Sashe 164
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jin motsin zasu fito yasa *Amie* barin wurin da sauri wacce data mik'e zata tafi Zeituna ta fad'a mata ai Hamnar ta dawo tana wajen Ummy, tana zuwa yayi daidai da jin wannan babban sirri da ake ta b'oyo, da sauri ta koma b'angaren Amna ta zauna sai ga Hamna sun shigo, kallonsu take tana ta sak'a da warwara, sai dai ta girgiza kai kawai tayi murmushi, sai taji ma ta kasa tashi ta bar gidan, Amna da Hamna take kallo tana hasaso Ammar a idonta, lallai duk cikin lamarin Amna aka rainwa hankali, to miye abun b'oye mata ana zalintarta, kai ba zai yiwu ba wallahi, *gwara komai ya fito uban kowa yaji duk a k'one tare*, haka ta ci gaba da zama har k'arfe *09:00* dare yayi.
Mutanen d'akin sun rage daga Amna da Hamna sai Amie, sai kuma Husseina wacce suke kwana tare amma tana nesa dasu sai gyangyad'i take, Hamna ce ta tashi ita ma tace "Besty bari na fad'awa Ummy saina aje ki gida."
"Ok besty." Ta fad'a tana binta da kallon yar rainin hankali, saida ta ga fitarta ta gyara zama ta kalli Amna da kyau tace "Amna ke fa yanzu nan baki san komai ba ko?"
Kallonta tayi tace "Komai kamar me fa?"
Girgiza kai tayi tace "Allah sarki, gaskiya Amna ana cutarki a gidan nan, mijinki, yar uwarki da kuka fito ciki d'aya, da kuma Ummy, sun taru suna raina miki hankali."
Duk mutanen da Amie ta ambata mutane ne da suka zama dunk'ulen rayuwarta, mutane ne masu matuk'ar mahimmanci a tattare da ita, dukansu zata iya sadaukar da rayuwarta akan su, dan haka a take taji wani haushinta da tsanarta sun dira a zuciyarta, sama da k'asa ta kalleta tace "Ni dai a sanin dana miki ban sanki da gulma da yarfe ba, bansan kuma yaushe kika koyesu ba?"
Murya k'asa k'asa tace "Amna wallahi maganar gaskiya nale fad'a miki, idan ma baki yarda ba to ki tambayesu kiji."
A kausashe tace "Na tambaye su me Amie? Wai dama gulma kika zo ba dubiya ba? To tashi ki fita."
Tab'e baki tayi ta mik'e tsaye ta kalleta tace "Dama ko a yan biyu akwai baud'add'e, ke kam ba zaki tab'a gane irin cutar da ake miki ba, amma idan mijin naki ya shigo ki tambayeshi waya
haifi Shureim? *Shi ko mahaifinshi*, inhar gaskiya zai fad'a zai ce miki shine, in kuma k'arya zai fad'a zai fad'a miki mahaifinshi ne."
Juyawa tayi tana fad'in "Sai anjima."
Zata fita Hamna ta shigo, juyawa tayi ita ma tace "Yawwa to yi sauri muje Hajia tace kar na jima."
Cikin wata irin murya Amna tace "Dakata."
Tsayawa sukayi suka juya suna kallonta, ba tare data tashi daga inda take ba ta kalli Hamna ido cikin ido babu yanayin wasa tace "Ki koma ciki babu inda zaki kaita."
Da mamaki Hamna tace "Me yasa?"
"Saboda munafuka ce." Ta fad'a kai tsaye, murmushi Hamna tayi a tunaninta jikin ne ya motsa tace "Kiyi hak'uri kinji yer uwa, ba jimawa zanyi ba yanzu zan dawo."
Da k'arfi tace "Hamna babu inda zaki kaita, in kuma baki yarda ba to kuje ga hanyar nan."
Kallon Amie Hamna tayi ta k'yabta mata ido alamar su mata wayo sai a zahiri da tace "Besty kawai ki tafi tunda yer uwata bata so ba zanje ba."
Jinjina kai Amie tayi ta fita, Hamna na ganin haka ta kalli Amna tace "Akwai abinda kike so na miki ne ko ka naje na kwanta? Bacci nale ji sosai."
Kallonta tayi tace "Kije ki kwanta saida safe."
Juyawa tayi ta fita tana zuwa ta ja mota ta fita ta d'auki Amie, hak'uri ta bata kan abinda ya faru tace ba komai. Tana fita Amna ta bita da kallo, murmushi tayi tace "Ko yaushe Amie ta haukace kuma? Su yanzu nan mutane kallon mai hankali suke mata? Lallai ma Allah ya bata lafiya."
