Sashe 51
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kama rigarshi yayi ta k'asa yayi sama da uta ya zage ya rik'e a hannu, wandon ma dama k'ugunshi roba ce, sab'ule shi yayi ya bar gajeran daya tsaya mishi a cinyoyi, jefawa Amar kayan yayi wanda ke murmushi yana ayyana rashin kunyar da Amna zata gani baiwar Allah, jin kayan a fuskarshi yasa ya yamutse fuska yace "Meye haka kuma?"
Saida Ammar ya zagayo ya zauna d'an nesa da Junaid da suka k'ura mishi ido yace "Ka had'a ka sanya duka, gigin tsohuwar can ya farka yasa ta mana mata a daren nan, kana so kayan bacci ma sai mun saka kala d'aya salon wata rana matarka ta k'wamuso ni a tunaninta kai ne."
Jibril ne yayi dariya yace "To idan ta kama ka d'in ba sai kace mata ba kai bane."
Kallonshi yayi da nufin magana amma ganin kallon da Junaid ke mishi yasa ya had'e fuska yace "Malam ko na mik'e na cire har wannan ma ta yanda za ka ga komai da kyau?"
Da sauri Junaid yace "Kai wa Allah ka rufa mana asiri, ina mu ina ganin wannan al'amari, in a matse kake da kayi tsirara ka jira 'yar k'anwarmu ta zo, wannan ba laifi ba."
Dogon tsaki yayi ya mayar da hankalinshi kan waya, Amar ne dake shirin fita ya cillo mishi kayanshi yace "Dan Allah ka saka kayanka, kasan fa har yara shigowa suke haka ma matan suna iya zuwa yin wani abun."
Kallon Amar d'in yayi yace "To meye a ciki? Duk yaron daya ganni haka ai nima nayi zama kamarshi, kuma shima zai dawo kamar ni d'in, mata kuma da kake magana a kai duk abinda zasu gani suji kunya bai wuce wannan abun ba wanda kuma basa rayuwar jin dad'i sai dashi."
Yanda ya k'arashe maganar yana nuna k'asan gajeran wandonshi da kuma had'e fuskar da yayi kai kace bashi ya fad'a ba yasa Amar cewa "Allah ya shirya ka."
Ba tare daya kalleshi ba yace "Tare da ebolar gidanku ba."
Jibril da tuni ya fahimta ne ya tuntsire da dariya sai Junaid da yace "Wace kuma ebola?"
Jibril ne cikin dariya yace "Wa fa inba Hajia ba, nasan dai ita yake nufi."
Amar ne ya d'an b'ata rai yace "Wallahi Ammar kaji tsoron Allah, ka sani fa kakar ka ce, ya zaka rainata haka?"
Wani kallo ya masa galala yace "Allah ko? To zo ka ci uwani shalelen Hajia."
K'wafa yayi inda Amar ya juya zai fita, muryar Ammar yaji yace "Bani kayana a hannu na."
Juyowa yayi ya kalleshi yace "Kai daka cillo min a hannu na ka damk'a min? Kusa da kai fa suke ka d'auka kawai."
Sake tamke fuska yayi cikin amon muryar da sam babu wasa a ciki yace "Na ce ka bani a hannu na ko."
Tabbas Amar yasan inhar bai bashi ba sai sunyi fad'a, shi kuma yana so ya ga ya cika alk'awarin daya d'aukarwa Ummy na zai dinga hak'uri da d'an uwanshi dan wani lokacin al'amarinshi kamar mai aljanu yake, dawowa yayi ya d'auki kayan ya mik'a mishi kafin ya juya zai fita, kallon bayanshi yayi yace "Idan kaje ka sa mana matar nan ta rubuto maka kalar rayuwar da take so muyi da matan bayan an d'aura auren, dan mu hardace a kanmu ya zauna mana sosai."
Girgiza kai kawai Amar yayi ya fice daga d'akin, d'aukar wandonshi yayi ya saka ya gyara zamanshi kamar zaiyi kwance a kujerar yana danna wayarshi yana shafar shafaffen cikinshi mai shegen fad'i, inda k'irjinshi kuma yace ja bani wuri saboda bud'ewar da yayi, jin su Junaid sunyi shiru yasa ya d'an saci kallonsu yace "Ka fad'a min indai kana sonta har yanzu ni kuma zan karb'omaka aurenta wajen iyayenta?"
Kallonshi sukayi sai Junaid da yace "Ina sonta har yanzu, amma tayaya zakayi haka? Gaskiya bana son wata matsalar Ammar, kuma naga kai kan ka baka tsira ba wajen Hajia."
