Sashe 191
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko da suka fito ya hangi Gambo sai kuwa Ammar ya tak'ark'are ya d'ora hannaye saman fuska ya shiga murzar ido wai shi a dole kuka ne yake, da sauri Gambo ya k'arasa ya tarbe shi da niyyar rumgume shi, amma ikon Allah sai Ammar ya fad'i k'asa zaune yana kuka cikin babbar murya yana tumurmusa k'afafu yana fad'in "Ni kawai ka koma babu inda zanje, haka kawai kuka manta dani a wurin nan suna ta dukana."
Rigarshi mai botira a gaba ya shiga kiciniyar bud'ewa yana fad'in "Dubi yanda suka farfasa min jiki, kamar ba d'anku ba ace duk babu mai so na a cikin, kalle ni fa dan Allah."
D'aga kai yayi sama yana wani kukan, kaf wurin babu wanda bai sakar masa ido ba, sai dai Gambo tuni ya harbo jirginshi yasan me yake nufi da abinda yake yi, juyowa yayi ya kalli major kafin yayi magana ya d'an muskuta tsayuwarshi yace "Wallahi yallab'ai babu wanda ya tab'a dukanshi a wurin nan, ko?"
Ya tambayi sauran yaran, dukansu girgiza kai sukayi alamar eh, kallonsu yayi ya tsaya da kukanshi yace "Na muku k'arya kenan?"
Kallon Gambo yayi yace "Abba na, ina k'arya ne ni?"
Juyawa Gambo ya sake yi ya kallesu yayi k'wafa tare da jinjina kai, sunkuyawa yayi ya tallaboshi yana fad'in "Rabu dasu yaro na, ai ba sai ka fad'a ba ma na sani, dubi duk yanda ka lalace."
Ai sai yaji dad'i Gambo ya taya b'era b'ari da sauri ya kamo hannunshi suka dawo kusa dasu, uku daga ciki ya nuna yace "Abba wad'an nan suke cinye min abinci na ina ganinsu, sai su had'a ni da wani banzan abinci bana iya cin shi ma, ni kawai ban yarda ba wallahi sai na shigar da k'ararsu."
A take suka shiga kallon kallo suna tausayawa kansu, su ai basu san girmanshi ya kai haka ba, kallonshi Gambo yayi yace "A'a bana son maganar shigar da k'ara, amma dai ka fad'i wani abinda kake so ni zan maka."
Ai da sauri major d'in yace "Yallab'ai..."
Kallonshi yayi yace "Ferme là."
Shirun yayi yana kallon Ammar dake kallonsu shima, a hankali yaji yace "Kawai su biyani kud'in abinci na."
Saida ya sauke ajiyar zuciya ta jin dad'i, da sauri cikin yaran wani yace "Nawa kake so yallab'ai."
Saida ya harare shi yace "Dukanku ku bada jaka sha biyar biyar."
D'aya daga ciki ne ya d'an bud'a baki irin yaushe muka ci wannan abincin? Idan siya zamuyi fa jaka goma zata bamu buhun oriba rice, major d'in suka ga yasa hannu aljihu ya ciro kud'in ya mik'a mishi, karb'a yayi tare da tara hannu wa sauran suma, da k'yar suka lalabo kud'in tunda wata yayi nisa😂, kallon major d'in Gambo yayi yace "Ya zamuyi yanzu?"
Girgiza kai yayi yace "Yallab'ai comme tu le veux."
Kallon Ammar yayi yace "Ina so na koma da yaro na, shin akwai tara ko wani abu ne?"
Girgiza kai yayi yace "Tun ranar aka so musu sulhu shine ya k'i."
"Me ye abunyi yanzu?"
Saida ya d'an kalli Ammar daya kafesu da ido yana ta kallo yana tunanin ta yanda zai diro musu kafin yace "Tara ce zai biya, sai kuma dan Allah ya kiyaye gaba, fad'a ba na shi bane yana babban mutum, sannan ya fita harkar yaron dan iyayenshi sun ce zasu d'auki mummunan mataki idan ya k'ara tab'a musu yaro, shine kawai."