Daga nan zaune ta saki wannan maganar kamar anyi rubutu a saman ruwa, jikinta ya bata Hamna ta tafi ta kai Amie gida ne, k'wafa tayi tace "Haba, kuje d'in mu gani."
Saida sukayi nisa da gida kuma basu kai ko rabin gidansu Amie ba mota ta tsaya cak, ko da Hamna ta duba wajen dake bayyana idan mai ne babu taga tanki cike yake, nan ta shiga tayar wa amma mota shiru, tsayawa tayi tana girgiza kai tana murmushi a hankali take fad'in "Amna, Amna, amma zan ci uwarki, ni zaki wa iskanci."
K'wafa tayi ta kalli Amie tace "K'awata, hak'uri zakiyi ki samu adaidaita ki hau, in dai ina tare dake to babu inda zan gusa."
Da mamaki ta kalleta tace "Me yasa? Wani abun ne ya faru?"
Murmushi ta mata tace "Ba zaki gane ba, kawai ki samu adaidaita."
Bud'e motar tayi ta fita ta kalleta tace "To ke ya zakiyi?"
Saida ta kalli titi tace "Karki damu, idan ma bata tashi ba zan kira a zo a d'auke ni."
"Ok, ki kula da kanki."
Jinjina kai tayi tace "Ok, saida safe."
Nan ta samu adaidaita ta tafi, tun a hanya data shiga WhatsApp d'inta ta kasa hak'uri ta tab'o sauran k'awayenta su biyu, gulma ajali inji yan magana, haka suka jima suna tattaunawa suna fad'in ashe ta ma fisu iskanci, shine in taga suna rayuwarsu saita dinga nuna tana k'yamar abun, ashe ita har shege ma gare ta kuma da mijin yar uwarta.
Saida ta ga tafiyar Amie ta kira Amna a waya, har ta kusa tsinkewa sannan ta d'auka tace "Lafiya? Har kin kaita d'in?"
Dariya Hamna tayi dan su rabu lafiya kar ta jawa motarta kwana akan titi, cikin muryar rarrashi tace "Dan Allah yar k'anwata taimaka min ina so na koma gida kinji, dare kayi kar Abba ya min fad'a."
Cikin kumburo baki Amna tace "Na k'i d'in, bani kika rainawa hankali ba?"
Sake mak'ale murya tayi tace "Dan Allah fa nace."
"To shinenan, ki bani hak'uri yanzu." Cewar Amna.
Saida ta gyara murya tace "To aunty Amna kiyi hak'uri."
Murmushi Amna tayi tace "Shikenan to kiyi sauri ki dawo gida kar wani ya sace min ke."
Dariya tayi tana wa motar key tace "An gama zuciyata."
Ko da ta kunna ta kama tana murmushi tayi baya baya ta d'auki hanyar komawa gida.
*Da safe* Hamna na ta kai da kawon gyara falon an gama ma bébé wanka, duk inda tayi sai Amna tabi ta da kallo, tun bata lura ba har ta ankare, tun abun bai tsaya mata akai ba har ta fara tsarguwa da kallon, tsayawa tayi tana kallonta tace"Wai ke lafiya?"
Sai kawai ta bushe da dariya kamar mahaukaciya, kallon mamaki Hamna ta bita dashi ta girgiza kai ta ci gaba da aikinta, Ummy na shigowa cikin shirin tafiya aiki da Shureim a hannunta, hannu ta tarawa Shureim tace "Zo nan."
Takawa yayi ya je wurinta ya tsaya, rik'e hannunshi tayi tana mishi wani kallo kamar yau ta fara ganinshi, sai kawai ta matso dashi kusanta ta sumbaci goshinshi, saida ta d'auke bakinta ta sake kallon fuskarshi sai tace "Kai ni fa sai naji na fi sonka da aka ce yar uwata ma ta haifeka."
Wani yamutsawar hanji Ummy da Hamna suka ji a lokaci d'aya, Husseina dake karin kumallo kallonta tayi irin kallon anya kuwa Amna, da sauri suka kalli juna suna zazzaro ido na alamar tambayar me ke faruwa, kallonsu Amna tayi a tare saida ta gama kallonsu sai tayi dariya ta nuna Hamna da hannu tace "Sakarya, ji yanda kika zaro ido kamar mahaukaciya, ko ke ma kin haukace irin na k'awarki?"
Da sauri suka saisaita nutsuwarsu, sai Ummy data kalli Husseina tace "Anya Hajia kuwa lafiyarta k'alau?"
