Sashe 70
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Colonel da har yanzu Zeinabu yake hangowa shi dai kallon kowa kawai yake, juyawa Ammar yayi zai fita Hajia wacce farkon al'amarin ita ma daru taso tayi, amma ganin babban jikan nata ya nuna bai yarda ba alhalin gata zaune yasa ta shirya b'ata mishi rai, cikin gadara tace "Ka ce baka yarda ba? To yanda da baka yardan ba ya za ayi kenan? A fasa?"
Juyowa yayi yace "Eh haka nake nufi."
Murmushi ta masa tace "To bari kaji Ammar, wallahi auren nan kamar anyi an gama, yar aikin gidanku zata shigo gidan nan a matsayin kishiyar uwarka, za'a ware mata d'aki kamar yanda aka ware ma uwarka, ubanka zai raba musu kwana, a gaban idonka dana uwarka zai shiga d'akin amaryar shi sai dai in kunga haka ku had'e zuciya ku mutu, kai idan da rabo ma nan da wata tara sai kunga sabon k'anenku da idonki."
_Ina fatan dai kun fahimci inda yayi gadon rashin kunyarshi da fitsara?_
Wata dariyar rashin mutumci ya mata yace "Hajajju mutan makka, ban miki musu ba cewa madarar mahaifina zata iya tasar d'an adam ba, amma gamsar da ita matar kam w..."
Cak ya tsaya da kalamanshi saboda saukar marin akan kumatunshi, Ummy ce tsaye gabanshi tana huci dan ba zata iya saurarenshi ba, da yatsa ta nuna masa k'ofar fita tana fad'in "Fita daga d'akin nan, ka fita nace."
Kallon Ummy yayi idonshi jawur da su kamar zai kama da wuta, cikin wani irin yanayi ya kalli Ummy kai kace ramawa zaiyi yace "Ummy mari na fa kikayi? Akan maganar k'azamar yarinyar da tsabar datti da za'a d'auke ta a jefa a cikin ruwan *Madarunfa* babu abinda zai hana ruwan yin bak'i k'irin, shikenan na fita."
Kallon Alhaji yayi wanda shi kanshi baiji dad'in marin ba yace "Alhaji na zo ne saboda ance kai kake nema na, amma ba dan haka ba da babu abinda zai sa na zo dan duk nan ciki bayan kai babu wanda zai iya kirana domin magana ta arzik'i."
Juyawa yayi zai fita cikin k'arajin murya Ummy ta fashe da kuka tace "Fita d'an iska kawai, duk nan ciki waye sa'anka da zaka zauna kanawa fitsara da rashin kunya."
Tsayawa yayi ya juyo da k'arfi da niyyar magana amma kuma zuciyarshi bugawa take da sauri, k'urawa Ummy ido kawai yayi kamar zai cinyeta d'anya, bubbuga k'irjin ta tayi tace "Eh na fad'a, kai sarkin zuciya ko? Ranka ya b'ace ne? To zo ka dake ni Ammar."
Husseina ce ta mik'e ta kamata ta zaunar da ita tana fad'in "Dan Allah Sa'ada ki daina zubar da hawaye akan d'an da kika haifa a cikinki, shin kinsan tasirin da hakan zai masa kuwa?"
Cikin kuka ta kalli Husseina tace "Hajia menayi? Wane laifi na aikata a duniya dana cancanci haihuwar Ammar? Shi fa ba k'aramin yaro bane, amma kullum saiya b'ata min rai a gidan nan hankalinshi ke kwantawa."
