Sashe 123
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Juyawa yayi ya fita ta bishi da murmushi Allah ya bada sa'a, tun a hanya yake k'ulla kalar k'aunar da zai nuna masa, to wai a kan me zata fad'a masa baya k'aunar d'an shi, ko bata san shine sanyin idaniyarshi na farko bane? Bata san duk suna mishi abinda suke mishi ne ba dan suna son ya gyaru ya zama na k'warai? Ta manta da duk fafutukar da yake saboda 'ya'yanshi yake yinta sannan Ammar shine magajinshi na farko? Me yasa bata tambaye shi me yaji ba a sanda aka fad'a mishi an rufe mishi? Amma ba komai zai nuna mata ba haka bane abinda take cewa ta ganin, da wannan tunanin ya isa ya baka tsandareriyar motar data sanar da jami'an babban mutum ya shigo, sanin sosai suka masa ba sanin shanu ba, dan haka suka sara masa cikin girmamawa ya shiga ciki, ikon Allah sai kallo, ganinshi hankali kwance matarshi na ciyar dashi cikin nishad'i, abinda ya aikata ya cancanta ya bibbige shi amma ba hali, k'wafa kawai yayi ya shiga inda zai samu belinshi. Cikin mutuntawa aka fad'a mishi ai Amar ya biya tarar kawai zasu iya tafiya, amma gobe da safe saiya dawo a musu sulhu saboda gaba, duk da haka saida ta d'ebo kud'in da baisan ko nawa bane ya zube kan teburin kafin suka fito, sai lokacin ne suka ga lieutenant, hannu ya d'aga masa yace "Abbana barka da dare, har ka iso?"
Tasowa yayi daga bencin kamar k'aramin yaro sai kawai ya rumgume shi yana wani k'amk'ame shi da kwantawa kan k'irjinshi yana fad'in "Nasan kana min son da baka ma kowa Abba, dama nasan zaka zo, ba zaka iya bacci a gidan can ba idan bana gidan nan, ko ba haka ba?"
Abun yafi k'arfin tunanin lieutenant, sai kawai ya tsinci kansa ya rumgume shi shima har da shafa kansa yana murmushin da baisan ko na miye ba yace "Gaskiya ne, ai indai har zaka kwana a nan to sai dai in gaba d'aya ahalin Gaga ne suka tare a wurin nan."
D'ago kai yayi ya kalleshi ba tare daya d'aga daga k'irjinshi ba, turo baki yayi gaba irin tunda na samu ka biye min to bari na yi abinda na jima ina kewarshi daga gareku, sai k'ara narkewa yake jikinshi kamar zai shige cikinshi, Amna dake kallon ikon Allah tashi tayi ta wanke hannunta ta had'a kayan, kallonta lieutenant yayi yace "Shikenan 'yata sai ki taho wurin mijinki baki sanar da kowa ba."
Murmushi kawai tayi kafin lieutenant ya d'agoshi daga jikinshi yace "To mu tafi ko?"
Kafad'a ya d'aga alamar a'a kamar yaron goye, kallon zan ci ubanka a wurin nan lieutenant ya mishi tare da cewa "Meye kuma?"
Cike da shagwab'a yace "Sai kace muje shalele."
Anya yaron nan banda aljanu kuwa? Tambayar da lieutenant ya ma kanshi kenan, wato dan ya ga ya zo shine saiya mishi iskanci yasa ranshi ya b'ace har ya kasa yin abinda ya fad'a, daga Ammar d'in har Amna kallonshi suke suna jiran suji me zaice, rarraba ido yake ganin jami'in dake tare dasu ne kawai yasa yayi murmushi yace "To muje shalele."
Dariya yayi ya rik'e hannun lieutenant da kuma hannun Amna suka rankaya yana fad'in "Daga yanzu ni ma na zama shalelenka, kaga Amar shalelen Hajia ne ni kuma na ka ko Abba?"
"Umm." Kawai ya fad'a ba tare da yace komai ba, kallonshi lieutenant yayi yace "Motarka fa?"
Saida ya bud'a ta lieutenant ya shiga ya hakimce sannan yace "Tare da Abbana zan tafi, gobe na dawo na d'auka daga nan nima saina shigar da k'arar wannan banzan."
