansa duka da 'ya'yansa da matansa,abinda ya sakashi haqura kenan,tun daga ranar idan na ganshi sai tsaki habaici da tsartar da yawu,sai duka ya tsargi kansa yana tsoro kada na tona masa asiri,sai ya koma kaman sirikina. Daga nan saina fara yawon nema mana abinci,duk da ba cikin kyakkyawar kama nake ba,amma duk wanda ya ganni ringidi ringidi zai jani ya kaini gun cin abinci a zubamin,saina juyewa su huda a leda,sukance ki cinye,indai kin bamu hadin kai lallai abinci saikin ture. Mutun na farko daya fara nunan me hakan yake nufi na samu na gudu ina zaginsa,akayi na biyu na uku na hudu na biyar shida har goma,duk wanda yaga bazai samu abinda yakeso ba saiya qwace abincinsa. Maza da yawa haka muka dinga yi,abinda ya sake dasamin duniya ba imani.....babu me taimako don Allah sai don wani abu na daban,dana fahimci haka saina fara tunanin ta yadda zan amfana da kudadensu ba tare da mutuncina ya tabu ba.
.....salis shine mutum na farko dana fara gwada hakan a kansa,na saka masa maganin bacci a lemo,na kuma debi kudade masu yawa na gudu. Wannan kudin su suka fara canza rayuwata,na siya mana abinci me yawa,suturu da komai na fara kwalliya muka fita daga qazanta.
*_GRADUATION DAY_*
*@KING ABDUL'AZEE INTERNATIONAL SCHOOL*
Triplet din 'yan qasa nigeria kuma haifaffun qasar madeenatul munawwara......wasu irin yara ne da sunansu dasu kansu sukayi fice cikin makaranta dama wajenta. Bawai don kawai farinjinin 'yan uku ba.....aah hatta da kaifin basira da Allah ya zuba musu,matsanancin nutsuwa da sanin ya kamata.....inda daga qarshe kuma suka zama dalibai madiya hazaqa da qoqari cikin daliban da makarantar ta fitar.
Sanda makarantar ta tasosu ta tsaidasu saman stage tana wassafa kyawun dabi'u da hazaqar yaran sai sabreen ta kasa daurewa,ta kifa fuskarta tsakanin tafukan hannayenta tana jin wani irin alfahari da yaran da kuma qaunarsu tana ratsata.......wani irin farinciki da batasan yadda zata misaltashi ba na kyauta da baiwar yaran da Allah yayi mata,wanda a yanzun haka cikin amsa kuwwa ake sanar da kowa cewa su din cikakkun 'yan qasa ne.....gwamantin saudiyya kuma sun dauki nauyin komai da komai nasu saboda girmamawa da jin dadin yadda suka zauna da kowa cikin makarantar dama qasar lafiya.
Da qyar ta iya isa tsakiyar yaran nata don karba musu kyaututtukan karramawa da suka samu,duk da jikinta a lullube yake kirif,baka ganin komai nata sai zagayayyar fuskarta,amma duk da haka wasu sun cika da mamakin cewa itace mamansu. Tun tana iya amsa har gifts din sukafi qarfinta saida jadda dake sanye cikin wata rantsatsiyar shadda ya tako da sanyin nan nasa da nutsuwarsa ya tallafeta da wasu kayayyakin.
Ranar wata rana ce da bazata gushe ba a zukatansu,cike da tarihin da bazai kankaru ba cikin rayuwarsu.
Already sun tsara ana kammala taron zasu koma makka su sauke umra gaba dayansu,saboda nuna godiyarsu ga Allah da kuma sake roqon ubangiji ingantacciyar rayuwa me dorewa.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
*_NACE BA......._*
*_Hajjaju a ina kike siyan turare?....._*
*_NACE A INA KIKE SIYAN TURARE?_*
*_Ga wani fa........TASTED AND TRUSTED ne.......mun gwada munga ingancinsa_*
*_Da yardar Allah saikin godemin_*
*_KUNSAN DUK INDA QAMSHI YAKE ZAKA SAMENI A GURIN,MAGANAR GASKIYA KENAN AHTO_*
Golden oud
Hawi
Sandal balls
Sandal flakes
Cotton bakhoor
Kabbasine mix
Khumra(alba,alsuma,ebony,monarch,musk)
Deep crush (luxury khumra).
