Sashe 120
Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read
*MAAMAH*
Idan tace hankalinta a kwance yake daga daren zuwa safiyar tayi qarya. Ta kirashi ta kirashi har batasan adadin sau nawa ba. Tabbas ta sani,a yanxu duk duniya idan ameenatu tace itace mahaifiya ga fu'ad,kuma tana tuhumarta batan sabreen ba wanda ya isa ya hana a daureta,ba wanda zai fiddata idan ba fu'ad din ba,da sauran mutuncinta,bataso wasan ya qare a haka,saidai hakan ya sake ninka qiyayyar anni sosai a ranta. Ita daya taketa shawa kanta alwashin saita yiwa ameenatu abu mafi munin da ba zata tabawa mantawa da ita ba,idan don tayi wannan ne don ta nuna mata iyakarta ne ganin suna qasar da ba tasu ba.....to tabbas ita kuma zata bar mata wani babban tabo a rayuwarta da ba zata taba mantawa dashi ba.
Musaddiq ta kira ta sanyashi nema mata fu'ad din,saidai shima kiran duniya wayar sunqi tafiya.
"Maamah wayoyinsa a kulle suke" Maganan data sake sakata a taraddadi da tunane tunane iri iri.
"Kada fa ya zamana ameenatu ta salwantar mata da yaro ne takeson tayi garkuwa da ita akan batun haka da wuri?" Wannan shine tunanin daketa mata kai kawo.
"Ya kamata ki xama cikin shiri.....ki xama a ankare.....karki nuna mata tsoronki,ki tabbatar mata da.naki zargin kema" Abinda zuciyarta take nanata mata kenan,wanda shine kuma ya bata qwarin gwiwa.
Cikin kwanakin sai ya zamana wani irin zama ake a gidan,kallo kallo kawai akeyi tsakanin maamah da anni din. Duk da maamah tana cikin d'ari d'ari da tunanin inda fu'ad da sabreen dinma suke......amma ta azawa ranta wani dakiya. Ta fannin annin kowanne taku na maamah din saman idanunta yake,ba komai take dubawa ba sai idanun yaransu da suke rayuwa guri daya,zai zame musu wani abu na daban kuma na tashin hankali idan suka ga wani sabani muraran a tsakaninsu,banda hakan a shirye anni yake akan maamah wannan karon.....duk da tana danjin relief idan farouq na bata tabbacin fu'ad da sabreen din suna lafiya.
Farouq din ya fahimci abinda ke faruwa,saidai bai nuna musu komai ba,yayi ma kaman bai sani ba,saidai time to time shima yana neman fu'ad din ta waya,amma dif kakeji ko sau daya bai taba katarin samunsa ba.....a haka sannu a sannu sai gashi an kwashe sati guda cif ba wanda yaji motsinsu ko yasan inda suke.
Zuwa sannan hankalin anni ya tashi sosai,kusan kullum sai tasa farouq ya kira mata shi,mafi qaranci sau biyu a rana,saboda kwanakin barinsu Maldives kusan za'a ce yayi,kwana uku ko hudu suka rage musi,gashi babu shi ba sabreen din.
Tun tana yiwa maamah din kara har abun yaci tura,ranar daya rage kwanaki uku subar qasar,da wani yammaci suna parlor. Amna ke mata kalba saman dogon gashinta da tafi masa kalba akan kitso,maamah tana daga gefe zaune tana kallo cikin tv. Ta tsiri wannan zamanne kawai don ta nunawa anni ba abinda zai tsoratata,hakanan itama me cikakken iko ce,duk da cikin rashin cikakkiyar nutsuwa itama take. Ba sabreen ce ma damuwarta ba danta shine damuwarta,idan tana da damuwa akan sabreen din bazai wuce na yadda take gudun kada anni ta fake da wannan ta tozartata a idon duniya ba.
Farouq ne ya shigo da sallama,kaman yadda suke koyi da tarbiyyar anni da umarninta,ya yiwa maamah barka da gida,ta amsa masa a d'age kaman yadda ta saba. Mugun haushinsa takeji.....tana ganinsa a asalin tantirin munafuki tun daga quruciyarsa kawo yanzu,kai tsaye zata iya cewa shine kanwa uwar gami da yaja mata yaro cikin gidansu ya hadashi da mayun iyayensa da suka kasa sakar mata kurwar d'a,suka hanata taci arziqin d'anta yadda ya dace. Ko a yanzun gani take cutar fu'ad kawai yakeyi yana amfana da arziqinsa,yana tatsarsa ne shima.....ba wani tare da suka samo arziqin,ba kuma wai iya harkar noma da kayan abinci yake wannan fantamawar ba,dukiyar gold da diamond din d'anta ce.