Hannu yasa aljihun rigarshi ta ciki ya fito da cash yan jaka goma goma d'auri uku na 300 000 ya ajiye gaban teburin yana fad'in "A biya tarar, insha Allah kuma za'a kiyaye."
Kasa amsa mishi major d'in yayi kud'in nan sun gama haukatashi, yana rik'e da hannun Ammar zasu wuce Ammar yace "To wayata fa ko kuna da gadona ne?"
Da sauri major d'in ya jawo wani coffre ya fito da wayoyi ya aje gaban tebur d'in, dubawa yayi ya d'auki tashi ya juya zasu tafi, Gambo ne yace "Bayan wayar babu kayanka ne?"
Ba tare daya kalleshi ba yace "Me zanyi dasu to? Su d'auka na bar musu."
Suna k'arasa aka bud'e musu motar suka shiga tare, saida suka d'auki hanya Gambo ya kalleshi da kyau, yayi bak'i abinki ga jar fata, ya rame sai gashi da duk yayi baje baje ba kyau, a hankali yace "Ammar."
Ba tare daya kalleshi ba yace "Na sani Abba, zan daina."
Da mamaki ya kalleshi yace "Kasan me?"
Yana kallon titi yace "Nasan cewa za kayi na daina rigima na girma, na daina irin wannan abubuwan ni ba yaro bane, sannan idan ban bari dan komai ba na daina ko dan iyalina."
A d'an tsorace ya kalleshi ya had'e yawu, har ga Allah abinda zai fad'a kenan, dan ko da kalaman sun banbanta maganar dai d'aya ce, da k'yar ya k'ak'aro murmushi yace "Ka min alk'awarin zaka daina to?"
Fuska a had'e yace "Eh Abba."
Rik'o hannunshi yayi yace "Nagode, kuma na ji dad'i sosai, kaga su kanka iyalinka hankalinsu zai kwanta."
Yar k'aramar k'wafa yayi ya matsu ya ganshi gida ya tashi hankalin uban kowa, ba dai shi suka wofantar ba? Zasu gane yau d'in nan zai bar musu gidan ya koma na shi gidan, har ita kankana sai ta ci kakanta yau, inbai manta ba da aka tab'a rik'e shi marigayiya zuwa tayi tace sai dai su kwana, amma ita shine babu ruwanta ko?
Ko da suka zo gida kusan babu wanda ya fita dan safiya ce, a lokacin Hamna tana tare da su Ummy suna shirya teburin cin abinci, suna juyawa dan amsa sallamarsu suka had'a ido, da wani irin farin cikin da ita kanta bata san ta samu kanta a ciki ba ta saki cokalan hannunta ta ruga a guje, ta manta da duk iyayen dake wuri ta fad'a k'irjin mijinta.
Saida ya lumshe ido alamar sak'on ya isa inda aka aikashi, amma da yake jaraba ce ya shigo da ita saiya ture ta a jikinshi ya kalli Gambo yana nuna mishi yace "Ka gani ko Abba, lafiyayyen abun kari ne suke shiryawa zasu ci hankali kwance, nan kaga alamar damuwa tare da wani na rishina a gidan?"
Kallon Ummy yayi da su Hajia da su lieutenant yace "Du barkanku da warhaka, Allah ya k'ara muku lafiya da arzik'i."
Da kanshi kuma ya amsa da "Ameen."
Hamna ya kalla kafin ya ankara ya cakumo hannunta ya fita da ita daga d'akin, k'ok'arin k'wacewa ta shiga yi tana fad'in "Yah Ammar, yah Ammar sake ni mana, dan Allah sake ni."
Saida suka kai k'ofar d'akinsu ya ja ya tsaya ya kalleta yace "Bud'e min k'ofar."
Kamar zata yi kuka tace "Makullin yana can na baro, bara n..."