Signature oil
Kuleccham
Kabbasine spray
*_YA SUBHANALLAH.....hajiyata dukka wadannan zaki samesu a_*
*_PRIME SCENTS(the scents of royalty_*
*KE DAGA JIN SUNAN KINSAN ZA'A ZUBDA QAMSHI ME AJI DA DAUKAN HANKALI*
*SUNA NAN A*
*_No 3,kabiru sani lawan street,farawa layout,Maiduguri road kano_*
*BA'A KANO KIKE BA?*
*_karki damu,tuntubeta ta nan,TABBAS kayanki zasu iskeki a duk inda kike cikin aminci da yardar Allah,NA BAKI TABBACIN HAKA_*
*DANNA RUBUTUNNAN DON YIN MAGANA DA ITA KAI TSAYE*
wa.me/+2348103155915
KO KI KIRATA TA NAN
08103155915
_Zafafabiyar_
175
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
____________________________
*_PLEASE FOLLOW MY TIKTOK PAGE_*
https://www.tiktok.com/@huguma.closet?_t=ZM-8y1pf9yfIVZ&_r=1
__________________________
175
A maimakon jirgi a babbar lafiyayyar mota suka taho zuwa makka. Wata irin tafiya ce ta iyali me dadin gaske,hirrraki da labarai duka sun cika motar dake dauke da JADDA FAMILY.
Saidai duk da hakan daga can seat din baya ita da fu'ad ne zaune,tadan dora kanta saman kafadarsa tana jin kasala da wani saqe saqe da cikinta yayi mata wanda batasan Meye dalili ba.
A fili kuwa hotunan graduation din take kalla daya bayan daya. Duk inda zata wuce fu'ad da yaran sai tayi zooming ta kallesu sosai,tana jin kaman ba yaranta ba,kaman wani imagination ne a cikin duniyar mafarki ma,har sai da fa'ad daketa sauraron shirmen yaran daga gaban motar yana murmushi kadan kadan ya ankara da ita.
"Kina mamaki ne?" Kai ta daga ta kalleshi sannan ta maida saman kafadarsa.
"Ina mamaki mana hamma......yau sabreen da kowa ke mata kallon KARUWA da yara irin wannan?,sabreen din da kowa ya gaza janta a jiki yaji meye damuwarta,meye kuma uzurinta yau ita keda yarannan?......sabreen din da tafi kowacce yarinya nutsuwa da hankali saboda ita din rainon ummee ce yau ta zama haka meye sila?,ba hujja ba dalili sai yanke hukunci babu bincike". Bata tsaya jin ta bakinsa ba ta dora.
"Alhaji ahmad me citta shine asalin sunan mahaifina,wanda ya shahara da sana'ar saida citta kanunfari da sauran kayan da suka danganci wannan da wasunsu ma daga qasar larabawa ake shigo musu dasu. Abbana ya auri ummeena ne a sanda yake da matan aure biyu da yara mata goma sha biyar,ummena ce ta uku,mace me tsananin haquri da kawaicin daya sanyata taci nasarar zama da sauran matan abbana,wanda cikin su take da babbar abokiyr adawa wato bibo,wadda ita ummee ke bi. Abban mu ya tsaya sosai a kanmu,shanmu cinmu tarbiyya da iliminmu,don har yanzu tasirin dagewarsa ce a jikina na ilimin dana samu daga private school daya sakamu me tsada,tun daga matakin free nursery har secondry,duk da cewa ina js 3 abbanmu ya koma ga Allah,ummenmu itace ta jajirce naci gaba da wannan makarantar har na shiga ss3 second semester,a lokacinne Allah yayi mata rasuwa,a lokacinne asirinmu ya tonu,maraici kuma ya afko.mana gadan gadan,ummenmu ba 'yar qasar nan bace,don haka bamu da kowa a kusa damu da zai tallafemu. Sh momma sunso tafiya damu amma kawu ya saka kuka,wai ya za'a tafi da zuri'ar ahmadu yana raye?,shi yayi alqawarin kula damu kaman yadda abbanmu ya kula da rayuwarsa. Abbanmu ne ya riqeshi bayan rasuwar iyayensu tun auren abban ma na fari,bai kuma qyale kawu ba sai daya aurar dashi ya hadashi da jari yana saka ran wasu halayensa da bayaso zuwa sannan kawun ya dainasu. Da wannan yaqinin suka barmu hannunsa,ashe kuma lokaci lokaci suna masa aike da sunanmu,amma ko labari bai taba bamu ba bare muga abinda suka kawo.
