Sashe 180
Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kalar makuba kaman an diga jini. "Why maamah.....why amna?!" Ya furta da wani irin sauti me cike da razani mamaki dake cakude da karyewa yana wara hannuwansa da kuma watsasu kaman wanda yake dakon kama wani abu. Wani irin shock taji,wanda ya kusa sanya numfashinta dakatawa na wucin gadi. "Me yasa maamah?.....me yasa?,idan ni kinyimin.......d'anki ne.....idan kin yiwa musaddiq.......d'anki ne......amma amnah fa?!" Ya fada da wata irin murya dake neman fara rawa saboda tsananin sarewa da dukkan komai,ya kuma qarasa maganar yana nuna waje da yatsarsa. "Me amna ta aikata maamah.....meye laifinta?" Ya kuma fada da yanayin mutumin da ya soma zarewa. "Idan kika bada kai bori zai hau.....idan kuma baka iya kama barawo ba saishi ya kamaka" Wani sashe na rubabbiyar zuciyarta ya sake bijiro mata da wannan shawarar,shawarar data qarfafi dukkan gabbanta,ta soma qoqarin tattaro kowacce nutsuwa tata,sannan kuma ta hana kanta shiga d'imuwa. "Kai fu'ad.....kalleni nan da kyau,idan kana cin qasa ka kiyayi ta shuru....ni dinnan nice uwarka,baka da sama dani.....ohhhh,wato kaje an karanto maka abinda zakacemin da kalar rashin kunyar da zaka yimin.....dukka ameenatu ta yo maka katunsa shine zakazo ka saukemin?!" "Ameenatu ameenatu dai?,ameenatun da batayi miki komai ba face alkhairi?,ameenatun da ta rungumi yaran da kikaji cewa baki buqatarsu?,ameenatun data yarda ta zauna ta kashe tata rayuwar saboda ta 'ya'yan da kika watsarwa duniya?,akwai wani alkhairi sama da wannan?,akwaishi......wata can daban tayi abinda uwa ta gaza yi?,wata can daban tayi abinda uwa take ganin ya zame mata babban aiki?" Ya qarasa fada yana zuba mata ido,qirjinsa yana sama da qasa yana jin kamar ciwon zuciya ne yake shirin kamashi. "Kin dawo kin sake kashemu a karo na biyu bayan wancan kisan da kika yiwa rayuwarmu.......me mukayi miki haka?,laifinmu ne da kika haifemu alhalin baki buqatarmu?" Ya fada a tausashe da wani irin rauni daya sanya idanunsa fitar hawaye "Daga kowanne bangare......cikin binciken kowanne laifi Maamah dai mahaifiyar fu'ad?,mahaifiyarsa?.....maamah dai?,wadda tayi silar zuwansa duniya?,maamahn ita ta dauke amna?,amna diya ga hamza kibiya?,mutumin daya zame musu uba......bango madafarsu?,ya tallafesu a sanda duniya tayi watsi dasu,ya rungumesu,a sanda ita da take Mazaunin uwar data kawosu duniya ta sanya qafa tayi wancakali dasu?.....ya rungumi farincikinsu da baqincikinsu?,ya rabu da duk wanda zaice baya sonsu?,ya qara zafin nemansa saboda su.......yayi musu riga yayi musu wando?,yayi kawar da dauda da duhun jahilci daga qwaqwalensu?,ya daga darajarsu a idanun duniya ta hanyar haskasu da hasken ilimi?,ya maidasu mutane ta hanyar basu ilimin addinin islama?,ya karbesu a matsayin 'ya'yan da shine yayi silar zuwansu duniya bawai uban riqo ba?,yayi musu gatan da ko 'ya'yan cikinsa bai musu ba?.....amnan dai itace d'iya ga ameenatu......ameenatun data dawowa auren hamza saboda yaran?,ameenatun data sadaukar da duk wata kulawa da lokacinta akan yaran?,ameenatun da bata yarda da wani abu me cutarwa ya rabesu ba?,ameenatun da idan kanaso kaga farincikinta.....ko kaga kirkinta ka yabi musaddiq.......ka yabi fu'ad......idan kanaso ku bata alaqarku taja baya ka zagesu ko ka kushesu.....ameenatun da ta sadaukar da lafiyarta saboda su su rayu cikin aminci?,taqi kwanciya ta huta sabodasu?,taqi ci saboda saboda basuci ba?,taqi sha saboda basu sha ba?......" Ya sake tsayawa saboda yadda numfashi ke masa wahalar shaqa. "Laifin ameenatu rainon 'ya'yanki da tayi......laifin ameenatu inganta rayuwar 'ya'yanki.....idan