Murmushin gefen labb'a yayiba tare daya kallesu ba yace "Ku zuba ido kuga ranar da zan fito da wacce nake so, wallahi sai dai ta ganta da ciki kawai ba tare da tasan yaushe haka ta faru ba ma, shirun da kuka ga nayi saboda bana da abin fad'a ne kamar yanda na fad'a ma ita kanta tsohuwar, Amna kuma banda wani dalili na nuna mata tsana ko k'iyayya, dama wannan kankanar ce."
Shiru sukayi dan sun san baida abin fad'a kamar yanda yace, da akwai kuwa daya fad'a ko da abinda zai fad'a zai jawo kwanciyar wani a gadon asibiti.
Amar na fita b'angaren iyayen ya nufa dan amsa kiran da Hajia ta masa, amma yana daf da shiga saiya samu Hamna har yanzu tana zaune tana kuka, tsayawa yayi ya sunkuya kusanta yana kallonta yace "Hamna."
D'agowa tayi ta sauke matsakaitan idontaa kanshi, cikin tausasawa yace "Ke ma kina kukan zab'in da Hajia ta miki ne?"
Saida ta share hawaye da hannunta cikin muryar da tasha kuka tace "A'a yah Amar, yah Junaid d'an uwana ne, ba zan k'i shi, sai dai Hajia ta ruguza min burina na zama gogagiyyar mai tsara kaya (fashion designer) da kuma zama mai kwalliya, sanin kanka ne mu mata Hajia bata yarje mana fita daga garin nan ba da sunan karatu, toya kenan idan nace zan tafi da auren yah Junaid a kai na? Ba zata amince ba, kuma gashi mun riga da mun gama magana da wani compagnie dake *Abuja* zan je a hutun nan da za ayi dan fara d'aukar darasi na kwalliya, shiyasa kawai nake kuka."
Shiru yayi yana kallon yatsun k'afar ta masu tsayi da tudu wanda na kusa da babban yatsan yafi kowane tsayi, ya d'an jima a haka kafin ya mik'e yace "Kiyi hak'uri kinji, zan shiga wajen Hajia yanzu na mata magana, insha Allah burinki ba zai ruguje ba."
D'ago kai tayi ta kalleshi tace "Nagode yahAmar, dan Allah ka min wannan taimakon, idan ba haka ba babu wani abinda nake so sai dai na zama matar gida nima."
Murmushi kawai yayi ya d'an jinjina mata kai ya shige falon, ajiyar zuciya ta sauke dan tasan zaiyi wuya Hajia ta kasa sauraren shalelenta, indai har ya nuna hakan yake so to zata amince ko da ita ba haka ta so ba.
*Fatan nasara Amar*
11/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*SANIN MASOYI*
_(sai Allah)_
*BAYA DA K'URA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
💞 _*MASOYA NA*_💕
_Bismillahir rahamanir rahim_
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_8_
Bud'ar bakin Raudat cewa tayi "Lahh! Ai Ammien mu tana raye, tare suka tafi basraba basraba amma ita bata dawo ba."
Cike da makirci tace "Ayya kunji dad'in ku, kuna da iyayenku a raye suna k'aunar ku, sannan Allah ya muku baiwa ta daula babu abinda kuka nema kuka rasa, sannan na tabbata iyayenku suna farin ciki da junansu bare hankalinku ya dinga tashi idan sun samu sab'ani."
Murmushi Raudat tayi tace "Gaskiya ne aunty, duk da iyayenmu suna yawan fad'a amma dai fad'an nasu na shirme ne, dan duk fad'an su basa awa d'aya basu shirya ba, kuma dama Ammie ita tafi d'aukar zafi."
Ta gefen ido ta kalleta kafin ta d'an zaro ido tace "Kina nufin yanzu nan iyayenku suna fad'a? To akan me?"
Cike da yarinta Raudat tace "Kamar yanda na fad'a miki fad'an su duk shirme ne, amma mafi aksari sunfi rigima akan kishin Ammien mu, wani lokacin kuma bamu san meke had'a su ba sai dai muga Ammie na b'uya a bayan Ammie, idan ita ta tsokani Dady kenan."
Saida ta kamo hannunta tace "Kenan Ammienku batayin duk abinda Dadynku baya so?"
Saida ta firfito da manyan idonta masha Allah kafin tace "Ban sani ba gaskiya, mu dai kawai rayuwar iyayenmu tana bamu sha'awa, suna k'aunar junansu sosai, suna raha da wasa a zamantakewarsu, shiyasa muma muke k'aunar su."
