← Book details Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 166 OF 215

Sashe 166

Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

son qamshi ce ,na muku tallan turarukan matar nan TASTED AND TRUSTED ne,duk irin turaren da kike siya ina baki shawara ki gwada nata,yayi yayi yayi,zaki kuma bawa wani labari,muddin kina da dama amma baki siya ba ina me tabbatar miki kin loser ,confirmed ,ba kuma bala'in tsada gareta ba.....sai sirrin sanin kan turaren,nima dai 'yar gidan malam shehu ce bare ace na manya muke using ahto ,ki gwada hajjaju zaki godemin,don tabbas idan me tsoron Allah ce ke kikayi kabbasarta kika saka humra ko lab lab dinta ba zaki iya fita unguwa ba saboda fitinannen qamshi suke bayarwa,ki gwada ki godemin +234 803 211 9803). "Saboda kai ne muffin......saboda kai ne". Idonsa ya lumshe yana sake zuqar qamshin,har cikin zuciyarsa yake sauka,wani nutsuwa qamshin yake bashi,kamar wadda aka tsoma a bahon turare. "Kiyimin rai please sabrrr" Ya fadi yana sake cusa kanta tsakanin dukiyar fulaninta. "Name?" Ta tambaya tana murmushi. "Don Allah kada ki bari wani yaji wannan qamshin idan bani ba". Ya qarasa maganar yana dago kansa gami da sanya idanunsa cikin nata don ta gane har ranshi,da gaske kuma yake maganar. Tafukan hannayenta dasu kansu qamshin suke ta saka tana dago kansa sosai. Zuwa yanzun tuni ta fara fahimtar yanayinsa....da yayi magana ko baiyi ba....idan yayin daga ina ta fito?. "Muffin.....kana tunanin zanbar wani hanci ko wani d'a namijin daban bakai ba ya samu wannan nutsatsen qamshin?.....har abada idan kace bakaso ko farfajiyar gidan nan qamshin nan ya fita bazai fita ba......a yanzun hatta da rai ka bani DUNIYATA......Ka bani rai tunda ka kusanto da makusantana kusa dani......dame ne zan saka maka ni ameenatu?" Ta qarashe maganar zuciyarta tana karyewa da wani irin rauni. Idanunshi cikin nata ya dora hannunsa saman mararta. "Kin gama sakamin ameenatu.....kin gama sakamin sabreena.....kin gamamin sakayya duniyata da kika bani iri.....yara uku fa?,lokaci guda?,a qaramin lokaci har haka?,kika cikamin muradin zuciyata?......abu daya ne ya rage kiyimin,karki guje ni tsanani ko dadi.....karki bari tarbiyyar yarana ta zama abun Allah wadai......ki soni irin son da ba wanda zaki bawa katankwacinsa.....that's all" Ya fada yana dage hannuwansa sama. Hannunta ta saka daga qeyarsa sannan ta hade goshinsu guri daya suna musayar numfashi. "Ka samu muffin.....ka gama samunsu.....amma zan qara da addu'a ga Abba......mutumin da yayi sanadin haifamin irin wannan mijin.....ubangiji ya jiqa kabarinsa ya kuma lullube kabarin nasa da dukkanin wani nau'i na rahamarsa" "Allahumma ameen" Ya fadi muryarsa qasan maqoshi yana sake jin ta masa kima sosai. "Abinci ko wanka?" Ta tambayeshi ba tare data dauke goshinta a nasa ba still kuma tana zaune saman cinyarsa. "Cin abinci sannan kazo kayi wanka yana raunana jiki my world" Idanu ta fitar tana dubansa bayan ta janye fuskarta. "Muffin.......da gaske komai naka dabanne,tsarukanka dabanne kaman yadda naji ana gulmarka......kasan duk wani abu da zai kiyaye lafiyarka" "Wait" Yace yana hade ransa da wasa. "Wake gulmata?,farouq ko?" Dariya sosai ta kubce mata har tana sake riqeshi don kada ta fadi. "Komai farouq?,komai farouq?.....BB ya kusa hutawa dai,nasan fannarshi zata siya masa 'yanci". Murmushi shima yayi yana kama hannunta suka miqe,shi kansa baisan ya wannan ranar zata kasance ba.....kowa ma ya shiga uku. Tsaf ya janyeta suka shiga wanka kaman yadda rules dinshi yake,har ya fara zame mata jiki,ya gaya mata sunna ce kuma bazai gaji da rayata ba,don duk wanda yayi koyi da wani abu cikin abinda manzan Allah yakeyi da zummar koyin yake dashi,to tabbas yana da ladan