duka haka ne ita kuma SABREEEN FA?!". Wannan tambayar daya jefa mata tafi kowacce gigitata. Sabreen?,ya tabbata ta qarasa bude mata aiki kenan kaman yadda taci alwashi?. "Ni na kawota rayuwarka.....kuma a yanzu bani da buqatar kasancewarku......na nuna maka ta dukka hanyar data kamata amma saboda banda kima da martaba a idanunka ka gagara fahimta". "Sai hakan yanzama license ya zama halaccin da zaki tura wani d'a namiji gidan aurenta.......dakin da d'anki ya gina saboda matarsa ta sunnah?.....yaje ya keta hurumin ubangiji?,.......kin auramin sabreen saboda ki.mallaki fu'ad......fu'ad din da bai mallaki wuta ko aljanna ba......fu'ad din da bai mallaki rayuwa ko mutuwa ba.......bai mallaki komai ba face wata aba da ake kira DUKIYA wadda ka iya zama fitina da jarrabawa ga bawa.......". Yana kaiwa qarshe ya jawo littafi da abun rubutun daya gani ajiye a gefe,ya jawo side table ya ajiye a tsakaninsu ya daga idonsa yana kallonta duba na kai tsaye. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 _Zafafabiyar_ 150 *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX "Na baki dama......daga farkon littafin nan har bangonsa ki rubuta adadin kudin da kikeso......na baki dama ki rubuta adadin alatun rayuwar da kikeso......na baki dama ki rubuta tsarin rayuwarki na shekaru dari nan gaba idan har zaki kai sannan......ni kuma zan tabbatar miki da wannan mafarkin,muddin zaki zare kanki daga rayuwarmu.......muddin zaki fita salin alin daga rayuwarmu......muddin zakiyi nesa da rayuwarmu......indai kin amince zaki bar iyalin ameenatu su rayu cikin salama su kuma zauna lafiya........ina fada miki hakanne cikin harshe na girmamawa.......ina gaya miki hakanne saboda har yanzu sunanki MAHAIFIYARMU.......Duk da girman abubuwan da kika aikatawa mutanen da basuji ba basu gani ba......ina gaya miki wannan zabinne saboda shine zaifi mana sauqi mu dake" Ya qarasa maganar yana jin wani mulmulallen dutsen wuta yana tsaya masa tsakanin wuyansa da qirjinsa yana qoqarin turashi da qyar. Fata yakeyi inama ace wani ko wata ce can daban suka aikata musu wannan abun ba maamah ba?......inama ace wasu mutanen ne daban keda alhakin dukka wadannan abubuwan ba maamah ba?,ya rantse da Allah da sai ya ganar dashi kuskuren bari da yayi uwarsa ta haifesa zuwa gidan duniyar ma gaba daya. "Fu'ad!.....ni kake gayawa wannan maganar?,ni kake cewa zaka rabu dani saboda ameenatu?" Ta tambaya tana jin wani irin tashin hankalin jahiltar matsayin ameenatu da tayi a baya. Ashe har zai iya katse alaqar uwa tsakaninsu saboda ameenatun dai?. "Fu'ad!.....ka saurareni da kyau!......." "Jaffal qalam" Ya fada yana miqewa daga gabanta. Zuciya da shaidan dukka suna kusa,duk sanda zai kalli fuskarta fuskar mahaifinsa yake kalla a tayi watsi dashi cikin tsananin ciwo bayan ta gama illatawa luguiguita lafiyarsa cikin mugunta.......duk sanda zai kalleta saiya tuna sanda take cida Mahaifinsu da abubuwan da aka hanashi ci ko sha saboda hakan zai iya zama sanadin komai.....ciki harda MUTUWARSA.......duk sanda ya kalleta saiya tuna sanda JADDA ta mutu saman cinyarsu saboda rashin gata suka kwana da gawarta ba wanda ya ko leqosu sai bayan wayewar gari......duk sanda ya kalli fuskarta sai ya tuna sanda musaddiq ke kwana yana kuka harda shidewa cikin kewa da qauna yana kiran sunanta.....burinsa shine kawai ya ganta......har yanzu kunnuwansa sun gaza manta yadda aka saka abun rushe gini ake dukan ginin gidan da mahaifinsu ya wahala da dukka qarfinsa ya ginashi don su rayu a ciki......ta badashi a mazaunin jingina ta karbi kudaden ta nausa zuwa duniya "Wannan dama ce a wajenki cikin girmamawa da kuma baki abinda