← Book details Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 168 OF 215

Sashe 168

Duniyata Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Randa FU'AD ya sauka ranar fanna tayi bridal dinta,baije ba farouq ma bai matsa ba tunda yasan bame son zuwan bane. A rana ta biyu ne akayi zaman ajo,wanda a wannan zaman kudi sukayi rana.....dukiya tayi kuka da idanunta,ya nunawa BB dinsa qauna irin wadda ta sanya farouq tara hawaye sosai a Idanunshi.
"Karka yadda kayi mana kuka gaban mata da tarin mutane,idan kayi hakan bamu yafe maka ba.....wannan kukan ka riqeshi sai sanda kuka kebe......idan ba haka ba za'a dauka lusari ta aura" Ya fada kadan a kunnen farouq bayan ya gama zazzage pound cikin abinda aka ajiye saboda zuba ajo din,don yana gama zubawa aka dauke abun,ya riga ya cika sai wani aka sanya.
Tofa......nan idanu dama hankulan 'yammata dama zaurawa masu lokaci yayo kan FU'AD din,taron mayu bawai na maita ba......mayun mata.....ma'abota son kyakkyawan namiji me abun hannunsa hankulansu ya tashi. Kowacce isassace me aji tana jin takai,don me qaramin class ma baya suka dinga ja suna rufawa kansu asiri,saboda sunsan kalar zaren ba kalar yadin bane......saidai su kansu isassun sai rab'e rab'e,an rasa zaqaqura me qarfin halin tunkarar me jadda din.....kwarjini yanata aikinsa.
Mota ya koma yayi zamanshi suns hira da duniyarsa,video call kaman ko yaushe,ta daga masa hannuwanta da sukasha wani irin jan lalle,tun daga tafin hannun har zuwa bayan hannun nata.
"Ya salam" Ya fada yana jin wani abu ya harba a jikinsa.
"Nawa me qunshin nan takeso a bata?".
"Anni ta biya mana ni dasu amna.....beside ma ai ka ban kudin da zai isheni kalar kowacce hidima".
"No....kudin dana baki ban bakishi bane don kiwa kanki komai ba,na baki shine don ki wata hidimar daban,zan saka miki a dollar account dinki,saiki cire".
"Allah yabarmin kai jadda na.....Allah yajamin da ranka uban 'ya'yana" Ta fada tana jin kanta yana fasuwa,bada komai ba kuma,da zallar kulawa.....da kalar mijin kuma data samu.
Sanda suka koma guest in dinsu farouq shine qarshen shigowa,bai kuma tashi shigowa ba sai daya na dare. A sannan FU'AD yana zaune saman abun sallah yana addu'o'insa,wanda duka ta neman dacewa da alkhairai ce duniya da lahira shida 'yan uwansa dama dukkan wani masoyinsu(harda ku fans na DUNIYATA
Ido suka hada FU'AD ya janye idanunsa yana hade rai.
"Wanne irin abune wannan?,zaka ajiye.mutane kuma ka tafi,baka tashi shigowa ba sai tsakiyan dare kaman wani barawo?" Wani dariya sosai Farooq ya saki yana qoqarin cire babbar rigar jikinsa.
"So sorry dude.....kasan abinka dame iyali kuma farin shiga.....inacan ina lallashinta wai yatsunta sun gaji......ga tafiya kano gobe donma flight ne.....".
" A gidan ubanwa ta zama iyalin naka?" Ya fada adan fusace,don ya kira sabreen yaso suyi hirar dare bai sameta ba.
"Ka rabo mutane da iyalinsu kuma kazo ka ajiyesu?". Ido farouq ya fiddo,yanason fashewa da dariya amma ya danne
"Ikon Allah....to ni me zan muku idan nazo din?,qarqari muyi hira fa?,kuma yanzu tsakani da Allah saboda rashin imani wanda keda sabuwar amarya ai abun a masa uzuri ne ko?.....to kuma ma naga wancan lokacin naka daurin auren.....qasarma ka bari kaqi dawowa ka barni da amaryar da abokan gaba daya.....wannan rashin adalci ne dason kai dude".
"Farouq....gori zaka yimin?....gate out please ka barni naji da damuwana" Wannan karon duk yadda yaso boye dariyar ya kasa,sai kawai ya saki abarsa yana nufar toilet.
"Bani nakar zomon ba.....ratayar ma ba'a bani ba.....iyali me dadi.....ashe haka lamarin yake dama" Ya qarasa fada yana shigewa gami da turo qofar.
Qwafa fuad ya saki,sai kuma murmushi ya qwace masa. To meye ma laifin farouq a ciki?,ita kanta sabreen din bata da laifi tunda tace masa zata aje wayarta dama,kawai dai iya shegensa ne ya motsa,da alama kuma ramuwa yakeson yayi masa.
*_ALQAWARIN ALLAH baya tashi_*
"An daura auren umarul farouq hamza kibiya,da fannah maisharif babaghana......jama'a kun shaida?". Sautin daya sanya fu'ad sakin tattausan murmushi yana furta.