Bata kai k'arshen maganarta ba taga yasa wa k'ofar k'afa da k'arfin sababi ya turata, ba shiri k'ofar ta wangale ta bud'e, turata yayi da k'arfi har tana neman fad'uwa kafin ya shiga shi ma, da sauri ya shige madafa inda ta mik'e dan binshi ta ga me zaiyi, tana kaiwa k'ofar shi kuma zai fito suka had'e, kwanukan data jera a madafar kamar kwalliya ta ga ya fito dasu a hannu, da mamaki ta kalleshi tace "Yah Amm.."
Bai bari ta gama fad'a ba ya buga kwanukan a k'asa, masu fashewa kam sun fashe mai lotsawa ya lomatsa, baki bud'e irin abun ya firgitata ta kalle shi tace "Wai me ye haka? Lafiyar ka..."
Sam bai bari ta fad'a abinda take son fad'a ba saboda hannun daya d'aga zai gaura mata mari, amma kuma kasawa yayi saiya kafe fuskarta da kallo, tsoro k'arara ne bayyane a fuskarta ta rintse ido ta kawar da kai gefe tana jiran jin saukarshi, jin shirun yasa a hankali ta shiga bud'a ido ta sauke kanshi, suna had'a ido sai kawai ta fashe da kuka dan abinda zata iya yi kenan, tana ganin ya sauke hannunshi k'asa sai kawai ta ruk'umk'umeshi a jiki tana sake fashewa da kukan sosai.
K'amk'ame shi tayi sosai tana fad'in "Kayi hak'uri yah Ammar, kayi hak'uri dan Allah kar kayi hushi dani, wallahi Abba ne ya tilasta ni kar na fad'awa kowa, kayi hak'uri dan Allah, yanzu ma nasan na sab'awa Abba tunda na kira Abba na fad'a mishi."
Wani irin tausayinta ne ya kashe shi, rumgume ta yayi shima ba shiri ya rad'a mata a kunne "Kin gama dani Hamna, ina sonki kinji."
D'ago kai tayi ta kalleshi tace "Muje kayi wanka bawan Allah sai tsami kake."
😂 Bushewa tayi da dariya hakan yasa shi matseta sosai suka shiga d'aki, sosai ta bashi kulawa a wannan lokacin, wanka soso da sabulu haka ta mishi, haka ta b'ata lokaci wajen wanke mishi gasumbarshi da gashin kanshi, hatta aske mafi sirrin wurin dake tara gashi ita ta cire mishi, tun a ban d'aki ta cire mishi akaihu kafin suka fito, da k'yar ya hak'ura ta shafa mishi mai ta caje mishi gashi ta shafa mishi mayukanshi, tana kawo mishi tea mai kauri da zafi ya shanye yaji k'arfi sai fa aiki ya tashi.
Ya nuna mata yayi kewarta na sati biyu, ya nuna mata yana son ta kuma yana son kasancewa da ita, ita ma bata tsaya a baya ba ta nuna mishi tayi kewarshi, suna d'aki hankali kwance suna raya zuk'atansu har azahar tayi. Lokacin da zai fita salla ne yake fad'a mata ta shirya yau zasu bar gidan nan tare da yaransu. Ba tayi musu ba dan tasan yanzu su fara tijara da to kawai ta bishi ta shiga had'a iya abinda zata had'a, sauran kuma tace daga baya sun gama d'auka.
Baya fitarsu kuma colonel ne ya kira Gambo yake tambayarshi yaya? A cewarshi "Mun dawo, gamu ma gida yanzu."
"Ina Hassan yake?" Cewar colonel, ko da Gambo yaji haka yasan babu arzik'i, mik'awa lieutenant wayar yayi yace "Gashi kuyi magana."
Ko da lieutenant ya amsa colonel yace "Hassan ka kyauta, an gode Allah ya saka da alkairi, yau Allah ya rufa maka asiri bana garin nan, da sai na maka k'ullin tsiya a ciki har ka amayo hanjin ka."