Shiga sukayi duka Amna na baya yace "K'arar me kuma?" Saida ya kalleshi yace "Abba k'azafi ya min wai ina saka kayan soja, har da cewa wai ina da bindiga."
Kallonshi lieutenant yayi irin kallon nan na anya Ammar ba gaskiya bane kuwa, saida ya tayar da motar suka d'auki hanya kafin yace "Ka daina shiga rigima Ammar, bana jin dad'in haka fa, wai kai baka san ka girma bane?"
"Zan daina Abba, dana gama da wannan yaron shikenan." Ya fad'a yana kallon titi, *meye nufinshi akan Jano ne? Ni dai nasan da abinda yake so dashi*, suna zuwa gida suka fito a mota suka nufi hanyar da zata sadasu da b'angarensu, dole ta inda lieutenant ya paka mota indai zasu wuce sai sun bi ta k'ofar shiga falon Hajia, hakanne yasa Ammar hangota zaune kan kujerar mulki, murmushi yayi ya tunkari shiga ciki, rik'oshi lieutenant yayi yace "Ina zaka kuma? Wuce ka bi matarka."
Langab'e kai yayi yace "Abba Hajia zai gaida duk yau bamu had'u ba duk bana jin dad'i."
Wani kallo ya masa yace "Ammar uwata ce fa, karka ja min zagi yanzu a daren nan mana."
"Allah Abba ba zan sa ba, nayi alk'awari." Yana fad'a ya shiga ciki da sallama, Amna kam da take jin haushin tura mata yer uwarta wani wuri bata shiga ba sai na su b'angaren data nufa. Yana zuwa kamar an tura shi ya durfafeta ya rumgume tare da sumbatar goshinta yana fad'in "Hajiata ikon Allah, wallahi duk nayi kewarki wunin nan kawai da ban ganki ba."
Tareshi tayi daga jikinta tana goge goshinta da fad'in "Kai rabu dani dallah, wai kai baka da lafiya ne?"
Kallonta yayi ya dafa saitin zuciyarshi yace " Yanzu ne kawai na fara jin na samu lafiya da nayi tozali dake."
Da k'arfi ya sake fizgo fuskarta ya sumbaceta a kumatu yana fad'in "Ina sonki, saida safe, karki bari kishina ya hanaki bacci."
Saida ta marmad'a ido saboda yanda ya fincikota, da kallo ta bishi tana mamakin halin wannan k'waya d'aya tak dake saka mata hawan jini, yanda ta kafe k'ofar da ido har ya b'ace ma ganinta sai kawai taji tana murmushi, kamar an tsikareta sai kuma taja tsaki tana fad'in "Mahaukaci."
*Capital*
Baccin marar dad'i har ya fara d'aukarta d'aya daga cikin ma'aikatan gidan ta shigo ta kirata, fitowa tayi jiki a sanyaye ta zo ta tsaya gabanta kamar yanda ita ma take tsaye, kasa d'aga kai tayi ta kalleta saboda tun tana tahowa taga kayan bacci ne jikinta masu shegen kyau da d'aukar ido, kamar saukar aradu ta kashe ta da mari tare da mata tsawa tace "Idiot, ina tsaye shine ke ma zaki tsaya min a kai haka."
Dafe kumci tayi ta bud'e baki ta kalleta tace "Kika mare ni?"
D'aga hannu ta sakeyi zata sake marinta tayi baya da k'arfi tana fad'in "A'a wallahi, ko uwata ban rayu da ita ba ta yanda zan iya fad'a miki ranar data d'aga hannunta a kaina, dan haka ya tsaya nan gaskiya."
Cike da iko tace "Ni kike fad'awa haka? To bari kiga abinda zanyi, ubanki zan fad'a ma ya sanar dake k'arfin ikona, idan ya fad'a miki da kanshi zaki fi ji da kyau."
Juyawa ta shiga ta wata k'ofa da zata sadata da d'akin baccinshi, tab'e baki Hamna tayi ta juya ta koma ni'imtaccen d'akinta ta kwanta, amma abun takaici sai ga mahaifinta cikin jallabiya tare da matarshi sai wani rirrik'eshi take tana kukan munafurci, bata san me ta fad'a mishi ba? Bata san meya faru ba kawai saiya rufe ta da fad'a kamar saukar ruwan sama, saida ya gama sannan ya jaddada mata duk abinda Aissata ta sakata tayi ko bata so dan ita ce mai gidan nan, sannan idan ta mata musu Allah ya isa bai yafe mata ba, juyawa yayi suka fita sai kawai ta fashe da kuka, duk rashin kirkin Hajia suna sakata su wala, babu takura babu matsi sai in ka taka mata doka, amma nan, lallai ma.