"Farouq......kwanaki uku suka rage mana mubar Maldives.....ka samomin 'ya'yana?" Tayi maganar cikin salon son isar da saqo ga maamah.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
_Zafafabiyar_
104
Kalmar 'ya'yana din kuwa ta daki zuciyar maamah da wani matsanancin kishi. Wato har fu'ad dinma ya tashi daga sunan dan riqo ya koma danta?.
"Aah anni....inata dai qoqari" Ya amsa mata yana fahimtar inda saqonta yasa gaba. Kai ta jijjjiga
"Zan sabawa fu'ad kuwa muddin qafafunsa yasa ya tafi bai sanarwa iyayensa ba.....idan kuma wani keda hannu kan hakan....na rantse da Allah ko waye bazan barshi ba.....tashi kaje,tsakanin yau da gobe nakeso ka lalubomin shi" Kai kawai kada mata yana tashi,maimakon ya koma daki sai ya juya yana sake ficewa a gidan.
Yau din Jordan ya nema kai tsaye,shima ya gaya masa tun randa suka fita tare bai sake ganinsa ba. Ci gaba yayi da bibiyarsa ta waya amma a banza,sai ya koma ya lalubi system dinsa da yakan ajiye schedule nasa da komai. Yasan password nasa da komai don haka kai tsaye ya bude ya shiga. Zallar aminci ne da yarda da kuma dawwamammiyar qauna,shima iya abinda yaje nema ya shiga ya duba kawai ya fito. Bai samu bayanin komai ba,hasalima bai ajiye inda zashi ba banda ranar da sukayi zasu fita din satin baya daya wuce ranar daya bace kenan.
Awa daya ya bawa ransa zai sake kiransa,idan bai sameshi ba kuwa aikin safa da marwa ya sameshi cikin tsibirin Maldives,wala'alla sai yayi hayar boat ko skis ya gewaye tsibirin Maldives ya nemowa anni 'ya'yanta.
"Oops.....wannan soyayya taku nima ta jefani kwale kwale.....where are you?.....anni ke kika jawo,da kin damqa masa matarsa salin alin dani kaina ban tsinciki kaina a halin da nake ciki ba" Ya fada yana furzar da iska daga bakinsa gami da yin relaxing jikin kujera yana lumshe ido. Murmushi ne kuma ya qwace masa saboda hango fuskar maamah da yayi,tayi wani laushi da yaushi ba tare data fahimci hakan ba
"Wato anni kema kinsan takan tsiya?" Ya fada qasan ransa yana komawa ya kwanta sosai saman sofa din.
Idan tace hankalinta a kwance yake daga daren zuwa safiyar tayi qarya. Ta kirashi ta kirashi har batasan adadin sau nawa ba. Tabbas ta sani,a yanxu duk duniya idan ameenatu tace itace mahaifiya ga fu'ad,kuma tana tuhumarta batan sabreen ba wanda ya isa ya hana a daureta,ba wanda zai fiddata idan ba fu'ad din ba,da sauran mutuncinta,bataso wasan ya qare a haka,saidai hakan ya sake ninka qiyayyar anni sosai a ranta. Ita daya taketa shawa kanta alwashin saita yiwa ameenatu abu mafi munin da ba zata tabawa mantawa da ita ba,idan don tayi wannan ne don ta nuna mata iyakarta ne ganin suna qasar da ba tasu ba.....to tabbas ita kuma zata bar mata wani babban tabo a rayuwarta da ba zata taba mantawa dashi ba.
Musaddiq ta kira ta sanyashi nema mata fu'ad din,saidai shima kiran duniya wayar sunqi tafiya.
"Maamah wayoyinsa a kulle suke" Maganan data sake sakata a taraddadi da tunane tunane iri iri.
"Kada fa ya zamana ameenatu ta salwantar mata da yaro ne takeson tayi garkuwa da ita akan batun haka da wuri?" Wannan shine tunanin daketa mata kai kawo.
"Ya kamata ki xama cikin shiri.....ki xama a ankare.....karki nuna mata tsoronki,ki tabbatar mata da.naki zargin kema" Abinda zuciyarta take nanata mata kenan,wanda shine kuma ya bata qwarin gwiwa.
Cikin kwanakin sai ya zamana wani irin zama ake a gidan,kallo kallo kawai akeyi tsakanin maamah da anni din. Duk da maamah tana cikin d'ari d'ari da tunanin inda fu'ad da sabreen dinma suke......amma ta azawa ranta wani dakiya. Ta fannin annin kowanne taku na maamah din saman idanunta yake,ba komai take dubawa ba sai idanun yaransu da suke rayuwa guri daya,zai zame musu wani abu na daban kuma na tashin hankali idan suka ga wani sabani muraran a tsakaninsu,banda hakan a shirye anni yake akan maamah wannan karon.....duk da tana danjin relief idan farouq na bata tabbacin fu'ad da sabreen din suna lafiya.