Cikin fad'a lieutenant yace "To bismillah, dan kaga bamu kusa shine zaka fad'a min magana, to ka zo kayi abinda za kayi."
Shima cikin fad'a yace "Yo mu ba abun kunyarmu bane wai d'an mu a rufe, kasan irin kunyata mun da kayi?"
Rigarshi mai botira a gaba ya shiga kiciniyar bud'ewa yana fad'in "Dubi yanda suka farfasa min jiki, kamar ba d'anku ba ace duk babu mai so na a cikin, kalle ni fa dan Allah."
D'aga kai yayi sama yana wani kukan, kaf wurin babu wanda bai sakar masa ido ba, sai dai Gambo tuni ya harbo jirginshi yasan me yake nufi da abinda yake yi, juyowa yayi ya kalli major kafin yayi magana ya d'an muskuta tsayuwarshi yace "Wallahi yallab'ai babu wanda ya tab'a dukanshi a wurin nan, ko?"
Ya tambayi sauran yaran, dukansu girgiza kai sukayi alamar eh, kallonsu yayi ya tsaya da kukanshi yace "Na muku k'arya kenan?"
Kallon Gambo yayi yace "Abba na, ina k'arya ne ni?"
Juyawa Gambo ya sake yi ya kallesu yayi k'wafa tare da jinjina kai, sunkuyawa yayi ya tallaboshi yana fad'in "Rabu dasu yaro na, ai ba sai ka fad'a ba ma na sani, dubi duk yanda ka lalace."
Ai sai yaji dad'i Gambo ya taya b'era b'ari da sauri ya kamo hannunshi suka dawo kusa dasu, uku daga ciki ya nuna yace "Abba wad'an nan suke cinye min abinci na ina ganinsu, sai su had'a ni da wani banzan abinci bana iya cin shi ma, ni kawai ban yarda ba wallahi sai na shigar da k'ararsu."
A take suka shiga kallon kallo suna tausayawa kansu, su ai basu san girmanshi ya kai haka ba, kallonshi Gambo yayi yace "A'a bana son maganar shigar da k'ara, amma dai ka fad'i wani abinda kake so ni zan maka."
Ai da sauri major d'in yace "Yallab'ai..."
Kallonshi yayi yace "Ferme là."
Shirun yayi yana kallon Ammar dake kallonsu shima, a hankali yaji yace "Kawai su biyani kud'in abinci na."
Saida ya sauke ajiyar zuciya ta jin dad'i, da sauri cikin yaran wani yace "Nawa kake so yallab'ai."
Saida ya harare shi yace "Dukanku ku bada jaka sha biyar biyar."
D'aya daga ciki ne ya d'an bud'a baki irin yaushe muka ci wannan abincin? Idan siya zamuyi fa jaka goma zata bamu buhun oriba rice, major d'in suka ga yasa hannu aljihu ya ciro kud'in ya mik'a mishi, karb'a yayi tare da tara hannu wa sauran suma, da k'yar suka lalabo kud'in tunda wata yayi nisa😂, kallon major d'in Gambo yayi yace "Ya zamuyi yanzu?"
Girgiza kai yayi yace "Yallab'ai comme tu le veux."
Kallon Ammar yayi yace "Ina so na koma da yaro na, shin akwai tara ko wani abu ne?"
Girgiza kai yayi yace "Tun ranar aka so musu sulhu shine ya k'i."
"Me ye abunyi yanzu?"
Saida ya d'an kalli Ammar daya kafesu da ido yana ta kallo yana tunanin ta yanda zai diro musu kafin yace "Tara ce zai biya, sai kuma dan Allah ya kiyaye gaba, fad'a ba na shi bane yana babban mutum, sannan ya fita harkar yaron dan iyayenshi sun ce zasu d'auki mummunan mataki idan ya k'ara tab'a musu yaro, shine kawai."
Hannu yasa aljihun rigarshi ta ciki ya fito da cash yan jaka goma goma d'auri uku na 300 000 ya ajiye gaban teburin yana fad'in "A biya tarar, insha Allah kuma za'a kiyaye."