Cikin murya k'asa k'asa tace "Ni ma dai abinda nake tunani kenan."
Amna kam kallon Shureim ta sake yi tace "Baka tafi islamiyya ba kai?"
A hankali yace "Yanzu Ummy zata kaini."
Murmushi ta masa tace "Yawwa, kana ji ko? Ka dinga karatu sosai saboda ka zama babban malami, kana so ka zama kamar wannan kai ma?"
Ta fad'a tana d'aukar wayarta, wa'azin *ustaz Rayyadun* (Allah k'ara girma malaminmu) ta nuna masa na vidéo tace "Ka gani ko? Ka zama kamar wannan kaima, kana so?"
Kai kawai ya d'aga mata irin shi dai yana saurarenta, su dai kallonta suke har Ummy ta mik'e ta kama shi suka fita, hankalin Hamna ya kasa kwanciya duk a takure take jin kanta, ta k'i yarda su had'a ido da Amna wacce ita kuma take ta binta da kallo har yanzu, idan ta ga Hamna ta k'i kallonta sai ta bushe da dariya, duk wanda ya zo gidan haka zai iskota a wannan yanayin, gashi kuma Hamna babu damar da zata barta dan wani abun sai tace dole Hamna ce kawai zata mata, haka suka dinga wannan zama babu dad'i babu hira tsakaninsu, sai dai ita Amnar tayi ta nata maganganun masu kama dana mai shirin barin duniya.
*Kwana uku* yau da faruwar wannan lamari, shirin biki ake ta yi sai dai ba wani da karsashi ake yinshi saboda yanayin jikin mai jego, kullum cikin taka tsantsan ake kan d'inkinta, ana yawan kwakwafarta kan rage magana da dariya mai k'arfi, amma abun sai a hankali in tayi wani abun kamar dai k'walwarta ce ta fara samun matsala. Yanzu ma Ammar ne ya shigo da babbar leda a hannu, ko da ya gaishe da mutanen d'akin ya nufi nashi d'akin, kamar daga sama aka tsinci muryar Amna tace "Ammar."
Cak ya dakata ya juyo ya kalleta, *Ammar*? Tunda yake da ita daga k'uruciya har girmanta bai tab'a ji ta kama sunansa ba haka, dama dai waccen marar kunyar ce, su kansu mutane mamaki ne ya kama su jin yanda ta kira sunan nashi kamar sunan Ammar k'arami, shi kanshi Ammar k'arami saida ya juyo ya kalleta, har ya cire hannunshi daga abincin da yake ci zai taho tace "Ba kai ba zauna."
K'ok'arin mik'ewa ta shiga yi hakan yasa Ummy taimaka mata ta tashi, saida taje kusanshi ta kalle shi tace "Muje ciki."
Mutanen d'akin sun rage daga Amna da Hamna sai Amie, sai kuma Husseina wacce suke kwana tare amma tana nesa dasu sai gyangyad'i take, Hamna ce ta tashi ita ma tace "Besty bari na fad'awa Ummy saina aje ki gida."
"Ok besty." Ta fad'a tana binta da kallon yar rainin hankali, saida ta ga fitarta ta gyara zama ta kalli Amna da kyau tace "Amna ke fa yanzu nan baki san komai ba ko?"
Kallonta tayi tace "Komai kamar me fa?"
Girgiza kai tayi tace "Allah sarki, gaskiya Amna ana cutarki a gidan nan, mijinki, yar uwarki da kuka fito ciki d'aya, da kuma Ummy, sun taru suna raina miki hankali."
Duk mutanen da Amie ta ambata mutane ne da suka zama dunk'ulen rayuwarta, mutane ne masu matuk'ar mahimmanci a tattare da ita, dukansu zata iya sadaukar da rayuwarta akan su, dan haka a take taji wani haushinta da tsanarta sun dira a zuciyarta, sama da k'asa ta kalleta tace "Ni dai a sanin dana miki ban sanki da gulma da yarfe ba, bansan kuma yaushe kika koyesu ba?"
Murya k'asa k'asa tace "Amna wallahi maganar gaskiya nale fad'a miki, idan ma baki yarda ba to ki tambayesu kiji."
A kausashe tace "Na tambaye su me Amie? Wai dama gulma kika zo ba dubiya ba? To tashi ki fita."
Tab'e baki tayi ta mik'e tsaye ta kalleta tace "Dama ko a yan biyu akwai baud'add'e, ke kam ba zaki tab'a gane irin cutar da ake miki ba, amma idan mijin naki ya shigo ki tambayeshi waya
haifi Shureim? *Shi ko mahaifinshi*, inhar gaskiya zai fad'a zai ce miki shine, in kuma k'arya zai fad'a zai fad'a miki mahaifinshi ne."