koyi dashi. Cikin wasu sauqaqan couples pyjamas suka shirya dukkanin farare da adon black wuya da hannu da qafan wandon da bai qarasa idon sahu ba. Kamar wasu ma'auratan daga wata qasar,suka sauka qasa tare. Bayan kammala cin abincin basu kwanta ba,dukka maganganu ne da shirye shiryen biki yaketa fama. Itadai tana gefe tana kallon zallar aikin zumunci irin ma fu'ad din,ta sake tabbatarwa bawai a banza Allah yaa sanya wannan dukiyar a hannunsa ba(Tabbas idan har Allah ya baka wadata fiye da sauran abokai ko 'yan uwanka,to ya baka ne don ka taimakesu,wala'alla duka harda arziqinsu ya saka a hannunsu don ka zama.silar ciresu daga matsi ko matsala,Allah yana sonka da yayi maka wannan baiwar,don zaka samu lada sanda kake basu ita ta hanyar data dace,don ka zama kamar wakilin Allah a bayan qasa,idan kuwa ka riqe ka hanasu yana kallonka.....tabbas! Kuma sai yayi hukunci akai, 'yan uwa dukiyarka kenan fa.....inaga wanda zai danne haqqin wani?,ina ga wanda zai cinye dukiya ko gumin wani?,Allah yasa mu dace,ya rabamu da taba abinda ba namu ba ya hayyu ya qayyumu). Ganin ta langabe masa zata yi bacci ya katse maganan da yakeyi da kowa ya dubeta. "Gate up ameenatu.....naga list na amna.....ke banga naki ba" Ido ta zaro,cikin muryar soma jin bacci tace "Muffin.......nawa name?" "Naki lefan.....naki lefen sabrrrr" Ya fada yana kama hannunta. "Banda wanda akayimin hamma?" Ta tambaya tana dan dariya saboda ta dauka zolaya ne. Kai ya girgiza. "A yanzun ke din cikakkiyar zabin MUHAMMAD FU'AD JADDA ce,sabon lefe sabon sadaki daga hannun jadda" Ya fada yana zame hannunsa a nata. Qasa ya saka hannunsa ya fiddo wata kyakkyawar leda ya zube kayan ciki. Kyawawan akwatuna ne har guda shida masu daukan hankali,iya akwatun kawai abun kallo ne,ba zaka gane kuma kallo ya koma sama ba sai daya bude abun ciki. Wasu irin sabbin designs ne na gold masu matuqar daukan hankali. Uku gold ne uku kuma diamond,wanda ta gane haka ne ta qaramar takardar dake maqale a ciki. Uku ya ware a ciki ya tura gabanta,ya bude wani jaka qarama dake gefan system dinsa ya ciro sabbin rafas na dubu d'aya d'aya na dollars a miqe kar dasu ya dora a sama. "Wannan shine sabon sadakin ameenatu muhammad jadda.....idan tana buqatar sama da haka tayi magana......wannan kuma" Sai ya tura sauran boxes din "Wannan kuma ladan rainon cikin da za'a yimin....duk da nasan ban isa na biyasu ba.....duk boxes daya a madadin yaro daya yake.....shima idan baiyi ba kiyi naming price dinki". Kaf jinin jikinta taji ya daskare na wucin gadi,uwar dukiyar daya zube mata kawai take.kallo tana jin zuciyarta tana raurawa,sarqoqi shida masu qololuwar darajar da batasan ya zata kimanta kudinsu ba?,ga tsabar kudi daya kusa naira million dari da sittin?. Tsoro ne kawai taji yana shirin kamata,tsoron ta yaya diyar ahmadu kamarta zata mallaki dukiya dare daya irin wannan?. Tana shirin zamewa tayi kneeling a gabansa ya dagota. "Kul karkimin godiya....karki qorafi,kinfi qarfin komai da zan baki,don kema kin bani abinda ban isa ni kadai na bawa kaina ba......kin soni da zuciya daya,kin tsallake duk wani gwaji da nayi miki da zummar gano dukiyar kikeso ko bata gabanki,a yanzu ba abinda bazan iya sadaukar miki ba...bare wannan da ba komai bane cikin abinda Allah ya mallakamin ba.....so komai na dauka na baki kin cancanceshi ne,addu'arki da soyayyarki kadai su nafi buqata a halin yanzu a rayuwata,Allah ya yimin komai". Qasa tayi da kanta tana jin hawaye yana sauka a idanunta,sai ya buge da tsokanarta har sai daya rakata daki,ya tabbatar ta kwanta ya lullubeta da duvet ya tofeta da addu'a. Sai daya tabbatar bacci ya soma cin qarfinta sannan ya dawo falon ya zauna yaci gaba da aikinsa.
Chapter 166 · 0% Book details