Sashe 94
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonshi Hajia tayi tace "Ina fatan dai uwarka ta fad'a muku irin hidimar dake gabanku? Dan kamar yanda na fad'a ne dole za ayi aure irin auren buzuwa."
Hannayenshi ya zuba aljihu yana mamakin yanda ko gaban idon mahaifiyarshi ko bayan idonta ba zata iya cewa mahaifiyarka ko mamanka ba sai dai uwaka, juyawa yayi zai fita yana fad'in "Zanyi komai akan zab'inki ai a shirye nake."
Cikin d'an d'aga murya tace "Kace ubanka ne zai biya sadakin? A wane dalili ne kai ba zaka biya ba?"
Ba tare daya tsaya ba bare ya juyo yace "Saboda shi za'a haifawa jikan."
Ummy ce ta d'aga kai ta bi k'eyar shi da kallo tana jinjina wannan al'amari na d'an nata, kamar ba shine jiya yayi wa yarinya fyad'e a cikin gidan nan ba, kai dole ma su b'oye wannan sirri ita da Hamna, dan ko sun fito dashi shi dai babu ruwa a idonshi bare yaji kunya ko nadama, zai ma iya fassarawa mutane yanda al'amarin ya kasance kad'an ne daga cikin aikinshi, Hajia kuma ko a jikinta sai jawo akwatinan da tayi aka bud'e, sam babu wanda yayi tsammanin da kaya a cikinsu duba da yanda shi kanshi ya d'auko su ya shigo da su, amma abun al'ajabi dukansu guda goma sha hud'u cike suke da kaya masu yawa da kyau, ga kuma goro da kud'i har million biyu rigis, Hajia kam ya birgeta a karon farko na rayuwarta, nan aka manta da jiran amarya ake anata duba kayan nan wasu na d'auka hoto, isowar motocin da suka tafi d'aukar amarya ne yasa Hajia kallon Sa'ada tace "Ki shiga da kayan d'akinki ki ajiye."
"To." Ta fad'a tana mik'ewa ta d'auki kayan tare da taimakon k'awayen ta ita ma da suka zo tausar k'irji.
*Alhamdulillah*
09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_*Alhamdulillah Ala ni'imatil islam, Allah nagode maka daka sawak'e min komai, ba yin kaina bane, ba dubarata bace, ba wayona bane, Allah nagode maka, yan uwa kuma nagode sosai da gudummuwarku, Addu'arku ta riskeni a sanda nake da buk'atar ta, haihuwa ta zo min da sauk'i fiye da zatonku, Allah kaine Allah kuma abun godiya, Allah ka raya min yarana ka bani ikon yi musu tarbiya irin ta addinin musulunci.*_👏
*Aci gaba da gashi guy's.*💃
_27_
Ana cikin wannan hidima aka kawo amarya, motoci dai gasu jingim wanda suka paka k'ofar gidan, amma Zeituna bata da dangin da har zasu iya d'aukar motocin, gaba d'aya wanda suka zo rakiyarta basu fi mata ashirin Ba. Kuma a haka wai dangi sun zo ne k'wansu da k'wark'watarsu saboda ta auri mai kud'i, tarba ta musamman suka samu daga gidan girma, inda aka wuce da amarya d'akin ta aka zaunar da ita, saida suka ci suka sha suka k'oshi kafin suka bar gidan tare da yi wa amarya jan kunne cewa karta manta da danginta wajen cin arzik'in, wasu daga cikin motoci aka saka suka mayar dasu gida suka bar amarya da halinta.
Kafatanin yaran gidan ne suka baibaye Zeituna suna kallo, wacce ita kuma ta sanda kanta k'asa ta kasa had'a ido da kowa saboda tunaninta duk kallon rashin mutumci suke mata, Hamna da Amna da Jamila ne suka shigo tare sai Umaimah dake bayansu, zaune sukayi inda Umaimah ke fad'in "Ku kuma ku tashi ku fita ku ba mutane wuri duk kun zo kun sata gaba kuna kallo."
Nazeefa ce ta kalleta tace "Ai dai ganin amarya muka zo."
Cikin tsawa Umaimah tace "Ke dallah tashi ku fita, ba gidan zata zauna ba sai kiyi ta kallonta ai."
Kamal ne ya kalli Umaimah ya mik'e tsaye yana zuba hannayenshi aljihu yace "Kaji mace dan Allah zaki kore mu, amaryar ubana ce fa."
