Sashe 77
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonshi Abbas yayi sosai, hak'ik'a yasan Alhaji Khamis mutumin kirki ne mai sanin ya kamata da dattako, sai dai kuma baisan komai a game da d'an sa ba, duk lalacewar Raihan kuwa zai yarda yayi wannan gangancin? Ganin baice komai ba yasa Alhaji Khamis cewa "Nasan abune mai wahala, amma karka damu ka fad'a min abinda ke ranka, maganar aure tafi k'arfin wasa, Baban gidan bai tab'a aure ba, karatu ya saka a gaba, yanzu haka ma yana *Maroc* wurin karatu, amma shekara mai zuwa zai kammala ya dawo gida, sunan mahaifina ne da shi, wato takwaranka ne."
Kallonshi Abbas yayi sai kawai yace "Ba damuwa Alhaji Khamis, ai hallaci ka mana, kasan yarana ka haifesu amma baka haifi halinsu ba."
Take suka shiga masallacin yan mutanen da suka rage suka shaida d'aurin auren *Abbas Khamis Abbas* da kuma *Khadija (Raihan) Abbas Abdul rahaman* akan sadaki dubu d'ari biyu.
Suna fitowa daga masallaci ana taya juna murna suna tattauna yanda tariyar zata kasance, amma Abbas cewa yayi ai kawai tunda shi Khamis gobe ne zai tafi to kawai zai tafi tare da surukarshi, sannan a yau zai gama mata shirye shirye taje can ta samu mijinta, kuma duk yayi hakane dan ya kawar da ita daga gabanshi, dan ranshi b'acewa yake idan ya ganta kuma tana tuna mishi da abinda shi ma ya aikata, nan Alhaji Khamis ya kira gida ya sanar da iyalai, mahaifiyar Baban gida ta rasu sai kishiyoyi, hakan yasa babu wacce tayi murna da jin haka, dan su abinda suka hango ba wai dalilin auren da gaggawa ba, a'a, tarin dukiyar da mahaifin yarinyar ke da shi, mutumin daya mallaki jirage na kanshi, compagnie da masana'antu ba adadi, sannan uwarta ma jinin sarauta ce, wannan bak'in cikin yasa suka kasa farin ciki, saidai sunyi abincin sadaka kamar yanda mai gidan yace, dan in basuyi ba rai zai b'ace kasancewarshi mutum jajirtattace a gidanshi.
Baban gida ma da yaji musu yayi wa mahaifin nashi, amma dayake yana da zafi saiya balbaleshi da bala'i yace idan ya turo mishi yarinyar ya yankata idan ya cika d'an halak ne shi, haka yaja baki yayi shiru shima yana jiran isowar yarinyar.
*Ma'aruf* da kanshi ne ya shigo musu da abun kari, babu abinda Ma'arufa tayi tunani dan dama kusan kullum shi ke siyowa, ko da baya da kud'i ita zata bayar ya siyo, yana kallonta har ta gama cin indomie ta d'auki lemun daya siyo mai sanyi ta fita dashi tana sha, fatan alkairi ya mata har da cewa tayi sauri ta dawo fa, tana kan hanyar zuwa ta kira Abbas a lokacin an d'aura auren yana wa su Ammie bayani, ganin lambarta yasa shi barin waje ya d'anyi nesa da su, Harira data fito d'auke da jus jus d'in da zata kaiwa bak'in dake gidan ta ganshi yana amsa waya, tsayawa tayi ta lab'e ta kasa kunne tana sauraren shi.
Abinda taji kawai shine "Naji, mu had'u a inda muka had'u jiya, amma ki sani wannan uta ce had'uwarmu ta k'arshe dake."
Tana ganin ya nufi wajen ajiyar motoci ta d'an fito daga lab'ewarda tayi ta aje jus jus d'in ta rigashi fita, yana fitowa ya d'auki hanya ita ma cikin sa'a adaidaita ta fito daga kwana, shiga tayi tace su bi bayan motar...
👏👏👏
22/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_21_
"Dan ubanka meye haka? Wallahi idan ka sake dukanta saina rama mata tunda d'an iska ne kai, Ammar meye haka? Zalincin ne ya motsa maka? Wannan wane irin haukane da iskanci? Me yarinyar nan ta maka da zaka kamata da duka haka?"