Juyawa tayi tana fad'in "Sai anjima."
Zata fita Hamna ta shigo, juyawa tayi ita ma tace "Yawwa to yi sauri muje Hajia tace kar na jima."
Cikin wata irin murya Amna tace "Dakata."
Tsayawa sukayi suka juya suna kallonta, ba tare data tashi daga inda take ba ta kalli Hamna ido cikin ido babu yanayin wasa tace "Ki koma ciki babu inda zaki kaita."
Da mamaki Hamna tace "Me yasa?"
"Saboda munafuka ce." Ta fad'a kai tsaye, murmushi Hamna tayi a tunaninta jikin ne ya motsa tace "Kiyi hak'uri kinji yer uwa, ba jimawa zanyi ba yanzu zan dawo."
Da k'arfi tace "Hamna babu inda zaki kaita, in kuma baki yarda ba to kuje ga hanyar nan."
Kallon Amie Hamna tayi ta k'yabta mata ido alamar su mata wayo sai a zahiri da tace "Besty kawai ki tafi tunda yer uwata bata so ba zanje ba."
Jinjina kai Amie tayi ta fita, Hamna na ganin haka ta kalli Amna tace "Akwai abinda kike so na miki ne ko ka naje na kwanta? Bacci nale ji sosai."
Kallonta tayi tace "Kije ki kwanta saida safe."
Juyawa tayi ta fita tana zuwa ta ja mota ta fita ta d'auki Amie, hak'uri ta bata kan abinda ya faru tace ba komai. Tana fita Amna ta bita da kallo, murmushi tayi tace "Ko yaushe Amie ta haukace kuma? Su yanzu nan mutane kallon mai hankali suke mata? Lallai ma Allah ya bata lafiya."
Daga nan zaune ta saki wannan maganar kamar anyi rubutu a saman ruwa, jikinta ya bata Hamna ta tafi ta kai Amie gida ne, k'wafa tayi tace "Haba, kuje d'in mu gani."
Saida sukayi nisa da gida kuma basu kai ko rabin gidansu Amie ba mota ta tsaya cak, ko da Hamna ta duba wajen dake bayyana idan mai ne babu taga tanki cike yake, nan ta shiga tayar wa amma mota shiru, tsayawa tayi tana girgiza kai tana murmushi a hankali take fad'in "Amna, Amna, amma zan ci uwarki, ni zaki wa iskanci."
K'wafa tayi ta kalli Amie tace "K'awata, hak'uri zakiyi ki samu adaidaita ki hau, in dai ina tare dake to babu inda zan gusa."
Da mamaki ta kalleta tace "Me yasa? Wani abun ne ya faru?"
Murmushi ta mata tace "Ba zaki gane ba, kawai ki samu adaidaita."
Bud'e motar tayi ta fita ta kalleta tace "To ke ya zakiyi?"
Saida ta kalli titi tace "Karki damu, idan ma bata tashi ba zan kira a zo a d'auke ni."
"Ok, ki kula da kanki."
Jinjina kai tayi tace "Ok, saida safe."
Nan ta samu adaidaita ta tafi, tun a hanya data shiga WhatsApp d'inta ta kasa hak'uri ta tab'o sauran k'awayenta su biyu, gulma ajali inji yan magana, haka suka jima suna tattaunawa suna fad'in ashe ta ma fisu iskanci, shine in taga suna rayuwarsu saita dinga nuna tana k'yamar abun, ashe ita har shege ma gare ta kuma da mijin yar uwarta.
Saida ta ga tafiyar Amie ta kira Amna a waya, har ta kusa tsinkewa sannan ta d'auka tace "Lafiya? Har kin kaita d'in?"
Dariya Hamna tayi dan su rabu lafiya kar ta jawa motarta kwana akan titi, cikin muryar rarrashi tace "Dan Allah yar k'anwata taimaka min ina so na koma gida kinji, dare kayi kar Abba ya min fad'a."
Cikin kumburo baki Amna tace "Na k'i d'in, bani kika rainawa hankali ba?"
Sake mak'ale murya tayi tace "Dan Allah fa nace."
"To shinenan, ki bani hak'uri yanzu." Cewar Amna.
Saida ta gyara murya tace "To aunty Amna kiyi hak'uri."
Murmushi Amna tayi tace "Shikenan to kiyi sauri ki dawo gida kar wani ya sace min ke."
Dariya tayi tana wa motar key tace "An gama zuciyata."