Kallon juna suka shiga yi dan abun ya basu mamaki, a sanin da suka ma Kamal baya da surutu irin haka, Hamna murmushi suka bishi da kallo har suka fita, sai Jamila da tace "Allah yasa kar mu samu yah Ammar na biyu a gidan nan."
"Ameen." Cewar Amna da saurinta, Umaimah ce ta kalli Zeituna wacce k'irjin ta ke dukan uku uku saboda zatonta zasu mata rashin kunya ne shiyasa suka kori yaran, cewa tayi "Aunty Zeituna ki bud'a fuskar ko, yaran sun fita sai mu kawai."
K'ara sanda kanta tayi taja gyalenta ta sake rufe fuska ruf, Hamna ce tabi hannayenta da kallo wanda suka sha lalle ba laifi mai kyau, amma da ganin gyalenta da kayan jikinta kasan ba shirin k'warai tayi ba ko aka mata, duk da bata yanayin farin ciki hannu tasa ta janyo mayafin tana fad'in "Haba aunty Zeituna mu ga kwalliyar mana, mu fa ba bak'in ki bane."
Kallon juna sukayi yayin da Umaimah har saida tayi dariya saboda ganin kwalliyar dake fuskarta, da sauri ta rufe bakinta tana kallon jagirar da ke fuskar Zeituna wacce ta mik'e zat babu lank'wasa,cike da mamaki Amna tace "Aunty Zeituna, waya miki wannan kwalliyar haka?"
Da sauri Zeituna ta d'ago kai ta kalleta sai kuma ta sauke kanta tana mamakin yanda duk suke kiranta da aunty, Umaimah ce tace "Aunty Zeituna, gaskiya tashi ki sake wanka ki zo ki sake shiri, dan kawuna ba zai so ganinki haka ba a darenku na farko."
Tintsirewa sukayi da dariya sai Hamna kawai data girgiza kai tana murmushi, ganin bata da niyyar tashi yasa Amna mik'ewa ta kamata suka nufi ban d'aki tana fad'in "Mik'e mana auntynmu, wannan kwalliya taki ai ta asalin 'yan k'auye ce aka miki."
Turata tayi ban d'akin tace tayi wanka ta fito dan ta goge wannan kwalliyar marar kan gado, Jamila ce ta mik'e tace ma Hamna "Sis ki duba mata kayan daya dace ta saka yanzu, dan ke ce ke shirin zama gwanar kwalliya da iya tsara kaya."
Hararanta tayi tace "Wai ku ina ruwanku da shirinta? Haka kawai ku mata katsalandan, kunsan tana so ko bata so da zaku mata shishigi? Watak'ila fa haka ta iya kwalliyarta, kenan zamu zauna kullum muna yi mata ne?"
Amna ce tace "Ke dai babu ruwanki kawai ki mata, in kuma ba zaki mata ba ki fad'a ni saina mata."
Hararan Amna tayi tace "Bansan iskanci Amna, ina wasa dake ne? To ba zanyi ba ki mata ke."
Mik'ewa tayi zata bar d'akin Amna ta tab'e baki tace "Kar Allah yasa kiyi d'in kiga idan za'a kasa yi mata ne."
Duk da Hamna taji zafin maganar amma banza ta mata dan bata son hayaniya, saida ta kai k'ofa zata fita Amna ta sake cewa "Dama tun jiya kike bak'in rai kamar wacce aka aikowa sak'on mutuwa."
Juyowa tayi ta kalleta cikin hassala tace "Amna bana son iya shege fa, wallahi karki sake min magana, inba haka ba kuma..."
K'wafa tayi ta sake juyawa zata fita Amna tace "Inba haka ba sai me? Me zakayi?"
Juyowa tayi ta dawo cikin harzuk'a tana fad'in "Dan Allah in kin cika 'yar halak ki sake tanka min, Amna ki min magana kiga yanda zan kifar dake a wurin nan."
*'Yan biyu akwai rigima🤔, ko kuma dai na familyn Gaga ne haka.*
Ba tare da wata shakka ba ta matsa kusa da ita tsabar jin masifa tace "Anyi d'in naga me zaki..."
Marin da Hamna ta sauke mata a kumatu yasa ta yin shiru bata shirya ba, dafe kunci tayi ta d'ago daga sunkuyawar da tayi bata shirya ba, da tsantsar mamaki ta kalleta tace "Hamna ni kika mara?"
"An mareki Amna me zakiyi?" Cewar Hamna a hassale, d'orawa tayi da "Ko zaki rama ne marar kunya?"