Cikin d'aga murya kamar zai fasa gidan yace "Ummy inba raini da iskanci ba ni Amna zata rainawa hankali? Na d'auke na kaita shagon Ilu amma dan iskanci a gabana zata tsaya kula wani bayan kuma tasan nine mijinta, akan me zata min haka? Laifin me nayi? Tana so ta nuna ni ba cikakken namiji bane ko me? Waccen d'in da me ya fini? Kyau? Ilimi ko kud'i? Ko kuma lafiya da girman jiki taga ya fini?"
Cikin hassala Ummy tace "Mijinta? An d'aura maka auren da ita ne? Kai bari ma na tambayeka? Ka k'addara an d'aura muku auren, kenan haka zaka mata wannan dukan tana matsayin matar taka?"
Zaro ido yayi yace "To me zan mata? D'aki zan sakata na dinga rera mata wak'a ina mata rawa dan na kwantar mata da hankali?"
Kallonshi Ummy tayi tace "In kuwa hakane lallai ba namiji bane kai, ba zaka tab'a zama jarumin namiji a gurin mace mai hankalin da tasan ciwon kanta, tun ranar da aka ce Amna ce k'addarar aurenka ta fad'a mata na fara mata kukan tausayi, dan indai har akayi kuskuren had'a ta da kai to babu makawa yarinyar nan tana daf da ajalinta."
Take yaji wasu hawaye na son taho mishi, mahaifiyarshi ce data haifeshi take fad'a masa haka? K'ok'ari yayi ya mayar da hawayen ya kalli Amna yace "Kina ji ko? A dalilinki ne take fad'a min haka, ni kuma nayi alk'awari saina tabbatar muku da namiji ne ni."
Girgiza kai Ummy tayi ta kama Amna suka mik'e tana gyara doguwar rigarta, Husseina ce da mamaki ya isheta tace "Amna kuma? Ai ba Amna bace Hamna ce, Ammar meyasa baka tsaya kayi tunani ba kawai ka hau dukanta haka?"
Dafe k'ugu yayi da hannu d'aya hannu d'aya kuma ya nuna kanshi yace "Kenan yanzu na zama mahaukaci ne da ban iya gane yaran da har goyasu nayi a bayana? Yaran da suka tashi a gaban idona ne zan kasa fahimtar wacece wannan ko wacce waccen?"
Kallonta Ummy tayi dan ta gane wacece ma a ciki, sai dai duhun dake akwai wajen bai bari ta iya ganewa ba, hakan yasa tace "Da gaske ne? Amna ce?"
Gyad'a kai tayi alamar eh, sallalami Husseina ta fara ta rik'e baki tace "Oh ni Husseina, yanzu dama Amna ce nake wa kallon Hamna? Amma meyasa dana kira Hamna kika amsa? Ita tana ina?"
Amna da har yanzu take jin marin nan daya mata da takalmi kuka kawai ta sake fashewa dashi, shi kuma k'wafa yayi ya kalleta ya nunata yace "Daga yanzu duk inda zaki je saina baki izini indai har nine wanda zai aure ki." wucewa yayi inda Ummy ta bishi da kallo ganin jikinshi biji-biji ga kayanshi sai k'yallin mai suke, kama Amna tayi suka shiga ciki bata yarda sun tsaya falon ba, sama suka haura d'akin su suka zaunar da ita, fad'a Ummy keyi sosai na haushi da takaici, har da cewa "To ubanki ne shi da har zaki tsaya ya miki wannan dukan? Ba dan kin zama sakarya ba ma akan me zakiyi tsaye yana d'irkarki haka? Amna aure fa ake shirin yi miki dashi, da hakane zaku zauna kinsa tsoronsa a ranki? Na tabbata da yer uwarki ce Hamna wallahi ko gudu ne tayi daga gurinshi, dan baya da maraba da mahaukaci idan ranshi ya b'ace."
Amna dai shiru tayi sai sharar hawaye take, hakan yasa Ummy cewa "Kiji harda wani cewa wai in zaki fita saida izininshi, to mu duk aikin banza ne kenan a gidan? To zaki fita bada izinin nashi ba sai naga in kasheki zaiyi."
D'agowa Amna tayi cikin kuka tace "A'a Ummy, tunda dai yace haka ni zan bi umarninshi, zan nemi izininshi kafin na fita, shikenan sai a zauna lafiya, ko Mama ma tana fad'a mana mu dinga jin maganarshi dan shi kad'ai ne ke tsawatar mana."
Da mamaki Ummy tace "Ke yanzu sai ki biye masa kuma?"