To fa hakan data faru ne yasa washe gari da safe ta kirata, tana zuwa tace "D'aki na zaki gyara min ki min shinfid'a, idan kin gama ki wanke ban d'aki da kyau sannan kiyi turare, idan kin gama sai ki zo na fad'a miki aiki na gaba da zaki min."
Hararanta ta farayi sama da k'asa kafin daga bisani ta tuna kalmar Allah ya isa da mahaifinta ya fad'a mata, cikin ladabi tace "To." Ta juya ta shiga d'akin, duk ni'imar duniya ta taru a d'akin nan, kud'i ko nace kayan kud'i kamar zasuyi magana da baki tsabar yanda aka tarwatsa su, komai na kud'i ne d'aruruwa ko milyoyi, gyarawa tayi ta share ta wanke har ban d'akin ta goge komai sannan tayi turare, kama daga na ruwa na tsintsiya har na wuta, hakan yasa d'akin k'ara sanyaya da sanyin k'amshi, tana idarwa ta fito ta fad'a mata, ki shiga madafa ki samu *Betrice* ta baki jadawalin duk abinda nake ci da kuma lokacin da nake cin shi, daga yanzu ke ce mai wannan alhakin."
Yawu ta had'e ba tace komai ba kawai ta wuce madafar, tana zuwa ta fara fad'a mata "07:30 zaki kai mata lipton a d'akinta, 08:00 zaki kai mata ruwa da matsatsun kayan itatuwa a d'akin motsa jiki, k'arfe 09:00 daidai zaki shirya mata petit déjeuner (karin kumallo) a kan table, da k'arfe..."
Hannu ta d'aga mata tana yatsina fuska tace "Dakata dan Allah, ki samu takarda ki rubata min zan duba daga baya, bana da lokacin wannan shashancin."
Yana fad'a ta barta nan tsaye tana kallonta, kamar yanda ta buk'ata haka ta ruba ta mata komai ta kai mata, daga wannan lokacin ta fara aiki dan matar muguwar yar tamne-tamne ce bata gajiya da had'id'iya, bata awa d'aya bata buk'aci wani abu ba, ko ba komai taji dad'i daya zama ita ce a gidan ba Amna ba, dan da ita ce to tana iya yin zuciya ta bar gidan sai kawai an ganta ta koma Maradi, sai dai Allah ya isar ta bita kam amma ba zata d'auka ba, da wannan yau ta kwanta baccin gajiya saboda bata huta ba ko kad'an sai kai da kawowa, abunka ga gidan gwamnati ga girma daga wani wurin zuwa wani tafiya ce mai tsayi.
*Gaga's house*
Tasowa yayi daga bencin kamar k'aramin yaro sai kawai ya rumgume shi yana wani k'amk'ame shi da kwantawa kan k'irjinshi yana fad'in "Nasan kana min son da baka ma kowa Abba, dama nasan zaka zo, ba zaka iya bacci a gidan can ba idan bana gidan nan, ko ba haka ba?"
Abun yafi k'arfin tunanin lieutenant, sai kawai ya tsinci kansa ya rumgume shi shima har da shafa kansa yana murmushin da baisan ko na miye ba yace "Gaskiya ne, ai indai har zaka kwana a nan to sai dai in gaba d'aya ahalin Gaga ne suka tare a wurin nan."
D'ago kai yayi ya kalleshi ba tare daya d'aga daga k'irjinshi ba, turo baki yayi gaba irin tunda na samu ka biye min to bari na yi abinda na jima ina kewarshi daga gareku, sai k'ara narkewa yake jikinshi kamar zai shige cikinshi, Amna dake kallon ikon Allah tashi tayi ta wanke hannunta ta had'a kayan, kallonta lieutenant yayi yace "Shikenan 'yata sai ki taho wurin mijinki baki sanar da kowa ba."
Murmushi kawai tayi kafin lieutenant ya d'agoshi daga jikinshi yace "To mu tafi ko?"