Ai kuwa Hamna na gama fad'a Amna ta d'auke ta da mari ita ma kamar wasa, jin zafin marin yasa Hamna idonta kad'awa sukayi ja sosai, takaici ne ya lullub'e ta wai k'anwar ta ce ta mareta a fuska, lallai akwai raini tsakaninsu kuma babba, tana shirin kai mata duka Jamila tayi saurin shiga tsakaninsu ta ture Amna gefe guda tana fad'in "Dan Allah kuyi hak'uri ya isa haka, ku bari."
Umaimah ma tasowa tayi ta rik'e Hamna ta fara bata hak'uri, wannan hayaniyar ce ta fito da Zeituna daga ban d'aki da kuma Ummy da su Zeinabu dake d'akin Ummyn wanda yafi kusa dana Zeituna, suna zuwa suma rabasu suka fara yi suna bawa Hamna hak'uri wacce ta d'auki zafi sosai, tabbas kowa yasan ranta ya b'ace saboda yanda ta rikid'e ta zama kamar Amna idan tayi zuciya, kuka Hamna keyi tana fad'in "Wallahi Ummy saina tozarta yarinyar nan, dan na sakar mata fuska shiyasa har zata iya d'aga hannu ta mareni, Allah saina ci uwarta a gidan nan dan ta gane da banbanci ni da ita."
Ummy ce ke fad'in "Kiyi hak'uri nace ko Hamna ta, ki k'yaleta tunda ke ce babba, muje d'akina ki huta kinji ko."
Cikin wani irin kuka kamar wacce aka wa mutuwa tace "Babu inda zanje, Allah saina tattaka ta Ummy, idan ba haka ba kuma kowa zai shiga matsala a gidan nan."
Murmushi Ummy tayi saboda ita dai tasan yan biyunta basu da k'ohi yanzu, dan haka ta jata tana fad'in "Naji to muje dai."
Tirjewa tayi sosai tace babu inda zata je saidai a barta da Amna, ita ma kuma Amna da su Zeinabu ke rik'e da ita cewa take "Dan Allah Ummy ki saketa ta zo ta kashe ni in zata iya, an fad'a miki tsoronki nake ne."
Ganin abun ya k'i kwantawa yasa Ummy daka tsawa tace "Ke Jamila, tunda ba zasu hak'ura ba ku kira Hajia ta zo ta rabasu, ni kam na gaji da wannan jininin kamar kukan tsohuwa."
Hannayenshi ya zuba aljihu yana mamakin yanda ko gaban idon mahaifiyarshi ko bayan idonta ba zata iya cewa mahaifiyarka ko mamanka ba sai dai uwaka, juyawa yayi zai fita yana fad'in "Zanyi komai akan zab'inki ai a shirye nake."
Cikin d'an d'aga murya tace "Kace ubanka ne zai biya sadakin? A wane dalili ne kai ba zaka biya ba?"
Ba tare daya tsaya ba bare ya juyo yace "Saboda shi za'a haifawa jikan."
Ummy ce ta d'aga kai ta bi k'eyar shi da kallo tana jinjina wannan al'amari na d'an nata, kamar ba shine jiya yayi wa yarinya fyad'e a cikin gidan nan ba, kai dole ma su b'oye wannan sirri ita da Hamna, dan ko sun fito dashi shi dai babu ruwa a idonshi bare yaji kunya ko nadama, zai ma iya fassarawa mutane yanda al'amarin ya kasance kad'an ne daga cikin aikinshi, Hajia kuma ko a jikinta sai jawo akwatinan da tayi aka bud'e, sam babu wanda yayi tsammanin da kaya a cikinsu duba da yanda shi kanshi ya d'auko su ya shigo da su, amma abun al'ajabi dukansu guda goma sha hud'u cike suke da kaya masu yawa da kyau, ga kuma goro da kud'i har million biyu rigis, Hajia kam ya birgeta a karon farko na rayuwarta, nan aka manta da jiran amarya ake anata duba kayan nan wasu na d'auka hoto, isowar motocin da suka tafi d'aukar amarya ne yasa Hajia kallon Sa'ada tace "Ki shiga da kayan d'akinki ki ajiye."
"To." Ta fad'a tana mik'ewa ta d'auki kayan tare da taimakon k'awayen ta ita ma da suka zo tausar k'irji.