Kasa amsa mishi major d'in yayi kud'in nan sun gama haukatashi, yana rik'e da hannun Ammar zasu wuce Ammar yace "To wayata fa ko kuna da gadona ne?"
Da sauri major d'in ya jawo wani coffre ya fito da wayoyi ya aje gaban tebur d'in, dubawa yayi ya d'auki tashi ya juya zasu tafi, Gambo ne yace "Bayan wayar babu kayanka ne?"
Ba tare daya kalleshi ba yace "Me zanyi dasu to? Su d'auka na bar musu."
Suna k'arasa aka bud'e musu motar suka shiga tare, saida suka d'auki hanya Gambo ya kalleshi da kyau, yayi bak'i abinki ga jar fata, ya rame sai gashi da duk yayi baje baje ba kyau, a hankali yace "Ammar."
Ba tare daya kalleshi ba yace "Na sani Abba, zan daina."
Da mamaki ya kalleshi yace "Kasan me?"
Yana kallon titi yace "Nasan cewa za kayi na daina rigima na girma, na daina irin wannan abubuwan ni ba yaro bane, sannan idan ban bari dan komai ba na daina ko dan iyalina."
A d'an tsorace ya kalleshi ya had'e yawu, har ga Allah abinda zai fad'a kenan, dan ko da kalaman sun banbanta maganar dai d'aya ce, da k'yar ya k'ak'aro murmushi yace "Ka min alk'awarin zaka daina to?"
Fuska a had'e yace "Eh Abba."
Rik'o hannunshi yayi yace "Nagode, kuma na ji dad'i sosai, kaga su kanka iyalinka hankalinsu zai kwanta."
Yar k'aramar k'wafa yayi ya matsu ya ganshi gida ya tashi hankalin uban kowa, ba dai shi suka wofantar ba? Zasu gane yau d'in nan zai bar musu gidan ya koma na shi gidan, har ita kankana sai ta ci kakanta yau, inbai manta ba da aka tab'a rik'e shi marigayiya zuwa tayi tace sai dai su kwana, amma ita shine babu ruwanta ko?
Ko da suka zo gida kusan babu wanda ya fita dan safiya ce, a lokacin Hamna tana tare da su Ummy suna shirya teburin cin abinci, suna juyawa dan amsa sallamarsu suka had'a ido, da wani irin farin cikin da ita kanta bata san ta samu kanta a ciki ba ta saki cokalan hannunta ta ruga a guje, ta manta da duk iyayen dake wuri ta fad'a k'irjin mijinta.
Saida ya lumshe ido alamar sak'on ya isa inda aka aikashi, amma da yake jaraba ce ya shigo da ita saiya ture ta a jikinshi ya kalli Gambo yana nuna mishi yace "Ka gani ko Abba, lafiyayyen abun kari ne suke shiryawa zasu ci hankali kwance, nan kaga alamar damuwa tare da wani na rishina a gidan?"
Kallon Ummy yayi da su Hajia da su lieutenant yace "Du barkanku da warhaka, Allah ya k'ara muku lafiya da arzik'i."
Da kanshi kuma ya amsa da "Ameen."
Hamna ya kalla kafin ya ankara ya cakumo hannunta ya fita da ita daga d'akin, k'ok'arin k'wacewa ta shiga yi tana fad'in "Yah Ammar, yah Ammar sake ni mana, dan Allah sake ni."
Saida suka kai k'ofar d'akinsu ya ja ya tsaya ya kalleta yace "Bud'e min k'ofar."
Kamar zata yi kuka tace "Makullin yana can na baro, bara n..."
Bata kai k'arshen maganarta ba taga yasa wa k'ofar k'afa da k'arfin sababi ya turata, ba shiri k'ofar ta wangale ta bud'e, turata yayi da k'arfi har tana neman fad'uwa kafin ya shiga shi ma, da sauri ya shige madafa inda ta mik'e dan binshi ta ga me zaiyi, tana kaiwa k'ofar shi kuma zai fito suka had'e, kwanukan data jera a madafar kamar kwalliya ta ga ya fito dasu a hannu, da mamaki ta kalleshi tace "Yah Amm.."
