Sashe 111
Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai kawo ta dinga yi cikin dakin nata tana tattare kowanne tashin hankali da take ganin zata sauke masa har zuwa sanda zata tursasashi guntule igiyar jarababben auren data hada. Bata taba dana sanin aikata wani abu ba irin hada aurensa da sabreen......tabbas yarinyar tana neman zame mata qadangaren bakin tulu......itace cikakken ma'anar karin maganar nan da ake cewa DAN HAKKIN DAKA RAINA SHIKE TSONE MAKA IDANU. Inda qannenta suna hannunta kawo yanzu tayi imani da yaqinin da batasan ma wanne hukunci zata sakasu su karba ba a madadin 'yar uwarsu ba. Minti daya zuwa goma sha biyar ta lissafa amma bataji shigowarsa ba,wannan ya sakata daukan wayarta ta kira musaddiq. Ba'a daga ba amma taji an turo qofar dakin nata an shigo. Koda ta waiwaya musaddiq dinne,ajiye wayar tayi tana dubansa. "Ina yayan naka?". "Na shiga daki kafin ya kammala,ina fitowa na tarar sun fita shi da BB farouq". Wani irin kallo ta watsa masa cikin fushi tana qanqance idanu. "Kasan me kayi musaddiq?!,kasan muhimmancin wannan kiran kuwa?....har yakai na baka saqo ka kasa zama ka jirayeshi ka isar masa?,kana hauka ne musaddiq!" Ta fada da wani yanayi daya bashi mamaki me kama da zata kai masa duka. A mamakance ya shanye mamakin yana yin qasa da kansa kafin yasake dubanta. "Kiyi haquri,idan ya dawo saina sanar masa,ko ina sukaje nasan ba nisa sukayi ba". " Baka da hankali.....bani da wannan lokacin,bani da Lokacin bata lokaci......wuce ka kiramin sabreen" Ta sake fada cikin daga murya tana nuna masa qofa. Mamaki ya sake kamashi ganin yadda ta birkice,yaga dai koma meye duk inda sukaje a gidan zasu dawo su kwana.....amma duka me ya kawo wannan yanayin mara dadi?. Yankewa kansa wahalar tunanin yayi ya juya a salube yana fita a dakin. Tana zaune daga gefan gadon tana duba hotunan da amna tace ta dauka a wayarta sanda saqon ya isketa. Ta daga kai tana duban musaddiq a mamakance. "Taje inji maamah" Ta sake maimaita saqon tana zubewa musaddiq dubanta. Tana juya dalilin kiranne da kuma abinda zai iya biyo baya a kiran. Bawai tana tsoron zuwa bane.....babu shakkarta ko dis cikin ranta.....bata wani tsoro ko shayin fuskantarta......kawai tana duba girman musaddiq ne da tabbas zata ce masa yaje yace mata bata zuwa. "Gani nan zuwa" Ta amsa masa tana aje wayar a gefanta sannan ta miqe tana zura qaramin Malaysian hijab dinta ta taka a hankali tana dosar qofar fita a dakin. Zuciyarta fal saqe saqe,cikin jikinta takejin koma meye ya sanya ta kira BA ALKHAIRI BANE.....koma meye kuma ta shirya fuskantarta. Tana tsaye ta zubawa qofar idanu tana dakon shigowarta,tana jin kaman tayi nawar isowar.....a haka ta murza qofar ta shigo kai tsaye ba tare data maida qofar ta kulle ba. Kallon kallo suka yiwa junansu me wani irin zurfi kafin maamah ta soma magana. "Bakisan adadin kuskure da wasan da kikayi da rayuwarki ba sabreen......bakisan gona da adadin iyakokin da kika sanya qafa kika tattaka ba......amma koma meye a yau zan yanke wannan alaqar da kike taqama dashi......yau dinnan.....kuma a nan wajen zan tabbatar miki da tsinkewar igiyoyin aurenki". Manyan idanunta ta maida ta lumshesu a nutse sannan ta budesu. "In har don wannan ne ni banga dalilin kirana da kikayi ba......wani abune da ke daya ya shafa maamah.....don Allah saboda daraja da mutuncin musaddiq da nake gani na roqeki kibarni na huta..... Allow me to rest.......tsakanina dake ba kare bin damo. Contract ne nace bazanyi ba