Mik'ewa tayi tace "Aunty bak'uwa saida safe."
Murmushi tayi tace "Aunty bak'uwa kuma? Ki kira ni da *Nasmat*."
Murmushi Raudat ta mata tace "Nice name aunty Nasmat, good night."
Da kallo kawai ta bita harta fita, tana fita ta tab'e baki tana tunano abinda ta fad'a mata, mik'ewa tayi ta cire kayanta ta fad'a toilet, ta jima tana k'arewa toilet d'in kallo ganin kamar ba wajen fitar da datti da k'azanta ba, ko bacci ya kamaka sai kayi a ciki kuma cikin nutsuwa, haka ta fara wanka kafin ta idar ta fito, jakarta da suka taho da ita ta bud'a ta shafa na shafawa ta murza na murzawa sannan ta saka rigar bacci iya gwiwa mai kyau, saida ta zauna kan gadon ta d'auko wasu magungunan mata wanda ta tanadesu dan Abbas kawai tasha sannan ta kwanta.
Suna kammala cin abinci Abbas ya shirya ya tafi taron nan, awa biyu ya d'auke shi kafin ya dawo gida, ya fito a motarshi zai shiga part d'in shi a farfajiyar gidan ya ci karo da mutum, mutum ma mace cikin shirin atamfa tasha ado, wa zai gani inba Harira ba, gidan shiru alamar kowa ya kwanta sai kukan d'awisu da talo-talon dake cikin gidan an ware musu wuri na musamman, tunda ya gane ita ce kawai ya zura kai zai wuce dan haka tayi saurin cewa "Sannu da zuwa yallab'ai."
Tsayawa yayi kawai ya kalleta kamar mai son gane nufinta, wani farrr ta fara da ido tana takowa cikin girgiza jikinta, tabbas kayan sun amshi jikinta musamman yanzu data yi yar k'iba sun zauna mata a jiki, kwalliyar ma ba laifi sai dai kawai in baka sonta ne zaka kushe ta, mamakin irin salon da take taho dashi yake yi harta tsaya gabanshi k'amshin turarenta da baida maraba da na 'yan bori ya daki hancinshi, muryarta ce ta dawo dashi daga d'aukaewar da numfashinshi ya kusa yi saboda bai tab'a jin turare irin wannan mai tayar da hankali ba tana fad'in "Yallab'ai, dama na ga baku dawo tare da Sameera bane, shine nace bara na jira ka dawo ko akwai abinda kake so wanda zan iya yi maka?"
Saida Ammar ya zagayo ya zauna d'an nesa da Junaid da suka k'ura mishi ido yace "Ka had'a ka sanya duka, gigin tsohuwar can ya farka yasa ta mana mata a daren nan, kana so kayan bacci ma sai mun saka kala d'aya salon wata rana matarka ta k'wamuso ni a tunaninta kai ne."
Jibril ne yayi dariya yace "To idan ta kama ka d'in ba sai kace mata ba kai bane."
Kallonshi yayi da nufin magana amma ganin kallon da Junaid ke mishi yasa ya had'e fuska yace "Malam ko na mik'e na cire har wannan ma ta yanda za ka ga komai da kyau?"
Da sauri Junaid yace "Kai wa Allah ka rufa mana asiri, ina mu ina ganin wannan al'amari, in a matse kake da kayi tsirara ka jira 'yar k'anwarmu ta zo, wannan ba laifi ba."
Dogon tsaki yayi ya mayar da hankalinshi kan waya, Amar ne dake shirin fita ya cillo mishi kayanshi yace "Dan Allah ka saka kayanka, kasan fa har yara shigowa suke haka ma matan suna iya zuwa yin wani abun."
Kallon Amar d'in yayi yace "To meye a ciki? Duk yaron daya ganni haka ai nima nayi zama kamarshi, kuma shima zai dawo kamar ni d'in, mata kuma da kake magana a kai duk abinda zasu gani suji kunya bai wuce wannan abun ba wanda kuma basa rayuwar jin dad'i sai dashi."
Yanda ya k'arashe maganar yana nuna k'asan gajeran wandonshi da kuma had'e fuskar da yayi kai kace bashi ya fad'a ba yasa Amar cewa "Allah ya shirya ka."
Ba tare daya kalleshi ba yace "Tare da ebolar gidanku ba."
Jibril da tuni ya fahimta ne ya tuntsire da dariya sai Junaid da yace "Wace kuma ebola?"
Jibril ne cikin dariya yace "Wa fa inba Hajia ba, nasan dai ita yake nufi."
