Sashe 92
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_26_
Kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "Fita zanyi yanzu, zaki sha kankana ne na taho miki da ita?"
Sama da k'asa ta harareshi taja dogon tsaki ta wuce d'aki, ba tare daya daina murmushin ba ya bita da kallon *zaki gane kurenki*, Hadiza ce ta juyo ta bita da kallo tace "Ke Hamna lafiyarki kuwa? Meye na tsakin daga abun arzik'i? Bana son iskanci kinji na fad'a miki, wannan ba yayanki bane? Ko dan kinga yau ya sakar muku fuska ne."
Mik'ewa yayi tsaye yana gyara zaman doguwar rigarshi yana fad'in "Tanti ni zan fita na dawo."
Kallonshi tayi cike da kulawa tace "A'a, ka zauna mana ka ci abinci saika fita, nasan dai yanzu bakin ruwa zaka je ko?"
Murmushi kawai ya mata ya nufi k'ofar fita, da kallo ta bishi a ranta tana mamakin wani sauyi data gani a tare da shi tana fad'in "Yau Ammar babu saurin kai duka, har Hamna ta mishi tsaki amma ya nuna ko a jikinshi, lallai yau farar juma'a ce, ba dan haka ba ai da sai dai ta jiyo ihunta a d'akin."
Wata zuciyar ta fad'a mata "Dama ai yau da gobe sai Allah, mutum yana canzawa kamar yanda zamani ke canzawa."
Ba tare data daina kallonshi ba tace "Ko kuma dai dan za'a had'a shi da Amna ne, tabbas ma hakane, watak'ila kunyarta yake ji yanzu saboda sun zama surukai."
Bata gushe daga tunanin ba taji muryarshi cikin d'aga murya yana fad'in "Mutumin ya kake?"
Da kallo ta bisu ganin shi da mai gidan nata suna gaisuwa irinta yaran zamani marasa jin magana, murmushi kawai take saboda yanda suka birgeta kamar wani d'a da uba, dawowa sukayi ciki har cikin runfar inda Shu'aibu ya kama hancin Hadiza yaja sosai yana mik'a mata sallayar hannunshi yana fad'in "Matanmu ya aiki? Ashe bak'i kikayi bayan tafiyata?"
Hadiza data saba take kuma jin dad'in zama da mijin nata murmushi ta masa tace "Sannu da zuwa, bak'i kuma ba bak'i ba kam."
Ammar da soyayyar dattawan ke birgeshi sagala hannunshi yayi a kafad'ar Shu'aibu ya ja hancinshi yana fad'in "Duk ka jaye mana hanci uwa har yayi tsayi kamar karas, ka canza wani salo mana."
Shima kama wuyanshi yayi suna dariya yace "Uwar ka dai ce ka shammata bani ba ja'iri kawai, kuma ma wani salo zan canza bayan na saba da wannan."
Kashe mishi ido d'aya yayi yace "Muje waje zan fad'a maka irin wanda zaka sauya."
Hararan wasa Shu'aibu ya masa yace "Me yasa sai mun fita? A sani na dai baka jin kunyar fad'an komai ko a gaban wa."
D'ora kanshi yayi a kafad'ar Shu'aibu tare da jawo rigarshi yana rufe ido wai kunya🙄🤔 (bala'i, ban tab'a gani ba), cikin nuna jin kunya yace "Nima bansan ya akayi ba yau na ji na sauya, kawai dai muje waje na fad'a maka sabon yayi."
Ture shi Shu'aibu yayi daga jikinshi ya kalli Hadiza da banda dariya da girgiza kai babu abinda take yace "Wai ina yan biyuna ne ikon Allah? Amma dai banda Hamna aka zo ko?"
Hadiza ce tace "Har da ita ko, yau dai matsiyata ne bisa kanta shiyasa, dan da farko data shigo ma kuka ta saka mana, duk ta canza dai tayi wata iri."
Daga cikin d'akin cikin taushin murya Amna "Kawu ina wuni."