Ammar da har yanzu ke tsaye yana kallonta idonshi ne suka sake rinewa, bugun zuciyarshi kuma ya sake nunkuwa, had'e hannunshi yayi ya dunk'ule shi cikin b'acin rai da neman wanda zaiyi masifa da shi ya juya, ai kuwa tvn Hajia ya kalla ya gabzawa dunk'ulellen hannun nan, abinka ga tvn zamani kuwa wacce ke manne a jikin bango sai kuwa ta gabce ta fad'o k'asa inda ta bugi k'aramin teburin glishin da aka d'ora décoder da kuma remonte, a tare kayan duk suka fad'o suka watse, juyowa yayi lokacin da wasu hawayen bak'in ciki da takaici suka zubo daga idonshi cikin muryar da zata tashi hankalin mai sauraro ya rik'e murfin k'ofa yace "Idan har kun tsane ni ku kashe ni mana, me ma yasa kika bari na zo duniya baku kashe ni ba? Ku kashe ni mana na huta kuma ku huta, naji ni d'an iska ne, fitsararre, marar kunya, bana da anfani a gareku, baku ga anfanin haihuwata ba, to na mutu mana ina ruwanku?"
Idan ka cire Hajia da lieutenant dukansu mutanen wurin mik'ewa sukayi tsaye saboda tsoron ganin halin da yake ciki, k'ofar daya rik'e sosai ya turata da k'arfi ta bada wata k'ara mai k'arfi, juyawa yayi kamar zai tashi sama ya bar d'akin ya nufi b'angarensu, Amar da d'an sauri ya fito da niyyar bin bayanshi Hajia tace "Shalele rabu da shi, ai dai kasan zuciyar ce ta motsa ko? Kuma kafi kowa sanin cewa yana hucewa kan wanda ma bai ji ba bai gani ba, dan haka rabu da shi karya illatala, ka barshi har ya sauko zai zo ya biyani tvn nan daya fasa bak'in munafiki kawai, dama yana jin haushin kallon da nake."
Lieutenant ne yace "Rabu da shi, ba mai kai ba kar wanda ya kuskura ya tanka masa har zuwa lokacin da zai sauko."
Alhaji dake tsaye ne cike da nuna rashin jin dad'i yace " Dan Allah magana mai dad'i ta dinga fitowa daga bakinku zuwa kanshi, ba kusan komai k'aramtar kalma kuka fad'eta tasiri take akan yaranku ba, kuma ya kamata ace kuna hak'uri dashi, yanzu nan kunsan dan kwana uku ba zai kula kowa ba."
D'an k'aramin tsaki yayi ya nufi d'akin shi inda Hajia ta bishi da harara da gunaguni kuma daga lieutenant har colonel babu wanda bai gani ba, duk da hakan bai musu dad'i ba amma hak'ura sukayi, Sa'ada ma da sauri ta tashi ta shiga d'akin ta tana ci gaba da kuka inda lieutenant ya bi bayanta, Hajia ma mik'ewa tayi ta nufi d'akin Alhaji dan suyi magana, hakan ne ya bawa Amar damar fita ya bi bayan d'an uwanshi da tunanin shi kawai ke kan hannunshi daya rotse yake zubar jini amma shi yaga bai ma damu ba, colonel kuma kallon Junaid yayi wanda shi dama tunda aka fara magana tsaye yake yace "Saika wuce ka d'auko min rigata d'aki, dan inhar zan shiga babu abinda zai hana ni gota uwar nan taka."
Da sauri Junaid ya juya ya shiga d'akin, akan gado ya d'auko rigar ya fito har lokacin Zeinabu na ban d'aki, yana kawo masa ya saka fita yayi ya bar gidan shima.