Jinjina kai tayi alamar eh tare da cewa "Ummy hakan shine zaman lafiya na, nasan ni ba yer uwata Hamna bace, nice mafad'aciyar kuma mai zuciyar, amma akan yah Ammar bana da ko d'aya, bansan meyasa ba."
Tab'e baki Ummy tayi tace "Lallai kina da aiki Amna."
Ko da yayi wanka shiryawa yayi cikin riga da wando bak'ak'e, makullin mota ya d'auka ya sake fita, k'aramin gurin cin abinci ne *Kebab* ya zauna ya ci abinci, daga nan kuma hanya ya d'auka saida ya samu inda babu hayaniya ya paka nan, jingina kawai yayi yana sauraron wa'azindake tashi a motar, maganganun Ummy ne kawai ke dawo masa a k'wak'walwa, awa d'aya da rabi ya d'auka a wurin nan kamar mai bacci kafin wayarshi ta fara ruri, saida kiran ya tsinke aka sake maidowa kad'ai ya taso daga kwanciyar da yayi ya d'auki wayar, a zuciyarshi yace "Abdullahi kuma? Meyasa zai kirani a wannan lokacin?"
Tsaki yayi saboda wata zuciyar data fad'a masa watak'ila zai maka k'orafine saboda baka je d'aukar amarya ba, d'auka yayi ya d'ora a kunne yayi shiru, daga can b'angaren Abdullahi yace "Ammar yane? Kana cikin gari ko kana gida?"
Can k'asan mak'oshi yace "Lafiya?"
Abdullahi ne yace "Lafiya ba lafiya, dama a cikin yan matan amarya ne aka bar wasu basu samu komawa tare da sauran mutane ba, kuma gashi duk wanda na kira wallahi wasu ma sun fad'a min kai tsaye ba zasu iya dawowa d'aukar su, ni ma kuma mota ta tun safe tana hannun k'ane na, yanzu haka nafi awa d'aya ina jiran adaidaita sahu ko taxi na samar musu amma wallahi shiru, gashi dare na k'arayi shiyasa nace bara na kiraka dan Allah ka zo ko Hamna ka d'auka, tunda kaga gidanku ba bari fitar dare ake yi ba inba da dalili mai..."
Ammar ne ya dakatar dashi cikin sanyayyar murya yace "Ya isa haka dan Allah, magana ba tsayawa ba numfasawa, yanzu kenan nufinka naje na zama drebata na d'auko ta? Bayan kuma a gida babu wanda ma yasan da fitarta, to ba zan iya ba."
Abdullahi ne yace "Dan Allah Ammar ka taimaka, bana so ne ta shiga matsala a dalilin halartar bikin nan nawa, dan Allah."
Kallonshi Abbas yayi sai kawai yace "Ba damuwa Alhaji Khamis, ai hallaci ka mana, kasan yarana ka haifesu amma baka haifi halinsu ba."
Take suka shiga masallacin yan mutanen da suka rage suka shaida d'aurin auren *Abbas Khamis Abbas* da kuma *Khadija (Raihan) Abbas Abdul rahaman* akan sadaki dubu d'ari biyu.
Suna fitowa daga masallaci ana taya juna murna suna tattauna yanda tariyar zata kasance, amma Abbas cewa yayi ai kawai tunda shi Khamis gobe ne zai tafi to kawai zai tafi tare da surukarshi, sannan a yau zai gama mata shirye shirye taje can ta samu mijinta, kuma duk yayi hakane dan ya kawar da ita daga gabanshi, dan ranshi b'acewa yake idan ya ganta kuma tana tuna mishi da abinda shi ma ya aikata, nan Alhaji Khamis ya kira gida ya sanar da iyalai, mahaifiyar Baban gida ta rasu sai kishiyoyi, hakan yasa babu wacce tayi murna da jin haka, dan su abinda suka hango ba wai dalilin auren da gaggawa ba, a'a, tarin dukiyar da mahaifin yarinyar ke da shi, mutumin daya mallaki jirage na kanshi, compagnie da masana'antu ba adadi, sannan uwarta ma jinin sarauta ce, wannan bak'in cikin yasa suka kasa farin ciki, saidai sunyi abincin sadaka kamar yanda mai gidan yace, dan in basuyi ba rai zai b'ace kasancewarshi mutum jajirtattace a gidanshi.
Baban gida ma da yaji musu yayi wa mahaifin nashi, amma dayake yana da zafi saiya balbaleshi da bala'i yace idan ya turo mishi yarinyar ya yankata idan ya cika d'an halak ne shi, haka yaja baki yayi shiru shima yana jiran isowar yarinyar.