Bai bari ta gama fad'a ba ya buga kwanukan a k'asa, masu fashewa kam sun fashe mai lotsawa ya lomatsa, baki bud'e irin abun ya firgitata ta kalle shi tace "Wai me ye haka? Lafiyar ka..."
Sam bai bari ta fad'a abinda take son fad'a ba saboda hannun daya d'aga zai gaura mata mari, amma kuma kasawa yayi saiya kafe fuskarta da kallo, tsoro k'arara ne bayyane a fuskarta ta rintse ido ta kawar da kai gefe tana jiran jin saukarshi, jin shirun yasa a hankali ta shiga bud'a ido ta sauke kanshi, suna had'a ido sai kawai ta fashe da kuka dan abinda zata iya yi kenan, tana ganin ya sauke hannunshi k'asa sai kawai ta ruk'umk'umeshi a jiki tana sake fashewa da kukan sosai.
K'amk'ame shi tayi sosai tana fad'in "Kayi hak'uri yah Ammar, kayi hak'uri dan Allah kar kayi hushi dani, wallahi Abba ne ya tilasta ni kar na fad'awa kowa, kayi hak'uri dan Allah, yanzu ma nasan na sab'awa Abba tunda na kira Abba na fad'a mishi."
Wani irin tausayinta ne ya kashe shi, rumgume ta yayi shima ba shiri ya rad'a mata a kunne "Kin gama dani Hamna, ina sonki kinji."
D'ago kai tayi ta kalleshi tace "Muje kayi wanka bawan Allah sai tsami kake."
😂 Bushewa tayi da dariya hakan yasa shi matseta sosai suka shiga d'aki, sosai ta bashi kulawa a wannan lokacin, wanka soso da sabulu haka ta mishi, haka ta b'ata lokaci wajen wanke mishi gasumbarshi da gashin kanshi, hatta aske mafi sirrin wurin dake tara gashi ita ta cire mishi, tun a ban d'aki ta cire mishi akaihu kafin suka fito, da k'yar ya hak'ura ta shafa mishi mai ta caje mishi gashi ta shafa mishi mayukanshi, tana kawo mishi tea mai kauri da zafi ya shanye yaji k'arfi sai fa aiki ya tashi.
Ya nuna mata yayi kewarta na sati biyu, ya nuna mata yana son ta kuma yana son kasancewa da ita, ita ma bata tsaya a baya ba ta nuna mishi tayi kewarshi, suna d'aki hankali kwance suna raya zuk'atansu har azahar tayi. Lokacin da zai fita salla ne yake fad'a mata ta shirya yau zasu bar gidan nan tare da yaransu. Ba tayi musu ba dan tasan yanzu su fara tijara da to kawai ta bishi ta shiga had'a iya abinda zata had'a, sauran kuma tace daga baya sun gama d'auka.
Baya fitarsu kuma colonel ne ya kira Gambo yake tambayarshi yaya? A cewarshi "Mun dawo, gamu ma gida yanzu."
"Ina Hassan yake?" Cewar colonel, ko da Gambo yaji haka yasan babu arzik'i, mik'awa lieutenant wayar yayi yace "Gashi kuyi magana."
Ko da lieutenant ya amsa colonel yace "Hassan ka kyauta, an gode Allah ya saka da alkairi, yau Allah ya rufa maka asiri bana garin nan, da sai na maka k'ullin tsiya a ciki har ka amayo hanjin ka."
Cikin fad'a lieutenant yace "To bismillah, dan kaga bamu kusa shine zaka fad'a min magana, to ka zo kayi abinda za kayi."
Shima cikin fad'a yace "Yo mu ba abun kunyarmu bane wai d'an mu a rufe, kasan irin kunyata mun da kayi?"