Yana shiga kai tsaye d'akin magungunanshi ya shiga, zaune yayi akan gadon marasa lafiya dake tsakiyar d'akin ya duk'ar da kai k'asa ya rik'e hannun dake fitar jini, har yanzu ya kasa tsayar da hawayen dake zubo mishi, tafarfasa kawai zuciyarshi keyi na k'una da k'unci, iyayen da suka haife ni, amma kullum babu kalma mai dad'i tsakani na dasu, tun ina yaro na fahimci me kalmar d'an iska take nufi, menayi da suka tsaneni tun ina yaron da bansan daidai da rashin daidai ba? Mena aikata gare su haka dayasa suka k'ini? Shin na zo musu ba yanda suka so bane? Ko kuma guda suka so haihuwa sai ni na fara fad'owa duniyar? Ko kuma dai ni wani sirri ne tare dani da yasa kowa na gidan nan ya tsane ni? Menene shi? Wa zai fad'a min dalilin tsanar da suka min? Iyaye na su hantare ni, kakanta ta zageni ta koreni daga wajenta, da irin haka suka raine ni a gidan nan, babu wanda ya tab'a rarrashi na, babu wanda ya tab'a tambayata damuwa ta ko matsalata, akan me? Akan me! Ya fad'a da k'arfi har da saka k'afa ya ture doguwar kujerar dake gaban gadon saida tayi baya.
Saukowa yayi ya d'auki alcohol ya bud'e ya rintse ido sosai ya dararawa hannun, wani rad'ad'i ne ya ziyarce shi amma a hankali ya bud'a ido ya kalli hannun yace "Wannan rad'ad'in bai kai rabin wanda nake ji a zuciyata ba a duk sanda suka kira ni da d'an iska."
Wasu hawaye ne suka sake taho mishi hakan yasa shi fad'awa kan gadon ya zaune yasa bandeji yana laulaye hannun yana fad'in "Kuna kirana d'an iska a kullum, shin baku tunanin na zama d'an iskan ? Namiji ne fa ni, ina da sha'awa da son jin dad'i, ba kwa tunanin tasirin addu'arku wata rana ya kaini ga aikata b'arna? Idan haka ta faru shima saik ku sake kirana d'an iska?"
Amar na tsaye k'ofar d'akin ya gagara shiga, yasan halin kayanshi ba zai tab'a bari ya rarrashe shi ba, abinda yaji kuma sai yaji kawai bari ya bashi wuri ya fad'i abinda ke ranshi ko yaji sauk'i, dan haka ya bar wurin cike da tausayin d'an uwanshi da kuma jin lallai iyayensu basa kyautawa.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Suna tafiya kawu Mamu ya tattaro kud'i ya shigo gidan afujajen kamar wanda zaho ya koro ya shiga bukkarshi, kud'in ya aje ya fito yana k'wala kiran Zeituna, ita ko tana can wajen yan bisashen da ake kiwo a gidan tana d'aure su, da sauri ta zo ta sunkuya gabanshi cikin fulatanci tace "Kawu gani."
Shima a fulatanci yace "Me kikeyi?"
Kallonshi tayi tace "Ina d'aure bisashe ne."
Juyawa yayi ya kalli Jumma dake cin tuwo yace "Innar Jumare, daga yau Zeituna karta sake aikin komai a gidan nan, ko da d'auke kara ne daga nan zuwa can, aikinta a gidan nan karya wuce yin wanka ta ci abinci ta zauna ta huta, kinji ko? Har wurin aiki ma surukinta yace karta koma zuwa."
Ya fad'a yana kama kunnenshi alamar taji, shek'ek'e Jumma ta kalleshi cikin k'warewa a harshenta tace "To me kenen zatayi idan batayi aiki ba? Ko mu bayinta ne da zamu dinga mata bauta?"
Cikin d'aga murya yace "To sai me idan kun mata bautar? Ku shekara nawa ta d'auka tana muku bautar? Ke bari kiji wallahi, tuwon ma idan har tana buk'ata a saka mata shi a baki to sai an saka mata ko da hakan na nufin zan biya kud'in hakan ne, idan kuma kika bari na kamata a gidan nan kin sakata aiki, to wallahi zan iya sakinki saki har uku, in yaso in auro yar birni ke kuma ki koma rigarku."
Kallonshi tayi tace "To wai meya faru ne? Akan me zaka ce zaka sakeni akan wannan mayyar yarinyar?"
Cikin karsashi yace "Saboda aure zan mata nan da kwana uku, yarinya mai k'ashin arzik'i ce, yau ma daga babban gidan da take aiki ne aka zo neman aurenta."