Kafad'a ya d'aga alamar a'a kamar yaron goye, kallon zan ci ubanka a wurin nan lieutenant ya mishi tare da cewa "Meye kuma?"
Cike da shagwab'a yace "Sai kace muje shalele."
Anya yaron nan banda aljanu kuwa? Tambayar da lieutenant ya ma kanshi kenan, wato dan ya ga ya zo shine saiya mishi iskanci yasa ranshi ya b'ace har ya kasa yin abinda ya fad'a, daga Ammar d'in har Amna kallonshi suke suna jiran suji me zaice, rarraba ido yake ganin jami'in dake tare dasu ne kawai yasa yayi murmushi yace "To muje shalele."
Dariya yayi ya rik'e hannun lieutenant da kuma hannun Amna suka rankaya yana fad'in "Daga yanzu ni ma na zama shalelenka, kaga Amar shalelen Hajia ne ni kuma na ka ko Abba?"
"Umm." Kawai ya fad'a ba tare da yace komai ba, kallonshi lieutenant yayi yace "Motarka fa?"
Saida ya bud'a ta lieutenant ya shiga ya hakimce sannan yace "Tare da Abbana zan tafi, gobe na dawo na d'auka daga nan nima saina shigar da k'arar wannan banzan."
Shiga sukayi duka Amna na baya yace "K'arar me kuma?" Saida ya kalleshi yace "Abba k'azafi ya min wai ina saka kayan soja, har da cewa wai ina da bindiga."
Kallonshi lieutenant yayi irin kallon nan na anya Ammar ba gaskiya bane kuwa, saida ya tayar da motar suka d'auki hanya kafin yace "Ka daina shiga rigima Ammar, bana jin dad'in haka fa, wai kai baka san ka girma bane?"
"Zan daina Abba, dana gama da wannan yaron shikenan." Ya fad'a yana kallon titi, *meye nufinshi akan Jano ne? Ni dai nasan da abinda yake so dashi*, suna zuwa gida suka fito a mota suka nufi hanyar da zata sadasu da b'angarensu, dole ta inda lieutenant ya paka mota indai zasu wuce sai sun bi ta k'ofar shiga falon Hajia, hakanne yasa Ammar hangota zaune kan kujerar mulki, murmushi yayi ya tunkari shiga ciki, rik'oshi lieutenant yayi yace "Ina zaka kuma? Wuce ka bi matarka."
Langab'e kai yayi yace "Abba Hajia zai gaida duk yau bamu had'u ba duk bana jin dad'i."
Wani kallo ya masa yace "Ammar uwata ce fa, karka ja min zagi yanzu a daren nan mana."
"Allah Abba ba zan sa ba, nayi alk'awari." Yana fad'a ya shiga ciki da sallama, Amna kam da take jin haushin tura mata yer uwarta wani wuri bata shiga ba sai na su b'angaren data nufa. Yana zuwa kamar an tura shi ya durfafeta ya rumgume tare da sumbatar goshinta yana fad'in "Hajiata ikon Allah, wallahi duk nayi kewarki wunin nan kawai da ban ganki ba."
Tareshi tayi daga jikinta tana goge goshinta da fad'in "Kai rabu dani dallah, wai kai baka da lafiya ne?"
Kallonta yayi ya dafa saitin zuciyarshi yace " Yanzu ne kawai na fara jin na samu lafiya da nayi tozali dake."
Da k'arfi ya sake fizgo fuskarta ya sumbaceta a kumatu yana fad'in "Ina sonki, saida safe, karki bari kishina ya hanaki bacci."
Saida ta marmad'a ido saboda yanda ya fincikota, da kallo ta bishi tana mamakin halin wannan k'waya d'aya tak dake saka mata hawan jini, yanda ta kafe k'ofar da ido har ya b'ace ma ganinta sai kawai taji tana murmushi, kamar an tsikareta sai kuma taja tsaki tana fad'in "Mahaukaci."
*Capital*
Baccin marar dad'i har ya fara d'aukarta d'aya daga cikin ma'aikatan gidan ta shigo ta kirata, fitowa tayi jiki a sanyaye ta zo ta tsaya gabanta kamar yanda ita ma take tsaye, kasa d'aga kai tayi ta kalleta saboda tun tana tahowa taga kayan bacci ne jikinta masu shegen kyau da d'aukar ido, kamar saukar aradu ta kashe ta da mari tare da mata tsawa tace "Idiot, ina tsaye shine ke ma zaki tsaya min a kai haka."