Cikin sakin fuska ya amsa da "Lafiya lau yan biyu ikon Allah, amma wace tayi magana? Kinsan ban cika gane ku ba har yanzu."
Amna ce tayi dariya zatayi magana Ammar yace mishi "Ba kankanar bace, d'ayar ce."
Kallonshi Shu'aibu yayi yace "Kai kam dama ai ko mahaifiyarsu ba zata nuna maka saninsu ba, Allah ya maka wannan baiwar tun haihuwarsu."
Murmushin jin dad'i yayi ya shafo gemunshi yace "Da wayona fa akayi auren Tanti da Tonton, sannan tare da ni tanti ta ci amarcinta, tare dani tayi laulayin cikinsu, hasalima ni nake shafa cikinta ina fad'a mata zata haifi yan biyu kamar ni da d'an uwa na, sannan a idona ta fara nak'udarsu ni ne ma na kira mutanen gida aka kaita asibi, tare dani akayi jegonsu, sannan tare da ni Ummy ta rainesu har sukayi wayo, to ni kam meye zai shige min duhu a tare dasu?"
Duk da Shu'aibu ya ji kishi a zuciyarshi lokacin da Ammar yace sun ci amarci, amma kuma bai nuna ba ko a fuska sai darewa da yayi yace "Gaskiyar kam, amma yanzu dai bari na gano kankanar ta bakinka."
Zai shiga d'akin Ammar ya rik'o hannunshi yace "Muje waje haba muyi hira, rabu da kankana nasan matsalarta."
Daga d'aki Amna tace "Kawu sallah ma take."
"Shiyasa dai banji muryarta ba ashe." Cewar Shu'aibu kafin ya kalli Hadiza yace "Idan kin gama abincin ki aiko mana shi k'ofar gida, wannan sarkin zancen ba zai barni na gama kallonki ba."
Dariyar shak'iyanci yasa suka nufi waje yana fad'in "Ai mutumina shiyasa nake so muje waje na k'ara baka wasu shawarwarin yanda zaka ci gaba da kula mana da tantinmu, dan naga ba tsufa kuke ba ku, shiyasa nake so naga kullum kana nan a jaruminka kana bada wuta a ciki."
Shu'aibu dariya yayi yace "Cikin me?"
Sunkuyar da kai yayi yace "Kai ma dai har saina fad'a? Ka sani mana."
Shu'aibu ne ya d'auki tabarma suka fita, suna zuwa ya shinfid'a a k'ark'ashin bishiyar dake k'ofar gidan tare da wata k'atuwar darduma suka zauna, a cikin gida kuma Hadiza k'walla kiran Amna tayi tana fitowa tace ta d'auki abinci ta kai musu, cikin ladabi ta d'auka har da ruwa ta kai musu.
*Gaga's House*😍
Hankalin Ummy ne ya fara tashi ganin babu Hamna kuma babu Amna, wayarta ta fara kira amma abun mamaki saita samu wayar a d'akinta, alama dai wahalar da tasha tasa ta manta da wayar ma a d'akinta, Amna ta koma kira ita kuma kashe wayar dan tunda zasu shiga aji ta kashe oga boss kuma yasa ta manta bata kunna ba, saida rana tayi sosai lokacin su Hamna na cin abinci ta d'auki wayar ta kunna, ganin kiran da Ummy tayi bata samu ba yasa ta mayar da kira, da sauri Ummy ta d'auka tana fad'in "Amna, lafiyarku k'alau kuwa? Ina kuka tsaya ne haka?"
Da murmushi a fuskarta tace "Ummy kiyi hak'uri banga kiranki ba sai yanzu na kunna wayar, wallahi muna lafiya lau babu komai."
"To kuna ina har yanzu baku zo gida ba?" Ta fad'a cike da k'aguwa, kallon Hamna tayi da ita ma ke kallonta tace "Ummy gamu nan gida wajen Mama."