Tunda ya ambaci aure Zeituna gabanta ya fad'i ta d'aga kai ta kalleshi tace "Aure kuma kawu?"
Juyowa yayi yace "Eh haka nake nufi."
Murmushi ta masa tace "To bari kaji Ammar, wallahi auren nan kamar anyi an gama, yar aikin gidanku zata shigo gidan nan a matsayin kishiyar uwarka, za'a ware mata d'aki kamar yanda aka ware ma uwarka, ubanka zai raba musu kwana, a gaban idonka dana uwarka zai shiga d'akin amaryar shi sai dai in kunga haka ku had'e zuciya ku mutu, kai idan da rabo ma nan da wata tara sai kunga sabon k'anenku da idonki."
_Ina fatan dai kun fahimci inda yayi gadon rashin kunyarshi da fitsara?_
Wata dariyar rashin mutumci ya mata yace "Hajajju mutan makka, ban miki musu ba cewa madarar mahaifina zata iya tasar d'an adam ba, amma gamsar da ita matar kam w..."
Cak ya tsaya da kalamanshi saboda saukar marin akan kumatunshi, Ummy ce tsaye gabanshi tana huci dan ba zata iya saurarenshi ba, da yatsa ta nuna masa k'ofar fita tana fad'in "Fita daga d'akin nan, ka fita nace."
Kallon Ummy yayi idonshi jawur da su kamar zai kama da wuta, cikin wani irin yanayi ya kalli Ummy kai kace ramawa zaiyi yace "Ummy mari na fa kikayi? Akan maganar k'azamar yarinyar da tsabar datti da za'a d'auke ta a jefa a cikin ruwan *Madarunfa* babu abinda zai hana ruwan yin bak'i k'irin, shikenan na fita."
Kallon Alhaji yayi wanda shi kanshi baiji dad'in marin ba yace "Alhaji na zo ne saboda ance kai kake nema na, amma ba dan haka ba da babu abinda zai sa na zo dan duk nan ciki bayan kai babu wanda zai iya kirana domin magana ta arzik'i."
Juyawa yayi zai fita cikin k'arajin murya Ummy ta fashe da kuka tace "Fita d'an iska kawai, duk nan ciki waye sa'anka da zaka zauna kanawa fitsara da rashin kunya."
Tsayawa yayi ya juyo da k'arfi da niyyar magana amma kuma zuciyarshi bugawa take da sauri, k'urawa Ummy ido kawai yayi kamar zai cinyeta d'anya, bubbuga k'irjin ta tayi tace "Eh na fad'a, kai sarkin zuciya ko? Ranka ya b'ace ne? To zo ka dake ni Ammar."
Husseina ce ta mik'e ta kamata ta zaunar da ita tana fad'in "Dan Allah Sa'ada ki daina zubar da hawaye akan d'an da kika haifa a cikinki, shin kinsan tasirin da hakan zai masa kuwa?"
Cikin kuka ta kalli Husseina tace "Hajia menayi? Wane laifi na aikata a duniya dana cancanci haihuwar Ammar? Shi fa ba k'aramin yaro bane, amma kullum saiya b'ata min rai a gidan nan hankalinshi ke kwantawa."
Ammar da har yanzu ke tsaye yana kallonta idonshi ne suka sake rinewa, bugun zuciyarshi kuma ya sake nunkuwa, had'e hannunshi yayi ya dunk'ule shi cikin b'acin rai da neman wanda zaiyi masifa da shi ya juya, ai kuwa tvn Hajia ya kalla ya gabzawa dunk'ulellen hannun nan, abinka ga tvn zamani kuwa wacce ke manne a jikin bango sai kuwa ta gabce ta fad'o k'asa inda ta bugi k'aramin teburin glishin da aka d'ora décoder da kuma remonte, a tare kayan duk suka fad'o suka watse, juyowa yayi lokacin da wasu hawayen bak'in ciki da takaici suka zubo daga idonshi cikin muryar da zata tashi hankalin mai sauraro ya rik'e murfin k'ofa yace "Idan har kun tsane ni ku kashe ni mana, me ma yasa kika bari na zo duniya baku kashe ni ba? Ku kashe ni mana na huta kuma ku huta, naji ni d'an iska ne, fitsararre, marar kunya, bana da anfani a gareku, baku ga anfanin haihuwata ba, to na mutu mana ina ruwanku?"
