← Book details Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 153 OF 215

Sashe 153

Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_* *_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_* *_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_* *_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_* *_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_* *_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_* *_HAIHUWA KIKAYI?_* *_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_* *_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_* _Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_ 08104553105 08127084190 *_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_* *_BGAWO'S KITCHEN_* *MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU* "Ex ambassador khaleed mustapha" Kalma ta farko da fu'ad ya fara fada bayan ya daga wayar. "Ranka ya dade sir......tuba muke.....tuba muke,ayimana afuwa,ayi mana rai" Ambassador khaleed ya fada cikin matuqar qanqantar da kai da kalmasa harshe. "Wani abu ya faru kenan" Fu'ad ya fada cikin halin ko in kula,abinda ya sake daga hankalin ambassador kenan. Yafi kowa sanin illar wannan shariyar tasa,har gwara ya fito maka a mutum,yayi maka duk yadda yakeso,yayi maka kalar hukuncin da yaga dama. "Ranka ya dade sir.....ina me baka afuwa......ina me baka haquri......don Allah.....don Allah a dubeni,ayimin rangwame". Gyara zamansa yayi tare da yiwa sabreen inkiyar ta matso taci abincin. Kai ta langabe masa,sai ya matsa da kansa ya soma diban abincin ya miqa mata yana tambayar ambassador. "Hala bakasan abinda yarinyarka take aitawa ba.....bama a kaina kadai ba,har kan mutanen da take taqamar matsayinka da matakin da kake kai sun tsaya mata sun kuma siya mata ticket na cin mutunci da qasqanci ga kowa?". Ya masa tambayar sanda sabreen ta saka hannu ta karbe spoon din ta maidashi bakinsa,ya bude bakin ta saka masa abincin sannan ya mata sign na itace next da zataci. Shuru ambassador yayi,yana juya irin amsar da zai bawa muhammad jadda. Yasan wayeshi farin sani ma tass kuwa.......yi masa qarya tamkar tafka wani babban kuskuren ne,hakanan gaya masa gaskiya kuma bazai taba zama mafita ba. "Ko ka sani ko baka sani ba wannan kai zaka bawa kanka amsa......". "Am really sorry sir......ayimin afuwa.......na yarda da kowanne hukunci ya kamata kayi mata koka dauka a kanta,na aminta da hakan ranka ya dade sir". Fareeda dake durqushe waje daya ta daga kanta da sauri,a mamakance tana duban mahaifinta. Shi da kansa yake sallamawa me jadda ita?,shi da kansa yake miqata izuwa gareshi kan yayi duk kalar hukuncin da yaga dama?. Ci gaba yayi da cin abincinsa yana kuma morewa kallon duniyarsa. Kaman bazaice komai ba....kaman bazai amsa ko ya sake magana ba......har ambassador ya fara sarewa gami da fidda rai kafin yace. "Zabin dawowar dukiyarka qwaya daya ne tak........tsaffin kudaden qasar nan da ka danqaresu a France.......zamuyi yarjejeniyar dawo dasu gida kuma qasata Nigeria don amfanin al'ummar qasar". Wani razani ya sake kama ambassador,wanne irin mutum ne fu'ad din?,kamar wani maye me gani har hanji?,kudade ne masu ciwo nauyi da yawa da yayi imanin koda iya su kadai iyalinsa suka tsira sun rabauta,amma har ya akayi ya ankara dasu?. "Ina fata kana saurarena?" Fu'ad ya tambayeshi yana cirar tissue yana goge bakinsa don abincin ya isheshi haka. Sai daya goge gumin fuskarsa da habar rigarsa sannan yace. "Ina jinka......na fahimta" "Good......secondly diyarka......rashin kyautata tarbiyyarta wannan matsalarka ce.....damuwarka ce.....haduwarka