*Alhamdulillah*
09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_*Alhamdulillah Ala ni'imatil islam, Allah nagode maka daka sawak'e min komai, ba yin kaina bane, ba dubarata bace, ba wayona bane, Allah nagode maka, yan uwa kuma nagode sosai da gudummuwarku, Addu'arku ta riskeni a sanda nake da buk'atar ta, haihuwa ta zo min da sauk'i fiye da zatonku, Allah kaine Allah kuma abun godiya, Allah ka raya min yarana ka bani ikon yi musu tarbiya irin ta addinin musulunci.*_👏
*Aci gaba da gashi guy's.*💃
_27_
Ana cikin wannan hidima aka kawo amarya, motoci dai gasu jingim wanda suka paka k'ofar gidan, amma Zeituna bata da dangin da har zasu iya d'aukar motocin, gaba d'aya wanda suka zo rakiyarta basu fi mata ashirin Ba. Kuma a haka wai dangi sun zo ne k'wansu da k'wark'watarsu saboda ta auri mai kud'i, tarba ta musamman suka samu daga gidan girma, inda aka wuce da amarya d'akin ta aka zaunar da ita, saida suka ci suka sha suka k'oshi kafin suka bar gidan tare da yi wa amarya jan kunne cewa karta manta da danginta wajen cin arzik'in, wasu daga cikin motoci aka saka suka mayar dasu gida suka bar amarya da halinta.
Kafatanin yaran gidan ne suka baibaye Zeituna suna kallo, wacce ita kuma ta sanda kanta k'asa ta kasa had'a ido da kowa saboda tunaninta duk kallon rashin mutumci suke mata, Hamna da Amna da Jamila ne suka shigo tare sai Umaimah dake bayansu, zaune sukayi inda Umaimah ke fad'in "Ku kuma ku tashi ku fita ku ba mutane wuri duk kun zo kun sata gaba kuna kallo."
Nazeefa ce ta kalleta tace "Ai dai ganin amarya muka zo."
Cikin tsawa Umaimah tace "Ke dallah tashi ku fita, ba gidan zata zauna ba sai kiyi ta kallonta ai."
Kamal ne ya kalli Umaimah ya mik'e tsaye yana zuba hannayenshi aljihu yace "Kaji mace dan Allah zaki kore mu, amaryar ubana ce fa."
Kallon juna suka shiga yi dan abun ya basu mamaki, a sanin da suka ma Kamal baya da surutu irin haka, Hamna murmushi suka bishi da kallo har suka fita, sai Jamila da tace "Allah yasa kar mu samu yah Ammar na biyu a gidan nan."
"Ameen." Cewar Amna da saurinta, Umaimah ce ta kalli Zeituna wacce k'irjin ta ke dukan uku uku saboda zatonta zasu mata rashin kunya ne shiyasa suka kori yaran, cewa tayi "Aunty Zeituna ki bud'a fuskar ko, yaran sun fita sai mu kawai."
K'ara sanda kanta tayi taja gyalenta ta sake rufe fuska ruf, Hamna ce tabi hannayenta da kallo wanda suka sha lalle ba laifi mai kyau, amma da ganin gyalenta da kayan jikinta kasan ba shirin k'warai tayi ba ko aka mata, duk da bata yanayin farin ciki hannu tasa ta janyo mayafin tana fad'in "Haba aunty Zeituna mu ga kwalliyar mana, mu fa ba bak'in ki bane."
Kallon juna sukayi yayin da Umaimah har saida tayi dariya saboda ganin kwalliyar dake fuskarta, da sauri ta rufe bakinta tana kallon jagirar da ke fuskar Zeituna wacce ta mik'e zat babu lank'wasa,cike da mamaki Amna tace "Aunty Zeituna, waya miki wannan kwalliyar haka?"
Da sauri Zeituna ta d'ago kai ta kalleta sai kuma ta sauke kanta tana mamakin yanda duk suke kiranta da aunty, Umaimah ce tace "Aunty Zeituna, gaskiya tashi ki sake wanka ki zo ki sake shiri, dan kawuna ba zai so ganinki haka ba a darenku na farko."
Tintsirewa sukayi da dariya sai Hamna kawai data girgiza kai tana murmushi, ganin bata da niyyar tashi yasa Amna mik'ewa ta kamata suka nufi ban d'aki tana fad'in "Mik'e mana auntynmu, wannan kwalliya taki ai ta asalin 'yan k'auye ce aka miki."
Turata tayi ban d'akin tace tayi wanka ta fito dan ta goge wannan kwalliyar marar kan gado, Jamila ce ta mik'e tace ma Hamna "Sis ki duba mata kayan daya dace ta saka yanzu, dan ke ce ke shirin zama gwanar kwalliya da iya tsara kaya."