Idan ka cire Hajia da lieutenant dukansu mutanen wurin mik'ewa sukayi tsaye saboda tsoron ganin halin da yake ciki, k'ofar daya rik'e sosai ya turata da k'arfi ta bada wata k'ara mai k'arfi, juyawa yayi kamar zai tashi sama ya bar d'akin ya nufi b'angarensu, Amar da d'an sauri ya fito da niyyar bin bayanshi Hajia tace "Shalele rabu da shi, ai dai kasan zuciyar ce ta motsa ko? Kuma kafi kowa sanin cewa yana hucewa kan wanda ma bai ji ba bai gani ba, dan haka rabu da shi karya illatala, ka barshi har ya sauko zai zo ya biyani tvn nan daya fasa bak'in munafiki kawai, dama yana jin haushin kallon da nake."
Lieutenant ne yace "Rabu da shi, ba mai kai ba kar wanda ya kuskura ya tanka masa har zuwa lokacin da zai sauko."
Alhaji dake tsaye ne cike da nuna rashin jin dad'i yace " Dan Allah magana mai dad'i ta dinga fitowa daga bakinku zuwa kanshi, ba kusan komai k'aramtar kalma kuka fad'eta tasiri take akan yaranku ba, kuma ya kamata ace kuna hak'uri dashi, yanzu nan kunsan dan kwana uku ba zai kula kowa ba."
D'an k'aramin tsaki yayi ya nufi d'akin shi inda Hajia ta bishi da harara da gunaguni kuma daga lieutenant har colonel babu wanda bai gani ba, duk da hakan bai musu dad'i ba amma hak'ura sukayi, Sa'ada ma da sauri ta tashi ta shiga d'akin ta tana ci gaba da kuka inda lieutenant ya bi bayanta, Hajia ma mik'ewa tayi ta nufi d'akin Alhaji dan suyi magana, hakan ne ya bawa Amar damar fita ya bi bayan d'an uwanshi da tunanin shi kawai ke kan hannunshi daya rotse yake zubar jini amma shi yaga bai ma damu ba, colonel kuma kallon Junaid yayi wanda shi dama tunda aka fara magana tsaye yake yace "Saika wuce ka d'auko min rigata d'aki, dan inhar zan shiga babu abinda zai hana ni gota uwar nan taka."
Da sauri Junaid ya juya ya shiga d'akin, akan gado ya d'auko rigar ya fito har lokacin Zeinabu na ban d'aki, yana kawo masa ya saka fita yayi ya bar gidan shima.
Yana shiga kai tsaye d'akin magungunanshi ya shiga, zaune yayi akan gadon marasa lafiya dake tsakiyar d'akin ya duk'ar da kai k'asa ya rik'e hannun dake fitar jini, har yanzu ya kasa tsayar da hawayen dake zubo mishi, tafarfasa kawai zuciyarshi keyi na k'una da k'unci, iyayen da suka haife ni, amma kullum babu kalma mai dad'i tsakani na dasu, tun ina yaro na fahimci me kalmar d'an iska take nufi, menayi da suka tsaneni tun ina yaron da bansan daidai da rashin daidai ba? Mena aikata gare su haka dayasa suka k'ini? Shin na zo musu ba yanda suka so bane? Ko kuma guda suka so haihuwa sai ni na fara fad'owa duniyar? Ko kuma dai ni wani sirri ne tare dani da yasa kowa na gidan nan ya tsane ni? Menene shi? Wa zai fad'a min dalilin tsanar da suka min? Iyaye na su hantare ni, kakanta ta zageni ta koreni daga wajenta, da irin haka suka raine ni a gidan nan, babu wanda ya tab'a rarrashi na, babu wanda ya tab'a tambayata damuwa ta ko matsalata, akan me? Akan me! Ya fad'a da k'arfi har da saka k'afa ya ture doguwar kujerar dake gaban gadon saida tayi baya.