da Allah kadai ya isheka barazana.......tayi attempting kasheni......inaso ta gaggauta fita da kanta media television da magazines ta tabbatarwa duniya da tayi yunqurin aikata hakan,tayi apologize nawa......tayi na matata.....ta tabbatarwa da duniya cikakken mutunci da darajar da iyalina ke dashi.......wannan muqulli ne kawai na budewar daskararru da kuma qwatattun dukiyoyinka......hukuncin yunqurin kisan kai kuma ita da hukuma.....sunsan matakin da yafi kamata su yanke a kanta". Ba fareeda kadai ba.....hatta da sabreen hukuncin ya mata nauyi,tayi zaton iya hakan da zatayi ya wanke duk sauran laifukanta... "Amma sir.......na dauka duka hakan zai wakilci kowanne laif......" "Khaleed!" Fu'ad ya kirashi a tsawace cikin fushin da har sabreen dake zaune a wajen sai data daga kai tana kallonsa,tana kallon yadda kamanninsa ke sauyawa alamun bacin rai ya fara tasiri a zuciyarsa. "Magana ake ta kisan kai bisa ganganci da niyya......magana ake ta bata mutunci da daukan hayar gidajen jaridu suyi batanci ga iyalina......kasan nawa ta kashe don kawai a buga sunan matata ta sunna da sunan KARUWA?,waye yake bata kudin?,a ina take samosu?,a gaban waye take dukka kalan rayuwar da taga dama?......wannan hukuncina ne ba wai shawara bace ko alfarma.....kana da right na cewa ba zatayi ba gaba daya......wannan ya rage naku.....dont contact me again indai akan wannan issue dinne.....i finalized the matter" "Please sir......please....." "Khaleed,Not my problem to solve......Could you please stop calling me?". Shuru ambassador yayi,ya tabbatar ba wani abu da zai sanya fu'ad canza wannan hukuncin nasa,abinda ya bawa fu'ad daman yanke kiran yana jan wani dogon tsaki kaman zai tsinke harshensa. A tausashe ta karbe wayar,ta sakata a DND mode ta ajeta gefe. Kamo lallausan tafin hannunsa tayi ta saka cikin nata tana lalubar qwayar idanunsa,cikin nasara ta samosu,saita kafeshi da idanunta tana kallonsa tana kuma murza tafin hannun nasa. Cikin minti biyar ya sauke wata nannauyan ajiyan zuciya,abinda ke tabbatar mata ya samu relief na bacin ransa. Hannunta ta dora saman cikinta tana nake fuska a shagwabe. "Suna tsorata sosai idan abbee dinsu yana cikin irin wannan fushin......sunce na bashi haquri,na gaya masa komai me wucewa ne,komai watarana zai zama sai labari". Murmushi ya subuce masa yana lumshe idanunsa,ya saka hannunsa ya dagota,ya dorata saman cinyarsa,tura hannunsa yayi saman cikinta a nutse ya aza tafin hannunsa akai. "Dukiya jarrabawa ce me zaman kanta....kaman yadda talauci take shima jarrabawa ne,duk wanda Allah ya jarrabi bawa dashi akwai nasa kalan qalubalen.....ki fadi musu daddynsu yana nan yana fighting akan yadda zasu rayu cikin aminci ba tare da sauran qaya ba akan hanyarsu.....i love them more than i love myself....." "I hope I'm still your number one?" Ta fadi a narke tana kyabe baki. Dole ta sanya wani murmushi me sauti ya subuce masa,ya kama kumatunta yadan riqe yana girgizawa. "You're filled with jealousy......madam.....ke din DUNIYATA ce fa gaba daya". Murmushi tayi yana boye fuskarta a kafadarsa. " Kiraminsu Musaddiq" Ya fada yana komawa normal mode dinsa. Zamewa tayi a jikinsa a hankali ta miqe,ta taka tana fita zuwa parlor din. Dukkansu suna zaune,kowa kusan wayace a hannunsa yana dannawa. Farooq kuma ya koma amsa waya. Rusunawa sukayi suka gaidata cikin girmamawa,ta amsa musu da danjin kunya da nauyi sannan tace musu. "Hamma yana kiranku" Miqewa sukayi suna wucewa ciki,banda farouq daya daga musu hannu alamun yana zuwa. So samu su shiga ciki duka ta zauna ita a nan,don wala'alla wata