Da k'arfi Ummy ta zaro ido tace "Me? Mamanku? Ke da wa?"
Jin yanda Ummy ta rud'e yasa tayi dariya tace "Ummy kwantar da hankalinki, yah Ammar ne ya kawo mu tare da Hamna muke."
Da sauri cike da tsoron abinda Hamna zata fad'awa mahaifiyarta Ummy tace "Ina Hamnar take? Bani ita."
Mik'awa Hamna wayar tayi ta ci gaba da cin abincinta Hamna kuma ta amsa da "Ummy lafiya lau muke fa."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Hamna ina cikin damuwa sosai, kar Hadiza ta fahimci wani abu ya faru dake, dan Allah ku dawo yanzu Hamna kafin Hajia ta ankare da rashin dawowarku, kinsan a kaina k'urar zata sauka tace da sani na kuka tafi babu izininta."
Cikin rashin karsashi Hamna tace "Ummy wallahi ba laifinmu bane, kawai muna fitowa daga makaranta ya zo ya d'auke mu da k'arfi."
Cikin rashin kulawa Ummy tace "Ni ban damu da lamarinshi ba, ko da kun dawo ma yasan yanda zaiyi ya fitar da kanshi wajen Hajia ko kuma ya sake tsula mata wata tsiyar, ku kawai nake ji Hamna, dan Allah ku k'ok'arta ku dawo kafin sallah la'asar, kunga gida anata hidima kuma ana tambayar ina kuke."
Cikin sanyin murya tace "Ummy yanzu ba zamu iya kwana a nan ba? Mun jima fa rabonmu da nan."
Da sauri tace "A'a Hamna rufa min asiri dan Allah, ni dai na rok'eku ku dawo yanzu kinji, inba haka ba ni zan zo garin na taho da ku, Hamna ko kin manta kina buk'atar kulawa ne?"
Turo baki tayi kamar tana gabanta tace "Shikenan Ummy zamu dawo."
Murmushi tayi mai sauti tana fad'in "Yawwa yar albarka, sai kun zo kinji, ina maman taku ne?"
"Tana waje." Cewar Hamna a dak'ile kafin Ummy tace "Bani ita mu gaisa."
"To." Ta fad'a tare da mik'awa Amna wayar tace "Kaiwa Mama."
Figar wayar tayi tana dalla mata harara da fad'in "Ke musaka ce da ba zaki iya tashi ba ko me?"
K'ala ba tace mata ba har ta fice ta kaiwa Mamansu wayar, sosai suka gaisa inda Hadiza take sake godewa Ummy kan kula mata da yaranta da take, sannan ta d'ora da "Munji kuma abun alkairi had'in da Hajia tayi, Allah ubangiji yasa alkairi yasa ayi muna raye."
Ummy ce ta amsa da "Ameen, insha Allahu ma ai zan zo ko dan muyi magana da shirye shiryen abinda ya kamata na bikin, ina jira ne a gama wannan sabgar lokacin an kawo komai da komai sai na zo."
Ita ma Hadiza murmushi tayi tace "Sa'ada kenan, ai ke ce uwar yaran nan, duk abinda kikayi wallahi d'aya ne, babu abinda zan ce muku ke da lieutenant ai sai godiya."
"Ba komai wallahi yiwa kaine ai." Da haka sukayi sallama ta mayarwa da Amna wayar d'aki wanda ta same su suna rigima Hamna ta dage sai Amna taje waje ta fad'awa Ammar Ummy tace su tafi, ita kuma tace ba zata ba salon ya mata rashin mutumci, dariya Hadiza tayi tace "To ke da zai aureki kina shakkar yi masa magana tun yanzu, ya kenan idan anyi auren?"
Hamna ce tace "Sai ya raina ta mana ya juyata yanda ya ga dama."
Hararanta tayi tace "To ina ruwanki idan ya juya nin? Ai ba ke ya juya ba ko? Kuma dama haka ake so mace ta zama k'asan mijinta."