Saukowa yayi ya d'auki alcohol ya bud'e ya rintse ido sosai ya dararawa hannun, wani rad'ad'i ne ya ziyarce shi amma a hankali ya bud'a ido ya kalli hannun yace "Wannan rad'ad'in bai kai rabin wanda nake ji a zuciyata ba a duk sanda suka kira ni da d'an iska."
Wasu hawaye ne suka sake taho mishi hakan yasa shi fad'awa kan gadon ya zaune yasa bandeji yana laulaye hannun yana fad'in "Kuna kirana d'an iska a kullum, shin baku tunanin na zama d'an iskan ? Namiji ne fa ni, ina da sha'awa da son jin dad'i, ba kwa tunanin tasirin addu'arku wata rana ya kaini ga aikata b'arna? Idan haka ta faru shima saik ku sake kirana d'an iska?"
Amar na tsaye k'ofar d'akin ya gagara shiga, yasan halin kayanshi ba zai tab'a bari ya rarrashe shi ba, abinda yaji kuma sai yaji kawai bari ya bashi wuri ya fad'i abinda ke ranshi ko yaji sauk'i, dan haka ya bar wurin cike da tausayin d'an uwanshi da kuma jin lallai iyayensu basa kyautawa.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Suna tafiya kawu Mamu ya tattaro kud'i ya shigo gidan afujajen kamar wanda zaho ya koro ya shiga bukkarshi, kud'in ya aje ya fito yana k'wala kiran Zeituna, ita ko tana can wajen yan bisashen da ake kiwo a gidan tana d'aure su, da sauri ta zo ta sunkuya gabanshi cikin fulatanci tace "Kawu gani."
Shima a fulatanci yace "Me kikeyi?"
Kallonshi tayi tace "Ina d'aure bisashe ne."
Juyawa yayi ya kalli Jumma dake cin tuwo yace "Innar Jumare, daga yau Zeituna karta sake aikin komai a gidan nan, ko da d'auke kara ne daga nan zuwa can, aikinta a gidan nan karya wuce yin wanka ta ci abinci ta zauna ta huta, kinji ko? Har wurin aiki ma surukinta yace karta koma zuwa."
Ya fad'a yana kama kunnenshi alamar taji, shek'ek'e Jumma ta kalleshi cikin k'warewa a harshenta tace "To me kenen zatayi idan batayi aiki ba? Ko mu bayinta ne da zamu dinga mata bauta?"
Cikin d'aga murya yace "To sai me idan kun mata bautar? Ku shekara nawa ta d'auka tana muku bautar? Ke bari kiji wallahi, tuwon ma idan har tana buk'ata a saka mata shi a baki to sai an saka mata ko da hakan na nufin zan biya kud'in hakan ne, idan kuma kika bari na kamata a gidan nan kin sakata aiki, to wallahi zan iya sakinki saki har uku, in yaso in auro yar birni ke kuma ki koma rigarku."
Kallonshi tayi tace "To wai meya faru ne? Akan me zaka ce zaka sakeni akan wannan mayyar yarinyar?"
Cikin karsashi yace "Saboda aure zan mata nan da kwana uku, yarinya mai k'ashin arzik'i ce, yau ma daga babban gidan da take aiki ne aka zo neman aurenta."
Tunda ya ambaci aure Zeituna gabanta ya fad'i ta d'aga kai ta kalleshi tace "Aure kuma kawu?"