dama ba tun yau ba,yana da wahalar gaske na yiwa rayuwata hukunci ayi challenge dina a sakani warwareshi......na bar miki contact dinki......na karbi rayuwar qannena kuma akwai abinda yayi saura?" Ta qarasa maganar tana zube mata idanunta wadanda suka fara tunasar da maamah wace ainihin sabreeen din......ta fara juyewa kuma zuwa tsohuwar sabreeen da ake dab da jana'izar halayenta. Wani irin mamaki maganganunta suka bawa maamah din,ranta ya sake dugunzuma. "Kina tunanin kinci bulus?,rayuwar yarona zaki gwadawa bariki?,a gaban idanuna zaki gwada aiki a kansa?" "Wanne yaron naki?" Ta fada cikin calmness. "Indai wannan ruhin dakike burin mallaka ne kike tunanin nayi wani abu a kai to ki hutar da kanki......banason wata hayaniya akan hakan don bani da sauran buqatarsa a rayuwata". "Yanzu kuwa zan tsinke duk wasu igiyoyi da suke tsakaninku" Ta fada a zafafe tana sungumar wayarta. Tana jin ya mata tsaho ta jirayi dawowarsa......ya mata tsaho har sai sanda ya dawo gidan ta gwada mata koda magani ko babu akwai sauran power na uwa da zata iya sakashi ya mata dukkan abinda tayi niyya. Mamakin maamah din ya sake cika sabreeen din. Tanaso ta gogewa matar haddar kanta tsaf.......tanaso ta gwada mata wani abu kansa amma inda akaci sa'a har yanzun da take tsaye bata jin jituwar halayensu shi da ita.....tabbas don a tsukin kafin ta hada karonta tabar rayuwarsu saita aje mata zazzafan darasi. Mummunan faduwa gabansa yayi sanda kiran ya shigo wayarsa,abinda zai iya cewa ya manta rabon da ya jishi. "Ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagis......aslih li sha'ani kullahu fala takilni ila nafsi darfata ainin" Ya motsa bakinsa a nutse ya karantata kafin ya daga wayar ya hadata da earpiece din da ya jawo ya saka a kunnensa,don ba kasafai yake magana da ita a hands free ba. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 _Zafafabiyar_ 97 _An rawaito daga manzan Allah S A W yana cewa"babu wanda zai shiga aljanna alhali akwai qwayar zarra na haqqin dan'uwansa a kansa_ _Bukhari da muslim_ "Muhammadu kana jina?" Tayi lafazin da wani irin kaushi. "Ina jinki maamah" "Indai ni uwarka ce dana haifeka.....na shayar dakai nono na har ka zama mutum.....ina umartarka a duk inda kake ka dawo gida yanzu yanzu......a sanda kake shigowar kuwa ina buqatar shaidar sakin matarka sabreeen......ma'ana ka datse dukka igiyoyin aurenka dake wuyanta.....muddin baka dawo ka aikata hakan ba daga yau ka dauka sunanka tsina......". Da wani azama ya latse kiran don bazai iya saurara ba. Sauti mafi muni da zai iya cewa kunnuwansa sun sake saurara kenan bayan tsahon shekaru.....sauti na biyi da ya kusa sanyashi kaman zai zare bayan sautin ALLAH YAYI MASA RASUWA ME BABBAN SUNA.....KUYI HAQURI...a ranar da ake gaya masa rasuwar mahaifinsa. Subuce masa steering motar yayi abinda ya ankarar da farouq kenan,ya sanya hannu da wani irin zafin nama ya kamoshi yana furta. "Subhanallah" Da wani irin qarfi. Karbar steering yayi yana qoqarin maida hankalinsa jikinsa amma sai yaji hakan ya gagareshi,wannan ya sakashi gangarawa gefan titi ya tsaida motar yana fita daga ciki. Numfashi yake ja sosai zuwa hunhunsa yana jin iskar da yake shaqa ta masa kadan,ko tambaya daya ya kasa amsawa farouq dake gefansa,sai daga baya ya fusgi kalmar "Mu koma gida farouq.....now" Bai musa ba ya bude masa murfin motar,ya taka da wani irin yanayi yana shiga,shima ya shiga mazaunin driver ya kunna motar yana juya kanta zuwa hanyar da suka baro. Ga mamakinta