Dafe kumci tayi ta bud'e baki ta kalleta tace "Kika mare ni?"
D'aga hannu ta sakeyi zata sake marinta tayi baya da k'arfi tana fad'in "A'a wallahi, ko uwata ban rayu da ita ba ta yanda zan iya fad'a miki ranar data d'aga hannunta a kaina, dan haka ya tsaya nan gaskiya."
Cike da iko tace "Ni kike fad'awa haka? To bari kiga abinda zanyi, ubanki zan fad'a ma ya sanar dake k'arfin ikona, idan ya fad'a miki da kanshi zaki fi ji da kyau."
Juyawa ta shiga ta wata k'ofa da zata sadata da d'akin baccinshi, tab'e baki Hamna tayi ta juya ta koma ni'imtaccen d'akinta ta kwanta, amma abun takaici sai ga mahaifinta cikin jallabiya tare da matarshi sai wani rirrik'eshi take tana kukan munafurci, bata san me ta fad'a mishi ba? Bata san meya faru ba kawai saiya rufe ta da fad'a kamar saukar ruwan sama, saida ya gama sannan ya jaddada mata duk abinda Aissata ta sakata tayi ko bata so dan ita ce mai gidan nan, sannan idan ta mata musu Allah ya isa bai yafe mata ba, juyawa yayi suka fita sai kawai ta fashe da kuka, duk rashin kirkin Hajia suna sakata su wala, babu takura babu matsi sai in ka taka mata doka, amma nan, lallai ma.
To fa hakan data faru ne yasa washe gari da safe ta kirata, tana zuwa tace "D'aki na zaki gyara min ki min shinfid'a, idan kin gama ki wanke ban d'aki da kyau sannan kiyi turare, idan kin gama sai ki zo na fad'a miki aiki na gaba da zaki min."
Hararanta ta farayi sama da k'asa kafin daga bisani ta tuna kalmar Allah ya isa da mahaifinta ya fad'a mata, cikin ladabi tace "To." Ta juya ta shiga d'akin, duk ni'imar duniya ta taru a d'akin nan, kud'i ko nace kayan kud'i kamar zasuyi magana da baki tsabar yanda aka tarwatsa su, komai na kud'i ne d'aruruwa ko milyoyi, gyarawa tayi ta share ta wanke har ban d'akin ta goge komai sannan tayi turare, kama daga na ruwa na tsintsiya har na wuta, hakan yasa d'akin k'ara sanyaya da sanyin k'amshi, tana idarwa ta fito ta fad'a mata, ki shiga madafa ki samu *Betrice* ta baki jadawalin duk abinda nake ci da kuma lokacin da nake cin shi, daga yanzu ke ce mai wannan alhakin."
Yawu ta had'e ba tace komai ba kawai ta wuce madafar, tana zuwa ta fara fad'a mata "07:30 zaki kai mata lipton a d'akinta, 08:00 zaki kai mata ruwa da matsatsun kayan itatuwa a d'akin motsa jiki, k'arfe 09:00 daidai zaki shirya mata petit déjeuner (karin kumallo) a kan table, da k'arfe..."
Hannu ta d'aga mata tana yatsina fuska tace "Dakata dan Allah, ki samu takarda ki rubata min zan duba daga baya, bana da lokacin wannan shashancin."
Yana fad'a ta barta nan tsaye tana kallonta, kamar yanda ta buk'ata haka ta ruba ta mata komai ta kai mata, daga wannan lokacin ta fara aiki dan matar muguwar yar tamne-tamne ce bata gajiya da had'id'iya, bata awa d'aya bata buk'aci wani abu ba, ko ba komai taji dad'i daya zama ita ce a gidan ba Amna ba, dan da ita ce to tana iya yin zuciya ta bar gidan sai kawai an ganta ta koma Maradi, sai dai Allah ya isar ta bita kam amma ba zata d'auka ba, da wannan yau ta kwanta baccin gajiya saboda bata huta ba ko kad'an sai kai da kawowa, abunka ga gidan gwamnati ga girma daga wani wurin zuwa wani tafiya ce mai tsayi.
*Gaga's house*