"Alhamdulillah......alhamdulillah"
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
_Zafafabiyar_
140
*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*
*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*
*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*
*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*
*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*
*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*
*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*
*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*
*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*
*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*
*_HAIHUWA KIKAYI?_*
*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*
*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*
_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_
08104553105
08127084190
*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*
*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*
Daga nan inda yake yana hangen sadakin fannah dake bada tabbacin ta zama ta farouq dinsa halak malak......hakanan yana iya hango farouq dake tsakiyar abokansa wanda shigarsa bata da maraba data jikin fu'ad din,sak da sak kaman yadda sukayi a bikin fu'ad din.
Lafiyayyen walima aka gudanar a gidan gwamnatin jihar borno bayan kammala daurin auren da tarin abokansu masu jini a jika,wanda kowannensu wani ne shi ta fannin ilimi da abun duniya.
Ana gamawa fu'ad ya wuce masauki yabar farouq da tarin abokanshi,don shi bazai iyama wannan iya shegen nasu ba,sun sanyashi a gaba sunata abubuwansu daya tabbatar sai yayi trending a social media. Tunda akayi hotuna wajen reception din yayo gaba,don akwai shirin da yakeso yayi.
Ruwa ya fara watsawa ya fidda wayarsa,kai tsaye ya kira duniyarsa. Daidai lokacin tana zaune suna kallon reception da daurin auren da ko awa guda ba'ayi da yinsu ba amma har an warwatsa a media.
Kishin fu'ad ke taso mata sosai saboda ganin tarin comment din yammata a kansa. Shi kadai amma ya fita daban a cikinsu,komai nasa daban yake,wani irin kwarjini me hade da nutsuwa da suka qarawa fuskarsa kyau da kuma kamala.
_"Lallai baaba ma da babansa fa.....duk kyan azurfa bata kai ya gold ba.....the jadda.....guy dinnan daban yake fa
"_ comment din wata daya gilma kenan daya sanya zuciyar sabreen quntata,ta kuma ture screen din daga fuskarta tana jan wani qaramin tsaki,can qasan ranta kuma tana mita.
"Bansan me yake damun 'yammatan yanzu ba,kamar mayunwata suke akan maza.....idan suka saka namiji a gaba baji ba gani?,ba kunya ba aji ba kamun kai?" Daga huda har amna sun fahimci me takewa qunquni,sai suka qunshe dariyarsu saboda zuwa yanzun suma suna jin tasu soyayyar da angwayensu har cikin jininsu.
Kayanta take hadawa dama,saboda tanason wucewa gida ne kafin su qaraso,tanaso ta kimtsa ta tarbeshi da kyau,idan yaso gobe sai ta dawo gidan annin. Kiran wayarsa ya sanya ta ajiye duk abinda takeyi,ta kuma daga kiran tana samun wajen zama.
"A ina kake?" Tambayar data fara masa kenan wadda ta bashi mamaki.
"Na dawo guest house masauki.......me ya faru?" Wata sassanyan ajiyar zuciya ta saki,tana jin dadi daya dawo din,at least ya tsira daga kallace mata shi da wadancan mayunwatan 'yammatan sukeyi.
"People are commenting about you everywhere
You're all over social media muffin" Ta fada da wata irin narkakkiyar shagwaba.
"What?" Ya fadi dariya nason qwace masa.
"Like nine angon?" Ya sake tambayarta.
"Am serous muffin" Ta sake fadi tana narke masa.
"Am all yours......am yours forever my World" Ya fadi da wani irin calmness daya bawa zuciyarta nutsuwa. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta soma gaidashi.
"Ya taron?"
"Alhmdlh.....but babu dadi coz bakya kusa dani".
"Nan da awanni kadan zamu kasance tare in sha Allah" Ta fada tana bashi confidence.
"In sha Allah" Shima ya maimaita. Lafiyan yaranshi shine next abinda ya qara tambaya,tayi murmushi tana dora hannunta saman mararta data fara tasawa tana bashi amsa.
"They're fine.....suna gaida abbunsu.....sunyi missing nasa"
"Me too my world.....akwai kyakkyawar gaisuwa tsakaninmu idan na dawo.....so get ready,be at home as soon as possible"
"Yanzun nake shiri in sha Allah"
"But.....karkice zaki fita da mota daya....ki jira su abdulgafar zasu kaiki har gida.....and nace su qara yawan security na gidan". Ya fada da serious murya.
"I hope komai lafiya ko?" Kai ya jinjina,kawai yana jin wani abu daban a jikinsa.
"Lafiya.....in sha Allah" Ya fada yana son tabbatarwa da kansa haka.
Cikin nuna tsananin kewa da qaunar juna sukayi sallama shida ita,kai tsaye kuma ya kira abdulgafar.
"Zamu qaraso gurin qarfe biyar......get ready please,a qara yawan security a airport da gida na harda gidan anni......har gidan farouq.....if possible inaso kowa cikin ku ya zama ankare da kowanne parts".
"As you wish sir" Ya fada cikin girmamawa.
"Ku rakata gida safely abdulgafar......bazan iya jurewa ba if something happen".
"Bazai faru ba sir in sha Allah"
"Good abdulgafar" Ya fada yana yanke kiran.
Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana dan wani gajeram tunani da shi kansa baisan na meye ba,sake daukan wayarsa yayi ya tura rubutaccen saqo ga duk wani guard da suke tare dashi a halin yanzu haka a maiduguri,sannan ya sauka yana laluben wayar farouq don jin yadda zasu shirya tahowa kano kada lokacin tashinsu ya fita.
Chapter 168 · 0% Book details