*Ma'aruf* da kanshi ne ya shigo musu da abun kari, babu abinda Ma'arufa tayi tunani dan dama kusan kullum shi ke siyowa, ko da baya da kud'i ita zata bayar ya siyo, yana kallonta har ta gama cin indomie ta d'auki lemun daya siyo mai sanyi ta fita dashi tana sha, fatan alkairi ya mata har da cewa tayi sauri ta dawo fa, tana kan hanyar zuwa ta kira Abbas a lokacin an d'aura auren yana wa su Ammie bayani, ganin lambarta yasa shi barin waje ya d'anyi nesa da su, Harira data fito d'auke da jus jus d'in da zata kaiwa bak'in dake gidan ta ganshi yana amsa waya, tsayawa tayi ta lab'e ta kasa kunne tana sauraren shi.
Abinda taji kawai shine "Naji, mu had'u a inda muka had'u jiya, amma ki sani wannan uta ce had'uwarmu ta k'arshe dake."
Tana ganin ya nufi wajen ajiyar motoci ta d'an fito daga lab'ewarda tayi ta aje jus jus d'in ta rigashi fita, yana fitowa ya d'auki hanya ita ma cikin sa'a adaidaita ta fito daga kwana, shiga tayi tace su bi bayan motar...
👏👏👏
22/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_21_
"Dan ubanka meye haka? Wallahi idan ka sake dukanta saina rama mata tunda d'an iska ne kai, Ammar meye haka? Zalincin ne ya motsa maka? Wannan wane irin haukane da iskanci? Me yarinyar nan ta maka da zaka kamata da duka haka?"
Cikin d'aga murya kamar zai fasa gidan yace "Ummy inba raini da iskanci ba ni Amna zata rainawa hankali? Na d'auke na kaita shagon Ilu amma dan iskanci a gabana zata tsaya kula wani bayan kuma tasan nine mijinta, akan me zata min haka? Laifin me nayi? Tana so ta nuna ni ba cikakken namiji bane ko me? Waccen d'in da me ya fini? Kyau? Ilimi ko kud'i? Ko kuma lafiya da girman jiki taga ya fini?"
Cikin hassala Ummy tace "Mijinta? An d'aura maka auren da ita ne? Kai bari ma na tambayeka? Ka k'addara an d'aura muku auren, kenan haka zaka mata wannan dukan tana matsayin matar taka?"
Zaro ido yayi yace "To me zan mata? D'aki zan sakata na dinga rera mata wak'a ina mata rawa dan na kwantar mata da hankali?"
Kallonshi Ummy tayi tace "In kuwa hakane lallai ba namiji bane kai, ba zaka tab'a zama jarumin namiji a gurin mace mai hankalin da tasan ciwon kanta, tun ranar da aka ce Amna ce k'addarar aurenka ta fad'a mata na fara mata kukan tausayi, dan indai har akayi kuskuren had'a ta da kai to babu makawa yarinyar nan tana daf da ajalinta."
Take yaji wasu hawaye na son taho mishi, mahaifiyarshi ce data haifeshi take fad'a masa haka? K'ok'ari yayi ya mayar da hawayen ya kalli Amna yace "Kina ji ko? A dalilinki ne take fad'a min haka, ni kuma nayi alk'awari saina tabbatar muku da namiji ne ni."
Girgiza kai Ummy tayi ta kama Amna suka mik'e tana gyara doguwar rigarta, Husseina ce da mamaki ya isheta tace "Amna kuma? Ai ba Amna bace Hamna ce, Ammar meyasa baka tsaya kayi tunani ba kawai ka hau dukanta haka?"
Dafe k'ugu yayi da hannu d'aya hannu d'aya kuma ya nuna kanshi yace "Kenan yanzu na zama mahaukaci ne da ban iya gane yaran da har goyasu nayi a bayana? Yaran da suka tashi a gaban idona ne zan kasa fahimtar wacece wannan ko wacce waccen?"
Kallonta Ummy tayi dan ta gane wacece ma a ciki, sai dai duhun dake akwai wajen bai bari ta iya ganewa ba, hakan yasa tace "Da gaske ne? Amna ce?"
Gyad'a kai tayi alamar eh, sallalami Husseina ta fara ta rik'e baki tace "Oh ni Husseina, yanzu dama Amna ce nake wa kallon Hamna? Amma meyasa dana kira Hamna kika amsa? Ita tana ina?"