Farouq din ya fahimci abinda ke faruwa,saidai bai nuna musu komai ba,yayi ma kaman bai sani ba,saidai time to time shima yana neman fu'ad din ta waya,amma dif kakeji ko sau daya bai taba katarin samunsa ba.....a haka sannu a sannu sai gashi an kwashe sati guda cif ba wanda yaji motsinsu ko yasan inda suke.
Zuwa sannan hankalin anni ya tashi sosai,kusan kullum sai tasa farouq ya kira mata shi,mafi qaranci sau biyu a rana,saboda kwanakin barinsu Maldives kusan za'a ce yayi,kwana uku ko hudu suka rage musi,gashi babu shi ba sabreen din.
Tun tana yiwa maamah din kara har abun yaci tura,ranar daya rage kwanaki uku subar qasar,da wani yammaci suna parlor. Amna ke mata kalba saman dogon gashinta da tafi masa kalba akan kitso,maamah tana daga gefe zaune tana kallo cikin tv. Ta tsiri wannan zamanne kawai don ta nunawa anni ba abinda zai tsoratata,hakanan itama me cikakken iko ce,duk da cikin rashin cikakkiyar nutsuwa itama take. Ba sabreen ce ma damuwarta ba danta shine damuwarta,idan tana da damuwa akan sabreen din bazai wuce na yadda take gudun kada anni ta fake da wannan ta tozartata a idon duniya ba.
Farouq ne ya shigo da sallama,kaman yadda suke koyi da tarbiyyar anni da umarninta,ya yiwa maamah barka da gida,ta amsa masa a d'age kaman yadda ta saba. Mugun haushinsa takeji.....tana ganinsa a asalin tantirin munafuki tun daga quruciyarsa kawo yanzu,kai tsaye zata iya cewa shine kanwa uwar gami da yaja mata yaro cikin gidansu ya hadashi da mayun iyayensa da suka kasa sakar mata kurwar d'a,suka hanata taci arziqin d'anta yadda ya dace. Ko a yanzun gani take cutar fu'ad kawai yakeyi yana amfana da arziqinsa,yana tatsarsa ne shima.....ba wani tare da suka samo arziqin,ba kuma wai iya harkar noma da kayan abinci yake wannan fantamawar ba,dukiyar gold da diamond din d'anta ce.
"Farouq......kwanaki uku suka rage mana mubar Maldives.....ka samomin 'ya'yana?" Tayi maganar cikin salon son isar da saqo ga maamah.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
_Zafafabiyar_
104
Kalmar 'ya'yana din kuwa ta daki zuciyar maamah da wani matsanancin kishi. Wato har fu'ad dinma ya tashi daga sunan dan riqo ya koma danta?.
"Aah anni....inata dai qoqari" Ya amsa mata yana fahimtar inda saqonta yasa gaba. Kai ta jijjjiga
"Zan sabawa fu'ad kuwa muddin qafafunsa yasa ya tafi bai sanarwa iyayensa ba.....idan kuma wani keda hannu kan hakan....na rantse da Allah ko waye bazan barshi ba.....tashi kaje,tsakanin yau da gobe nakeso ka lalubomin shi" Kai kawai kada mata yana tashi,maimakon ya koma daki sai ya juya yana sake ficewa a gidan.
Yau din Jordan ya nema kai tsaye,shima ya gaya masa tun randa suka fita tare bai sake ganinsa ba. Ci gaba yayi da bibiyarsa ta waya amma a banza,sai ya koma ya lalubi system dinsa da yakan ajiye schedule nasa da komai. Yasan password nasa da komai don haka kai tsaye ya bude ya shiga. Zallar aminci ne da yarda da kuma dawwamammiyar qauna,shima iya abinda yaje nema ya shiga ya duba kawai ya fito. Bai samu bayanin komai ba,hasalima bai ajiye inda zashi ba banda ranar da sukayi zasu fita din satin baya daya wuce ranar daya bace kenan.
Awa daya ya bawa ransa zai sake kiransa,idan bai sameshi ba kuwa aikin safa da marwa ya sameshi cikin tsibirin Maldives,wala'alla sai yayi hayar boat ko skis ya gewaye tsibirin Maldives ya nemowa anni 'ya'yanta.
"Oops.....wannan soyayya taku nima ta jefani kwale kwale.....where are you?.....anni ke kika jawo,da kin damqa masa matarsa salin alin dani kaina ban tsinciki kaina a halin da nake ciki ba" Ya fada yana furzar da iska daga bakinsa gami da yin relaxing jikin kujera yana lumshe ido. Murmushi ne kuma ya qwace masa saboda hango fuskar maamah da yayi,tayi wani laushi da yaushi ba tare data fahimci hakan ba
"Wato anni kema kinsan takan tsiya?" Ya fada qasan ransa yana komawa ya kwanta sosai saman sofa din.