Hararanta tayi tace "Wai ku ina ruwanku da shirinta? Haka kawai ku mata katsalandan, kunsan tana so ko bata so da zaku mata shishigi? Watak'ila fa haka ta iya kwalliyarta, kenan zamu zauna kullum muna yi mata ne?"
Amna ce tace "Ke dai babu ruwanki kawai ki mata, in kuma ba zaki mata ba ki fad'a ni saina mata."
Hararan Amna tayi tace "Bansan iskanci Amna, ina wasa dake ne? To ba zanyi ba ki mata ke."
Mik'ewa tayi zata bar d'akin Amna ta tab'e baki tace "Kar Allah yasa kiyi d'in kiga idan za'a kasa yi mata ne."
Duk da Hamna taji zafin maganar amma banza ta mata dan bata son hayaniya, saida ta kai k'ofa zata fita Amna ta sake cewa "Dama tun jiya kike bak'in rai kamar wacce aka aikowa sak'on mutuwa."
Juyowa tayi ta kalleta cikin hassala tace "Amna bana son iya shege fa, wallahi karki sake min magana, inba haka ba kuma..."
K'wafa tayi ta sake juyawa zata fita Amna tace "Inba haka ba sai me? Me zakayi?"
Juyowa tayi ta dawo cikin harzuk'a tana fad'in "Dan Allah in kin cika 'yar halak ki sake tanka min, Amna ki min magana kiga yanda zan kifar dake a wurin nan."
*'Yan biyu akwai rigima🤔, ko kuma dai na familyn Gaga ne haka.*
Ba tare da wata shakka ba ta matsa kusa da ita tsabar jin masifa tace "Anyi d'in naga me zaki..."
Marin da Hamna ta sauke mata a kumatu yasa ta yin shiru bata shirya ba, dafe kunci tayi ta d'ago daga sunkuyawar da tayi bata shirya ba, da tsantsar mamaki ta kalleta tace "Hamna ni kika mara?"
"An mareki Amna me zakiyi?" Cewar Hamna a hassale, d'orawa tayi da "Ko zaki rama ne marar kunya?"
Ai kuwa Hamna na gama fad'a Amna ta d'auke ta da mari ita ma kamar wasa, jin zafin marin yasa Hamna idonta kad'awa sukayi ja sosai, takaici ne ya lullub'e ta wai k'anwar ta ce ta mareta a fuska, lallai akwai raini tsakaninsu kuma babba, tana shirin kai mata duka Jamila tayi saurin shiga tsakaninsu ta ture Amna gefe guda tana fad'in "Dan Allah kuyi hak'uri ya isa haka, ku bari."
Umaimah ma tasowa tayi ta rik'e Hamna ta fara bata hak'uri, wannan hayaniyar ce ta fito da Zeituna daga ban d'aki da kuma Ummy da su Zeinabu dake d'akin Ummyn wanda yafi kusa dana Zeituna, suna zuwa suma rabasu suka fara yi suna bawa Hamna hak'uri wacce ta d'auki zafi sosai, tabbas kowa yasan ranta ya b'ace saboda yanda ta rikid'e ta zama kamar Amna idan tayi zuciya, kuka Hamna keyi tana fad'in "Wallahi Ummy saina tozarta yarinyar nan, dan na sakar mata fuska shiyasa har zata iya d'aga hannu ta mareni, Allah saina ci uwarta a gidan nan dan ta gane da banbanci ni da ita."
Ummy ce ke fad'in "Kiyi hak'uri nace ko Hamna ta, ki k'yaleta tunda ke ce babba, muje d'akina ki huta kinji ko."
Cikin wani irin kuka kamar wacce aka wa mutuwa tace "Babu inda zanje, Allah saina tattaka ta Ummy, idan ba haka ba kuma kowa zai shiga matsala a gidan nan."
Murmushi Ummy tayi saboda ita dai tasan yan biyunta basu da k'ohi yanzu, dan haka ta jata tana fad'in "Naji to muje dai."
Tirjewa tayi sosai tace babu inda zata je saidai a barta da Amna, ita ma kuma Amna da su Zeinabu ke rik'e da ita cewa take "Dan Allah Ummy ki saketa ta zo ta kashe ni in zata iya, an fad'a miki tsoronki nake ne."
Ganin abun ya k'i kwantawa yasa Ummy daka tsawa tace "Ke Jamila, tunda ba zasu hak'ura ba ku kira Hajia ta zo ta rabasu, ni kam na gaji da wannan jininin kamar kukan tsohuwa."