kiketa harin mallaka din tsahon shekaru kina fadi tashi.....ki rubuta!....ki rubuta!!.....ki rubuta!!!!....ki gayyato wasu ma su tayaki rubutun?!!!,wannan damar ce kawai ta rage......'yanci muke nema!!!!,yanci muke buqata....." Sai ya hade hannayensa alamun roqo "A wannan karon da kanmu muke roqarki ki tafi ki barmu kaman yadda kikayi a baya". Sai ya fara tafiya da baya da baya idanunshi a kanta yana barin falon. Irin kallon da ya jima baiyi mata irinsa ba. Ya dade rabon daya sanya idonsa cikin nata,ya dade rabon daya iya daga kai ya dubeta,tana hango abubuwa da yawa cikin idanunsa. "Idan kika rubuta hakan yana bawa ameenatu tabbacin kinbar mata su dama dukkan wata dama ko matsayi da zasu sake takawa a gaba.....kinbar mata su da dukka wani arziqi da zai sake habaka nasu......kinbar mata dukkan wata alfarma ta amsa sunan UWAR ME JADDA har abada......iya abinda kika samu daman rubutawa shine kawai naki rabon har abada.....baki da wani sauran dama ko rabo a jikinsu saidai idan sun rigaki MUTUWA" Maganar da shaidaniyar zuciyarta ke gaya mata kenan sanda yake dab da fita a falon,abinda ya sanyata zabura ta miqe,sai wani irin jiri ya taso mata,amma cikin tsananin taurin rai dana zuciya ta cije ta kuma soma takawa tana binsa da hanzari gami da qwalla kiran sunansa. Turus yayi ya tsaya gaban gate din gidan yana kallon tarin 'yan press da suka cika qofar gidan maqil. "Da gaske ne kenan yallabai.....mamarka itace tayi kidnapping d'iyar alhaji hamza kibiya dake kwance a asibiti a yanzu tana jinya?,yanzu haka ma akwai d'iyar qawarta a cikin gidan nan da tayi!kidnapping nata tsahon watanni ba'a sani ba me suna laila?" . Wani abu yaji yana neman kayar dashi,abu daya ya saka masa sassauci ganin yadda dukkaninsu suka sauke cameras dinsu a kanshi cikin nuna masa girmamawa. Kasa magana yayi cikin tsananin mamakin yadda akayi!maganan ya fita?,waye kuma ya gayyatosu?,amsar da ya sameta kai tsaye daga bakin wani dan jarida. "Mun samu half details na cikakken labarin daga wajen aminiyarta hajja harira......ta kuma bamu tabbacin zamu samu full din daga bakin hajiya mariya ahmad" Ya qarashe fadi sanda maamah ki fitowa da sassarfa tana qwala kiran sunan fu'ad din. Waiwayawa yayi ya zube idanunsa a kanta a sanda sam bata lura da taron da dama ita suke kwadayin gani ba.....malam sa'adu ya tsaidasu da qyar ba,sai kawai ya dauke kanshi ya kuma dubesu da dakakkiyar muryarsannan dake qara masa kwarjini,wadda a yau take cakude da bacin rai yace. "Ku bani hanya....bani keda labarin ba". Tsakiya suka buda masa ya fara wucewa da sassarfa,bayajin akwai wani abu da zaiyi mata.....ba wani abu da yayi saura da zai iyayi mata shi "Fu'ad......a matsayina na mahaifiyarka ina me baka umarnin........" "Yauwa.....shikenan ma.....gata nan ta fito" Yaji muryoyin wasu a cikin su suna fadi gami da kunna cameras dinsu suka saitasu sannan sukayi kanta. "Kada ki damu,wataqila sun soma fahimtar kece mahaifiya ga fu'ad din.....girman ya fara dawo miki,wataqila ameenatu ta sallama ne" Wata zuciyar ta gaya mata,don haka ta dake tana dubansu sanda suke yowa kanta yuuu. "Ranki ya dade......samun tabbaci da neman sahihancin rahotanni yasa mukazo gareki.....da gaske kece mahaifiyar muhammad fu'ad jadda?.....mamallakin kamfanin jadda diamond chores resources?" . Wani murmushin alfahari ya kubce mata,murmushin da ya dusashe duk wani bacin rai da tashin hankalin data tsinci kanta yanzu yanzu a cikinsa. "Qwarai da gaske.....nice" "Ma sha Allah......kina tare da laila d'iyar qawarki kenan?". Da farko tambayar ta mata banbarakwai,amma zuciya batan basira da neman suna suka gina mata tunanin wataqila