Ko da ta kunna ta kama tana murmushi tayi baya baya ta d'auki hanyar komawa gida.
*Da safe* Hamna na ta kai da kawon gyara falon an gama ma bébé wanka, duk inda tayi sai Amna tabi ta da kallo, tun bata lura ba har ta ankare, tun abun bai tsaya mata akai ba har ta fara tsarguwa da kallon, tsayawa tayi tana kallonta tace"Wai ke lafiya?"
Sai kawai ta bushe da dariya kamar mahaukaciya, kallon mamaki Hamna ta bita dashi ta girgiza kai ta ci gaba da aikinta, Ummy na shigowa cikin shirin tafiya aiki da Shureim a hannunta, hannu ta tarawa Shureim tace "Zo nan."
Takawa yayi ya je wurinta ya tsaya, rik'e hannunshi tayi tana mishi wani kallo kamar yau ta fara ganinshi, sai kawai ta matso dashi kusanta ta sumbaci goshinshi, saida ta d'auke bakinta ta sake kallon fuskarshi sai tace "Kai ni fa sai naji na fi sonka da aka ce yar uwata ma ta haifeka."
Wani yamutsawar hanji Ummy da Hamna suka ji a lokaci d'aya, Husseina dake karin kumallo kallonta tayi irin kallon anya kuwa Amna, da sauri suka kalli juna suna zazzaro ido na alamar tambayar me ke faruwa, kallonsu Amna tayi a tare saida ta gama kallonsu sai tayi dariya ta nuna Hamna da hannu tace "Sakarya, ji yanda kika zaro ido kamar mahaukaciya, ko ke ma kin haukace irin na k'awarki?"
Da sauri suka saisaita nutsuwarsu, sai Ummy data kalli Husseina tace "Anya Hajia kuwa lafiyarta k'alau?"
Cikin murya k'asa k'asa tace "Ni ma dai abinda nake tunani kenan."
Amna kam kallon Shureim ta sake yi tace "Baka tafi islamiyya ba kai?"
A hankali yace "Yanzu Ummy zata kaini."
Murmushi ta masa tace "Yawwa, kana ji ko? Ka dinga karatu sosai saboda ka zama babban malami, kana so ka zama kamar wannan kai ma?"
Ta fad'a tana d'aukar wayarta, wa'azin *ustaz Rayyadun* (Allah k'ara girma malaminmu) ta nuna masa na vidéo tace "Ka gani ko? Ka zama kamar wannan kaima, kana so?"
Kai kawai ya d'aga mata irin shi dai yana saurarenta, su dai kallonta suke har Ummy ta mik'e ta kama shi suka fita, hankalin Hamna ya kasa kwanciya duk a takure take jin kanta, ta k'i yarda su had'a ido da Amna wacce ita kuma take ta binta da kallo har yanzu, idan ta ga Hamna ta k'i kallonta sai ta bushe da dariya, duk wanda ya zo gidan haka zai iskota a wannan yanayin, gashi kuma Hamna babu damar da zata barta dan wani abun sai tace dole Hamna ce kawai zata mata, haka suka dinga wannan zama babu dad'i babu hira tsakaninsu, sai dai ita Amnar tayi ta nata maganganun masu kama dana mai shirin barin duniya.
*Kwana uku* yau da faruwar wannan lamari, shirin biki ake ta yi sai dai ba wani da karsashi ake yinshi saboda yanayin jikin mai jego, kullum cikin taka tsantsan ake kan d'inkinta, ana yawan kwakwafarta kan rage magana da dariya mai k'arfi, amma abun sai a hankali in tayi wani abun kamar dai k'walwarta ce ta fara samun matsala. Yanzu ma Ammar ne ya shigo da babbar leda a hannu, ko da ya gaishe da mutanen d'akin ya nufi nashi d'akin, kamar daga sama aka tsinci muryar Amna tace "Ammar."
Cak ya dakata ya juyo ya kalleta, *Ammar*? Tunda yake da ita daga k'uruciya har girmanta bai tab'a ji ta kama sunansa ba haka, dama dai waccen marar kunyar ce, su kansu mutane mamaki ne ya kama su jin yanda ta kira sunan nashi kamar sunan Ammar k'arami, shi kanshi Ammar k'arami saida ya juyo ya kalleta, har ya cire hannunshi daga abincin da yake ci zai taho tace "Ba kai ba zauna."
K'ok'arin mik'ewa ta shiga yi hakan yasa Ummy taimaka mata ta tashi, saida taje kusanshi ta kalle shi tace "Muje ciki."