....... Tom ko bayan mutuwar abba kowacce mace ita ta koma hidimar kanta da kanta,to yanzun da bamu da uwa sai ya zamana ba wanda ya damu damu,ba wanda yake dubamu,ba wanda yake damuwa da munci bamu ci ba,munsha ko bamu sha ba,mun tashi lafiya?,waye baida lafiyar?,dukka ba wanda ya saka hakan a tsarinsa. Da farko na dauka abun na wasa ne,na dauka zasuji qanmu,saina fara nema mana abinci daga dakunansu kafin na fahimci ba wanda zai iya cida mu,don da zagi nake fita a dakin da qyama da tsangwama,daga bisani dole na koma roqarwa su huda a maqota,donni ban damu naci ba,muddin sukaci shikenan tawa me sauqi ce,zan iya kwana uku ma banci komai ba,saidai nasha baqin ruwa na kwanta. Sannu a hankali suma maqotan suka fara hanani,sai ya zamana mun qarasa galabaicewa,ciwon yunwa yanason kama huda da haneefa da bata gama sanin ma me ake ba idan yunwar taji ba. Ba wanka ba wanki don ba wanda zai bamu sabulu,saidai da yake ummenmu ta saba mana da tsafta hakanan mukeyi da zallar ruwa.
Maqociyarmu kuma qawa ga bibo ita ta fara bani shawara.
"Kina da kyau sosai sabreen,kaf gidanku ba yaro me kyanki.....me zai hana ki tallata hajar jikinki?,wallahi abinci ma saikun bawa wani" A ranar hankalina yayi mugun tashi,mukayi uwaka ubaka da ita,kaf kimarta ta zube a ido na,ita kuma ta kamani tamin shegen duka akan na mata sata kuma na mata rashin kunya. Ba wanda ya damu yaji ba'asi saboda basa sonmu bamu da gata,saima tayata da bibo tayi,haka nayi kwana uku kwance ina zazzabi ba magani a dole na warke. Sanda naga yunwa na neman rayuwarmu saina fara da tambayar alhaji baqo,aboki na kusa ga mahaifinmu wanda nake kyautata zaton zai iya taimaka mana" Shuru tayi tana hadiyar wani abu me ciwo.
"Saidai abun mamaki abinda kuma ko yau na tuna yakemin ciwo,ya nemi yaci amanar amintaka,ya nemi na bashi mutuncina yaci gaba da ciyar damu duka. A nan ne naci masa mutunci saboda mamakin daya bani,kamar yadda mukayi da waccar matar shima duka yayimin ya hadamin da sharri,abu na farko daya fara qeqasarmin da zuciya,na fahimci kaman ba wanda zaiji tausayinmu a unguwar,binda yasa na kasa mantawa ko yafewa,na koma na kunna masa gobara a dakinsa data jaza masa asara me yawa,ya gano nice,yace zai kaini ga 'yan sanda,na gaya masa ina da shaidar cewa muddin ya aikata haka ni kuma nizan babbake gidansa duka da 'ya'yansa da matansa,abinda ya sakashi haqura kenan,tun daga ranar idan na ganshi sai tsaki habaici da tsartar da yawu,sai duka ya tsargi kansa yana tsoro kada na tona masa asiri,sai ya koma kaman sirikina. Daga nan saina fara yawon nema mana abinci,duk da ba cikin kyakkyawar kama nake ba,amma duk wanda ya ganni ringidi ringidi zai jani ya kaini gun cin abinci a zubamin,saina juyewa su huda a leda,sukance ki cinye,indai kin bamu hadin kai lallai abinci saikin ture. Mutun na farko daya fara nunan me hakan yake nufi na samu na gudu ina zaginsa,akayi na biyu na uku na hudu na biyar shida har goma,duk wanda yaga bazai samu abinda yakeso ba saiya qwace abincinsa. Maza da yawa haka muka dinga yi,abinda ya sake dasamin duniya ba imani.....babu me taimako don Allah sai don wani abu na daban,dana fahimci haka saina fara tunanin ta yadda zan amfana da kudadensu ba tare da mutuncina ya tabu ba.
.....salis shine mutum na farko dana fara gwada hakan a kansa,na saka masa maganin bacci a lemo,na kuma debi kudade masu yawa na gudu. Wannan kudin su suka fara canza rayuwata,na siya mana abinci me yawa,suturu da komai na fara kwalliya muka fita daga qazanta.