Amar ne ya d'an b'ata rai yace "Wallahi Ammar kaji tsoron Allah, ka sani fa kakar ka ce, ya zaka rainata haka?"
Wani kallo ya masa galala yace "Allah ko? To zo ka ci uwani shalelen Hajia."
K'wafa yayi inda Amar ya juya zai fita, muryar Ammar yaji yace "Bani kayana a hannu na."
Juyowa yayi ya kalleshi yace "Kai daka cillo min a hannu na ka damk'a min? Kusa da kai fa suke ka d'auka kawai."
Sake tamke fuska yayi cikin amon muryar da sam babu wasa a ciki yace "Na ce ka bani a hannu na ko."
Tabbas Amar yasan inhar bai bashi ba sai sunyi fad'a, shi kuma yana so ya ga ya cika alk'awarin daya d'aukarwa Ummy na zai dinga hak'uri da d'an uwanshi dan wani lokacin al'amarinshi kamar mai aljanu yake, dawowa yayi ya d'auki kayan ya mik'a mishi kafin ya juya zai fita, kallon bayanshi yayi yace "Idan kaje ka sa mana matar nan ta rubuto maka kalar rayuwar da take so muyi da matan bayan an d'aura auren, dan mu hardace a kanmu ya zauna mana sosai."
Girgiza kai kawai Amar yayi ya fice daga d'akin, d'aukar wandonshi yayi ya saka ya gyara zamanshi kamar zaiyi kwance a kujerar yana danna wayarshi yana shafar shafaffen cikinshi mai shegen fad'i, inda k'irjinshi kuma yace ja bani wuri saboda bud'ewar da yayi, jin su Junaid sunyi shiru yasa ya d'an saci kallonsu yace "Ka fad'a min indai kana sonta har yanzu ni kuma zan karb'omaka aurenta wajen iyayenta?"
Kallonshi sukayi sai Junaid da yace "Ina sonta har yanzu, amma tayaya zakayi haka? Gaskiya bana son wata matsalar Ammar, kuma naga kai kan ka baka tsira ba wajen Hajia."
Murmushin gefen labb'a yayiba tare daya kallesu ba yace "Ku zuba ido kuga ranar da zan fito da wacce nake so, wallahi sai dai ta ganta da ciki kawai ba tare da tasan yaushe haka ta faru ba ma, shirun da kuka ga nayi saboda bana da abin fad'a ne kamar yanda na fad'a ma ita kanta tsohuwar, Amna kuma banda wani dalili na nuna mata tsana ko k'iyayya, dama wannan kankanar ce."
Shiru sukayi dan sun san baida abin fad'a kamar yanda yace, da akwai kuwa daya fad'a ko da abinda zai fad'a zai jawo kwanciyar wani a gadon asibiti.
Amar na fita b'angaren iyayen ya nufa dan amsa kiran da Hajia ta masa, amma yana daf da shiga saiya samu Hamna har yanzu tana zaune tana kuka, tsayawa yayi ya sunkuya kusanta yana kallonta yace "Hamna."
D'agowa tayi ta sauke matsakaitan idontaa kanshi, cikin tausasawa yace "Ke ma kina kukan zab'in da Hajia ta miki ne?"
Saida ta share hawaye da hannunta cikin muryar da tasha kuka tace "A'a yah Amar, yah Junaid d'an uwana ne, ba zan k'i shi, sai dai Hajia ta ruguza min burina na zama gogagiyyar mai tsara kaya (fashion designer) da kuma zama mai kwalliya, sanin kanka ne mu mata Hajia bata yarje mana fita daga garin nan ba da sunan karatu, toya kenan idan nace zan tafi da auren yah Junaid a kai na? Ba zata amince ba, kuma gashi mun riga da mun gama magana da wani compagnie dake *Abuja* zan je a hutun nan da za ayi dan fara d'aukar darasi na kwalliya, shiyasa kawai nake kuka."
Shiru yayi yana kallon yatsun k'afar ta masu tsayi da tudu wanda na kusa da babban yatsan yafi kowane tsayi, ya d'an jima a haka kafin ya mik'e yace "Kiyi hak'uri kinji, zan shiga wajen Hajia yanzu na mata magana, insha Allah burinki ba zai ruguje ba."
D'ago kai tayi ta kalleshi tace "Nagode yahAmar, dan Allah ka min wannan taimakon, idan ba haka ba babu wani abinda nake so sai dai na zama matar gida nima."