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_26_
Kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "Fita zanyi yanzu, zaki sha kankana ne na taho miki da ita?"
Sama da k'asa ta harareshi taja dogon tsaki ta wuce d'aki, ba tare daya daina murmushin ba ya bita da kallon *zaki gane kurenki*, Hadiza ce ta juyo ta bita da kallo tace "Ke Hamna lafiyarki kuwa? Meye na tsakin daga abun arzik'i? Bana son iskanci kinji na fad'a miki, wannan ba yayanki bane? Ko dan kinga yau ya sakar muku fuska ne."
Mik'ewa yayi tsaye yana gyara zaman doguwar rigarshi yana fad'in "Tanti ni zan fita na dawo."
Kallonshi tayi cike da kulawa tace "A'a, ka zauna mana ka ci abinci saika fita, nasan dai yanzu bakin ruwa zaka je ko?"
Murmushi kawai ya mata ya nufi k'ofar fita, da kallo ta bishi a ranta tana mamakin wani sauyi data gani a tare da shi tana fad'in "Yau Ammar babu saurin kai duka, har Hamna ta mishi tsaki amma ya nuna ko a jikinshi, lallai yau farar juma'a ce, ba dan haka ba ai da sai dai ta jiyo ihunta a d'akin."
Wata zuciyar ta fad'a mata "Dama ai yau da gobe sai Allah, mutum yana canzawa kamar yanda zamani ke canzawa."
Ba tare data daina kallonshi ba tace "Ko kuma dai dan za'a had'a shi da Amna ne, tabbas ma hakane, watak'ila kunyarta yake ji yanzu saboda sun zama surukai."
Bata gushe daga tunanin ba taji muryarshi cikin d'aga murya yana fad'in "Mutumin ya kake?"
Da kallo ta bisu ganin shi da mai gidan nata suna gaisuwa irinta yaran zamani marasa jin magana, murmushi kawai take saboda yanda suka birgeta kamar wani d'a da uba, dawowa sukayi ciki har cikin runfar inda Shu'aibu ya kama hancin Hadiza yaja sosai yana mik'a mata sallayar hannunshi yana fad'in "Matanmu ya aiki? Ashe bak'i kikayi bayan tafiyata?"
Hadiza data saba take kuma jin dad'in zama da mijin nata murmushi ta masa tace "Sannu da zuwa, bak'i kuma ba bak'i ba kam."
Ammar da soyayyar dattawan ke birgeshi sagala hannunshi yayi a kafad'ar Shu'aibu ya ja hancinshi yana fad'in "Duk ka jaye mana hanci uwa har yayi tsayi kamar karas, ka canza wani salo mana."
Shima kama wuyanshi yayi suna dariya yace "Uwar ka dai ce ka shammata bani ba ja'iri kawai, kuma ma wani salo zan canza bayan na saba da wannan."
Kashe mishi ido d'aya yayi yace "Muje waje zan fad'a maka irin wanda zaka sauya."
Hararan wasa Shu'aibu ya masa yace "Me yasa sai mun fita? A sani na dai baka jin kunyar fad'an komai ko a gaban wa."
D'ora kanshi yayi a kafad'ar Shu'aibu tare da jawo rigarshi yana rufe ido wai kunya🙄🤔 (bala'i, ban tab'a gani ba), cikin nuna jin kunya yace "Nima bansan ya akayi ba yau na ji na sauya, kawai dai muje waje na fad'a maka sabon yayi."
Ture shi Shu'aibu yayi daga jikinshi ya kalli Hadiza da banda dariya da girgiza kai babu abinda take yace "Wai ina yan biyuna ne ikon Allah? Amma dai banda Hamna aka zo ko?"
Hadiza ce tace "Har da ita ko, yau dai matsiyata ne bisa kanta shiyasa, dan da farko data shigo ma kuka ta saka mana, duk ta canza dai tayi wata iri."
Daga cikin d'akin cikin taushin murya Amna "Kawu ina wuni."