Amna da har yanzu take jin marin nan daya mata da takalmi kuka kawai ta sake fashewa dashi, shi kuma k'wafa yayi ya kalleta ya nunata yace "Daga yanzu duk inda zaki je saina baki izini indai har nine wanda zai aure ki." wucewa yayi inda Ummy ta bishi da kallo ganin jikinshi biji-biji ga kayanshi sai k'yallin mai suke, kama Amna tayi suka shiga ciki bata yarda sun tsaya falon ba, sama suka haura d'akin su suka zaunar da ita, fad'a Ummy keyi sosai na haushi da takaici, har da cewa "To ubanki ne shi da har zaki tsaya ya miki wannan dukan? Ba dan kin zama sakarya ba ma akan me zakiyi tsaye yana d'irkarki haka? Amna aure fa ake shirin yi miki dashi, da hakane zaku zauna kinsa tsoronsa a ranki? Na tabbata da yer uwarki ce Hamna wallahi ko gudu ne tayi daga gurinshi, dan baya da maraba da mahaukaci idan ranshi ya b'ace."
Amna dai shiru tayi sai sharar hawaye take, hakan yasa Ummy cewa "Kiji harda wani cewa wai in zaki fita saida izininshi, to mu duk aikin banza ne kenan a gidan? To zaki fita bada izinin nashi ba sai naga in kasheki zaiyi."
D'agowa Amna tayi cikin kuka tace "A'a Ummy, tunda dai yace haka ni zan bi umarninshi, zan nemi izininshi kafin na fita, shikenan sai a zauna lafiya, ko Mama ma tana fad'a mana mu dinga jin maganarshi dan shi kad'ai ne ke tsawatar mana."
Da mamaki Ummy tace "Ke yanzu sai ki biye masa kuma?"
Jinjina kai tayi alamar eh tare da cewa "Ummy hakan shine zaman lafiya na, nasan ni ba yer uwata Hamna bace, nice mafad'aciyar kuma mai zuciyar, amma akan yah Ammar bana da ko d'aya, bansan meyasa ba."
Tab'e baki Ummy tayi tace "Lallai kina da aiki Amna."
Ko da yayi wanka shiryawa yayi cikin riga da wando bak'ak'e, makullin mota ya d'auka ya sake fita, k'aramin gurin cin abinci ne *Kebab* ya zauna ya ci abinci, daga nan kuma hanya ya d'auka saida ya samu inda babu hayaniya ya paka nan, jingina kawai yayi yana sauraron wa'azindake tashi a motar, maganganun Ummy ne kawai ke dawo masa a k'wak'walwa, awa d'aya da rabi ya d'auka a wurin nan kamar mai bacci kafin wayarshi ta fara ruri, saida kiran ya tsinke aka sake maidowa kad'ai ya taso daga kwanciyar da yayi ya d'auki wayar, a zuciyarshi yace "Abdullahi kuma? Meyasa zai kirani a wannan lokacin?"
Tsaki yayi saboda wata zuciyar data fad'a masa watak'ila zai maka k'orafine saboda baka je d'aukar amarya ba, d'auka yayi ya d'ora a kunne yayi shiru, daga can b'angaren Abdullahi yace "Ammar yane? Kana cikin gari ko kana gida?"
Can k'asan mak'oshi yace "Lafiya?"
Abdullahi ne yace "Lafiya ba lafiya, dama a cikin yan matan amarya ne aka bar wasu basu samu komawa tare da sauran mutane ba, kuma gashi duk wanda na kira wallahi wasu ma sun fad'a min kai tsaye ba zasu iya dawowa d'aukar su, ni ma kuma mota ta tun safe tana hannun k'ane na, yanzu haka nafi awa d'aya ina jiran adaidaita sahu ko taxi na samar musu amma wallahi shiru, gashi dare na k'arayi shiyasa nace bara na kiraka dan Allah ka zo ko Hamna ka d'auka, tunda kaga gidanku ba bari fitar dare ake yi ba inba da dalili mai..."
Ammar ne ya dakatar dashi cikin sanyayyar murya yace "Ya isa haka dan Allah, magana ba tsayawa ba numfasawa, yanzu kenan nufinka naje na zama drebata na d'auko ta? Bayan kuma a gida babu wanda ma yasan da fitarta, to ba zan iya ba."
Abdullahi ne yace "Dan Allah Ammar ka taimaka, bana so ne ta shiga matsala a dalilin halartar bikin nan nawa, dan Allah."