Murmushi kawai yayi ya d'an jinjina mata kai ya shige falon, ajiyar zuciya ta sauke dan tasan zaiyi wuya Hajia ta kasa sauraren shalelenta, indai har ya nuna hakan yake so to zata amince ko da ita ba haka ta so ba.
*Fatan nasara Amar*
11/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*SANIN MASOYI*
_(sai Allah)_
*BAYA DA K'URA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
💞 _*MASOYA NA*_💕
_Bismillahir rahamanir rahim_
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_8_
Bud'ar bakin Raudat cewa tayi "Lahh! Ai Ammien mu tana raye, tare suka tafi basraba basraba amma ita bata dawo ba."
Cike da makirci tace "Ayya kunji dad'in ku, kuna da iyayenku a raye suna k'aunar ku, sannan Allah ya muku baiwa ta daula babu abinda kuka nema kuka rasa, sannan na tabbata iyayenku suna farin ciki da junansu bare hankalinku ya dinga tashi idan sun samu sab'ani."
Murmushi Raudat tayi tace "Gaskiya ne aunty, duk da iyayenmu suna yawan fad'a amma dai fad'an nasu na shirme ne, dan duk fad'an su basa awa d'aya basu shirya ba, kuma dama Ammie ita tafi d'aukar zafi."
Ta gefen ido ta kalleta kafin ta d'an zaro ido tace "Kina nufin yanzu nan iyayenku suna fad'a? To akan me?"
Cike da yarinta Raudat tace "Kamar yanda na fad'a miki fad'an su duk shirme ne, amma mafi aksari sunfi rigima akan kishin Ammien mu, wani lokacin kuma bamu san meke had'a su ba sai dai muga Ammie na b'uya a bayan Ammie, idan ita ta tsokani Dady kenan."
Saida ta kamo hannunta tace "Kenan Ammienku batayin duk abinda Dadynku baya so?"
Saida ta firfito da manyan idonta masha Allah kafin tace "Ban sani ba gaskiya, mu dai kawai rayuwar iyayenmu tana bamu sha'awa, suna k'aunar junansu sosai, suna raha da wasa a zamantakewarsu, shiyasa muma muke k'aunar su."
Mik'ewa tayi tace "Aunty bak'uwa saida safe."
Murmushi tayi tace "Aunty bak'uwa kuma? Ki kira ni da *Nasmat*."
Murmushi Raudat ta mata tace "Nice name aunty Nasmat, good night."
Da kallo kawai ta bita harta fita, tana fita ta tab'e baki tana tunano abinda ta fad'a mata, mik'ewa tayi ta cire kayanta ta fad'a toilet, ta jima tana k'arewa toilet d'in kallo ganin kamar ba wajen fitar da datti da k'azanta ba, ko bacci ya kamaka sai kayi a ciki kuma cikin nutsuwa, haka ta fara wanka kafin ta idar ta fito, jakarta da suka taho da ita ta bud'a ta shafa na shafawa ta murza na murzawa sannan ta saka rigar bacci iya gwiwa mai kyau, saida ta zauna kan gadon ta d'auko wasu magungunan mata wanda ta tanadesu dan Abbas kawai tasha sannan ta kwanta.
Suna kammala cin abinci Abbas ya shirya ya tafi taron nan, awa biyu ya d'auke shi kafin ya dawo gida, ya fito a motarshi zai shiga part d'in shi a farfajiyar gidan ya ci karo da mutum, mutum ma mace cikin shirin atamfa tasha ado, wa zai gani inba Harira ba, gidan shiru alamar kowa ya kwanta sai kukan d'awisu da talo-talon dake cikin gidan an ware musu wuri na musamman, tunda ya gane ita ce kawai ya zura kai zai wuce dan haka tayi saurin cewa "Sannu da zuwa yallab'ai."
Tsayawa yayi kawai ya kalleta kamar mai son gane nufinta, wani farrr ta fara da ido tana takowa cikin girgiza jikinta, tabbas kayan sun amshi jikinta musamman yanzu data yi yar k'iba sun zauna mata a jiki, kwalliyar ma ba laifi sai dai kawai in baka sonta ne zaka kushe ta, mamakin irin salon da take taho dashi yake yi harta tsaya gabanshi k'amshin turarenta da baida maraba da na 'yan bori ya daki hancinshi, muryarta ce ta dawo dashi daga d'aukaewar da numfashinshi ya kusa yi saboda bai tab'a jin turare irin wannan mai tayar da hankali ba tana fad'in "Yallab'ai, dama na ga baku dawo tare da Sameera bane, shine nace bara na jira ka dawo ko akwai abinda kake so wanda zan iya yi maka?"