magana zasuyi data shafesu,to amma farouq yana nan,ita kuma yanzu kunyarsa takeji,dole ta juya ta koma dakin. Yana zaune still saman kujerar,ya miqe qafafunsa hannunsa da cup din ruwa yana sha. Gaidashi sukayi shima cikin girmamawa kaman yadda suka saba,ya jiye glass cup din yana amsa musu. "Anni bata shigo ba?" Ya tambaya yana dubansu. "Eh sai zuwa anjima kadan,abba ne yadan tashi da ciwon kai". "Subhanallah,amma ba wanda ya gayamin a cikinku?" Ya fada cikin dan nuna bacin rai. Idanu kawai suka hada kowa ya sadda kansa,kota yaya zasu gaya masa bayan ko ganinsa basu samu yi ba. waya ya dauka ya kira abban,suka gaisa yaji jikin bawai tsanani ko yawa yayi ba,yace suyi xamansu yau su huta,tunda komai yana tafiya lafiya alhamdulillah,sannan sukayi sallama ya aje wayar yana dubansu. "A cikinku akwai wanda yayi magana da wani cikin abokai ko 'yan uwa sanda zamu baro madeena mu sauka a nigeria?". Daga kai sukayi suna dubansa,don tambayar tashi ta musu wani iri. Kai ya jinjina musu. " Eh ina nufin ko a hira ba wanda ya bawa wani full details na ranan dawowarmu da inda zamu sauka?" "Full details?" Musaddiq ya tambaya yana kallon hamman nasa. Kai fu'ad ya jinjina yana maida hankalinsa a kansa. "Eh" Fu'ad ya jaddada masa. "Akwai hamma" Musaddiq ya fada abinda ya faru a wancan ranar yana dawo masa. Ido fu'ad ya lumshe sannan ya budesu. "Waye?" Ya tambayeshi kai tsaye. "Maamah ta bani wani number na tura mata details din.....ban kawo komai a raina ba hamma......ban kuma yi tunanin akwai wata matsala da hakan zai haifar mana ba" Ido sosai ya zubawa musaddiq din,yana jin kanshi ya masa nauyi da ambatar sunan maamah a lamarin. Tsoro ya kama sha da fargabar kada sunanta ya fito cikin jerin sahun sunayen mutanen da suke da hannu a faruwar al'amarin fa. "Me yasa zakayi haka musaddiq?......me yasa baka kiyaye wasu abubuwa?,kana tunanin ni dakai saddiq farouq amna dama duk wanda yake under jadda family ordinary human ne?" . Shuru yayi jikinsa yana yin sanyi. Tun sanda abun ya faru wannan abun yake a ranshi,jiki da zuciyarsa duka suna gaya masa akwai alaqa tsakanin abun da kuma wancan address din daya bada,wannan ya sanyashi tilastawa kansa zama tuno digits din daya turawa address din,ya kuma sake zaunar dasu tsaf cikin kansa. "Baka riqe name din dake jikin contact din ba....koda bincike ne ta yaya kake tunanin za'a iya yinsa?" Fu'ad dake kallonsa da takaici ya fada. "Na riqe digits din...." Shuru ya danyi yana ci gaba da kallonsa "Really?" Kai ya jinjina masa,sai ya waiwaya ga saddiq. "Ya baka digits din ka turawa saleem.....kace masa injini" Ya fada yana maida bayansa jikin kujera yayi relaxing. Wani irin bacin rai ne yake ratsashi,maamah itace silar faruwar wannan abun?,to hadin baki sukayi da fareeda kenan wajen kasheshi ko goyon baya ta bata?,hakan yana da alaqa da hallarar kowa a asibitin da nuna zallar damuwarsa a kansa amma banda ita?. Kanshi ya samu da girgizawa,yana jin cewa sam maamah din ba zata aikata haka ba. "Amma ta taimaka wajen kauda abbanku daga duniya?" Tambayar da tazo daga qasan zuciyarsa kenan,ta kuma sake taso masa da wani irin bacin rai. A hautsine take duban mahaifin nata bayan ya gama gaya mata hanyar mabudin arziqinsa da yake hannunta,bisa tsari da kuma dokar da fu'ad ya bayar. "Yanaso yayi humiliating dina ne abba......ta yaya zan fita gaban 'yan jarida na tonawa kaina da kaina asiri?....hakan kuma ba yana nufin na wanke kaina da kaina bane?,tamkar kenan na bawa shari'a daman yankemin hukunci da daukan mataki a kaina ta sassauqar hanya?" Ta fada
Chapter 153 · 0% Book details