Cikin sakin fuska ya amsa da "Lafiya lau yan biyu ikon Allah, amma wace tayi magana? Kinsan ban cika gane ku ba har yanzu."
Amna ce tayi dariya zatayi magana Ammar yace mishi "Ba kankanar bace, d'ayar ce."
Kallonshi Shu'aibu yayi yace "Kai kam dama ai ko mahaifiyarsu ba zata nuna maka saninsu ba, Allah ya maka wannan baiwar tun haihuwarsu."
Murmushin jin dad'i yayi ya shafo gemunshi yace "Da wayona fa akayi auren Tanti da Tonton, sannan tare da ni tanti ta ci amarcinta, tare dani tayi laulayin cikinsu, hasalima ni nake shafa cikinta ina fad'a mata zata haifi yan biyu kamar ni da d'an uwa na, sannan a idona ta fara nak'udarsu ni ne ma na kira mutanen gida aka kaita asibi, tare dani akayi jegonsu, sannan tare da ni Ummy ta rainesu har sukayi wayo, to ni kam meye zai shige min duhu a tare dasu?"
Duk da Shu'aibu ya ji kishi a zuciyarshi lokacin da Ammar yace sun ci amarci, amma kuma bai nuna ba ko a fuska sai darewa da yayi yace "Gaskiyar kam, amma yanzu dai bari na gano kankanar ta bakinka."
Zai shiga d'akin Ammar ya rik'o hannunshi yace "Muje waje haba muyi hira, rabu da kankana nasan matsalarta."
Daga d'aki Amna tace "Kawu sallah ma take."
"Shiyasa dai banji muryarta ba ashe." Cewar Shu'aibu kafin ya kalli Hadiza yace "Idan kin gama abincin ki aiko mana shi k'ofar gida, wannan sarkin zancen ba zai barni na gama kallonki ba."
Dariyar shak'iyanci yasa suka nufi waje yana fad'in "Ai mutumina shiyasa nake so muje waje na k'ara baka wasu shawarwarin yanda zaka ci gaba da kula mana da tantinmu, dan naga ba tsufa kuke ba ku, shiyasa nake so naga kullum kana nan a jaruminka kana bada wuta a ciki."
Shu'aibu dariya yayi yace "Cikin me?"
Sunkuyar da kai yayi yace "Kai ma dai har saina fad'a? Ka sani mana."
Shu'aibu ne ya d'auki tabarma suka fita, suna zuwa ya shinfid'a a k'ark'ashin bishiyar dake k'ofar gidan tare da wata k'atuwar darduma suka zauna, a cikin gida kuma Hadiza k'walla kiran Amna tayi tana fitowa tace ta d'auki abinci ta kai musu, cikin ladabi ta d'auka har da ruwa ta kai musu.
*Gaga's House*😍
Hankalin Ummy ne ya fara tashi ganin babu Hamna kuma babu Amna, wayarta ta fara kira amma abun mamaki saita samu wayar a d'akinta, alama dai wahalar da tasha tasa ta manta da wayar ma a d'akinta, Amna ta koma kira ita kuma kashe wayar dan tunda zasu shiga aji ta kashe oga boss kuma yasa ta manta bata kunna ba, saida rana tayi sosai lokacin su Hamna na cin abinci ta d'auki wayar ta kunna, ganin kiran da Ummy tayi bata samu ba yasa ta mayar da kira, da sauri Ummy ta d'auka tana fad'in "Amna, lafiyarku k'alau kuwa? Ina kuka tsaya ne haka?"
Da murmushi a fuskarta tace "Ummy kiyi hak'uri banga kiranki ba sai yanzu na kunna wayar, wallahi muna lafiya lau babu komai."
"To kuna ina har yanzu baku zo gida ba?" Ta fad'a cike da k'aguwa, kallon Hamna tayi da ita ma ke kallonta tace "Ummy gamu nan gida wajen Mama."