sanda ta sauke wayar a fusace saita samu idanun sabreeen a kanta da wani irin nutsuwa tana dubanta. "In don wannan abunne.....ai da basai kin tasoni ba,zaki iya aiwatarwa koda bana wajen" Ta fada tana zama saman stool din dakin tana kallonta. "Sabreeen tana zaman zamanta aka gayyatota kan abinda bai cikin tsarinta......sabreeen tace bataso.....ba zatayi ba akayi amfani da rayuka uku masu matuqar muhimmanci fiye da nata ruhin aka sakata yin abinda bata taba yiwa wani ba......ta yaya a yanzun saboda ita din ba kowan kowa bace za'a cisgeta daga inda aka dasata?" Kai ta girgiza. "Yadda aka gayyatoni ba shiri......bazan fita a sanda ban shirya ba,saboda gaba a guji taba rayuka irin na ameenatu din.....da kin kwantar da hankalinki ma zan fita.....amma fa a sanda nayi niyya,a sanda koshi wanda kika hada alaqarmu dashi din bai shirya ba......amma tunda kin zabi na fita a sanda kikeso kaman yadda kika shigo dani a sanda kikeso......inajin ya kamata shi wanda akayi komai dominshi yasan yadda aka qulla abun aka kuma warwareshi.....don nagaya yanamin wani gani gani yana kuma kallona a matsayin makwadaiciyar dukiyarsa......bayan kuma ata nan gefansa akwai uwarmu gaba daya" Tayi maganar fuskarta da murmushi kaman me fadin wasu kalmomi masu dadi. Abinda kenan yake sake qule maamah......yadda qaramar alhakin ke zama tana yaba mata zance duk yadda taga dama. Iya wannan kadai ya isheta hujjar qwace suna da license na zama surukarta. Suruka take nema irin wadda zata juyata kaman d'iyar data haifa,wadda zata bita kaman yadda raqumi yake biyar akalarsa ba saba hanya. "Kina tunanin ke dinnan qaramar alhaki kina da wani hujja dalilo ko qwarin gwiwar fadan magana akaina d'ana ya yarda?". "Aah" Ta fada idonta akan wayarta tana dannawa wadda ke sake tsokane idanun maamah. "Ni bance dole ya yarda ba....amma dai qila wannan zai taimaka" Ta qarasa maganar tana kunna wani sauti wanda sai data waiwayo dashi maamah ta fahimci video ne. Tayi matuqar kaduwa,ta kuma yi mummunar razana da yadda ta gansu tarwai ita da Hajj harira......rana ta farko da suka fara takawa gidansu dakinsu suna gabatar mata da contract din aurenta da fu'ad. Komai ya fita kaman yanzu ake dauka,da sautin muryarsu da komai. Boyayyen murmushi ta saki ganin yadda abun ya daki.maamah da wani.irin razanannen yanayi. Boyayyar CCTV camera din data saka a parlor din kenan ba tare da sanin kowa ba. Zama da JIB ya qareta abubuwa da yawa,tun sanda tayi noticing canzawar huda awancan lokacin da Naseer yaso bata ta,ta yanke ta sakata,wanda ita ta taimaka mata taga duk wani motsi na huda.....ya kuma sake qarfafa mata zargin da shi yayi sila ta gano komai. "Wannan kawai zan nuna masa don yasan cewa bani na kawo kaina rayuwarsa.......ba sonshi nake ba.......ban taba kuma sonsa ba.....banajin kuma zan soshi din.......rabuwa da zaiyi dani kaman ragemin aiki yayi......" Maganarta ta tsaya a nan sanda lallausan qamshinsa ya marabci hancinta.....kaman giftawar walqiya kuma sai gashi a wanze cikin dakin a wani birkitaccen yanayi. Wani irin kallo da yake saukar mata shi ya sanyata zare idanunta daga kanshi. Wani irin birkitaccen kallo yake mata zuciyarsa na wani mahaukacin bugawa da kalamanta na qarshe da kunnuwansa sukayi katarin ji "Ba sonshi nake ba......ban taba kuma sonsa ba,bana jin kuma zan soshi din......rabuwa da zaiyi dani kaman ragemin aiki yayi......". Inda tasan girma da nauyin da kalaman sukayiwa qirjinsa tabbas ba zata fadesu ba. Janye nasa idanun shima