Da k'arfi Ummy ta zaro ido tace "Me? Mamanku? Ke da wa?"
Jin yanda Ummy ta rud'e yasa tayi dariya tace "Ummy kwantar da hankalinki, yah Ammar ne ya kawo mu tare da Hamna muke."
Da sauri cike da tsoron abinda Hamna zata fad'awa mahaifiyarta Ummy tace "Ina Hamnar take? Bani ita."
Mik'awa Hamna wayar tayi ta ci gaba da cin abincinta Hamna kuma ta amsa da "Ummy lafiya lau muke fa."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Hamna ina cikin damuwa sosai, kar Hadiza ta fahimci wani abu ya faru dake, dan Allah ku dawo yanzu Hamna kafin Hajia ta ankare da rashin dawowarku, kinsan a kaina k'urar zata sauka tace da sani na kuka tafi babu izininta."
Cikin rashin karsashi Hamna tace "Ummy wallahi ba laifinmu bane, kawai muna fitowa daga makaranta ya zo ya d'auke mu da k'arfi."
Cikin rashin kulawa Ummy tace "Ni ban damu da lamarinshi ba, ko da kun dawo ma yasan yanda zaiyi ya fitar da kanshi wajen Hajia ko kuma ya sake tsula mata wata tsiyar, ku kawai nake ji Hamna, dan Allah ku k'ok'arta ku dawo kafin sallah la'asar, kunga gida anata hidima kuma ana tambayar ina kuke."
Cikin sanyin murya tace "Ummy yanzu ba zamu iya kwana a nan ba? Mun jima fa rabonmu da nan."
Da sauri tace "A'a Hamna rufa min asiri dan Allah, ni dai na rok'eku ku dawo yanzu kinji, inba haka ba ni zan zo garin na taho da ku, Hamna ko kin manta kina buk'atar kulawa ne?"
Turo baki tayi kamar tana gabanta tace "Shikenan Ummy zamu dawo."
Murmushi tayi mai sauti tana fad'in "Yawwa yar albarka, sai kun zo kinji, ina maman taku ne?"
"Tana waje." Cewar Hamna a dak'ile kafin Ummy tace "Bani ita mu gaisa."
"To." Ta fad'a tare da mik'awa Amna wayar tace "Kaiwa Mama."
Figar wayar tayi tana dalla mata harara da fad'in "Ke musaka ce da ba zaki iya tashi ba ko me?"
K'ala ba tace mata ba har ta fice ta kaiwa Mamansu wayar, sosai suka gaisa inda Hadiza take sake godewa Ummy kan kula mata da yaranta da take, sannan ta d'ora da "Munji kuma abun alkairi had'in da Hajia tayi, Allah ubangiji yasa alkairi yasa ayi muna raye."
Ummy ce ta amsa da "Ameen, insha Allahu ma ai zan zo ko dan muyi magana da shirye shiryen abinda ya kamata na bikin, ina jira ne a gama wannan sabgar lokacin an kawo komai da komai sai na zo."
Ita ma Hadiza murmushi tayi tace "Sa'ada kenan, ai ke ce uwar yaran nan, duk abinda kikayi wallahi d'aya ne, babu abinda zan ce muku ke da lieutenant ai sai godiya."
"Ba komai wallahi yiwa kaine ai." Da haka sukayi sallama ta mayarwa da Amna wayar d'aki wanda ta same su suna rigima Hamna ta dage sai Amna taje waje ta fad'awa Ammar Ummy tace su tafi, ita kuma tace ba zata ba salon ya mata rashin mutumci, dariya Hadiza tayi tace "To ke da zai aureki kina shakkar yi masa magana tun yanzu, ya kenan idan anyi auren?"
Hamna ce tace "Sai ya raina ta mana ya juyata yanda ya ga dama."
Hararanta tayi tace "To ina ruwanki idan ya juya nin? Ai ba ke ya juya ba ko? Kuma dama haka ake so mace ta zama k'asan mijinta."