Sashe 168
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sakin hannun Hajia tayi ta kalli inda Hadiza ke tsaye wacce ta zo da taji jikin ya k'i kyau, ita ma alamar ta zo ta mata ta rik'e hannunta, magana take yi amma bata jin komai, a hankali ta durk'usa ta kai kunnenta kusan bakinta, cikin sanyin muryar da bata fita tace "Mama, ki yafe min, ki yafe min, Abba ma ya yafe min, yah Ammar, ki kira min yah Ammar na rok'i gafararshi, dan Allah ki ce masa ya zo ina son ganinshi, Mama, Mama, Mama, sau uku na kira sunanki ko? Dan Allah ki ce Hamna ta zauna tare da yah Ammar da kuma yara na, zata iya kula dasu kamar yanda nake yi, dan Allah Mama, kinji, kinji ko."
D'agowa tayi tace "Na ji Amna, kiyi ta kalmar shahada a bakinki, bari na kira miki Ammar d'in."
Tashi tayi da sauri ta fita, amma tana fitowa ita ma ta tsaya cikin wani d'aki da babu kowa ta shiga rera kuka, ta d'auki kusan minti ashirin tana kuka kafin ta fita ta same shi zaune ya had'a kai da gwiwa, da sauri tace "Ammar, ka zo dan Allah Amna tana son ganinka."
Tasowa yayi daga cikin masallacin ya matso kusanta cikin layi na galabaita yace "Mama dan Allah ku rabu da ita, zafin ciwo ne ke damunta kawai."
"A'a Ammar, ka zo kawai tunda tace tana buk'atar ganinka."
Cike da kasala yace "Shikenan muje."
Juyawa tayi ya saka takalminsa ya bi bayanta, ji yake gabanshi na tsananta fad'uwa, ko da suka isa d'akin suka ji ana ta kalmar shahada da kabbara, babbar kalmar data daki zuciyarsa ita ce ta"Allah yasa anyi sa'ar tafiya."
Suna shiga tare suka ganta ruf, da d'aya d'aya ya shiga kallon mutanen d'akin, yanayin kowa da furucin bakunansu ya tabbatar masa da abinda zuciyarsa ke raya masa, wani tartsatsi yaji daga kanshi har zuwa k'afarshi, kamar wani ne ya turashi sai ganinshi sukayi ya fad'i warwasss...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_64_
Da sauri Ummy tayi kanshi ta durk'usa tana duba shi, mik'ewa tayi da sauri zata fita daga d'akin saiga Amar da Jibril sun shigo da sallama, da sauri ta kallesu tace "Yawwa ku kama shi dan Allah, ina zuwa."
Fita tayi daga d'akins
su kuma suka tallabe shi suka fito dashi, a wani d'akin aka kwantar da shi Ummy duk ta rikice sai wasu likitocin ne suka diba shi suka saka masa ruwa.
*Allah mai girma*, jinjiga, girgiza, d'imuwa da zautuwa babu wanda baiyi ba, Amna dai ta tafi gidanta na gaskiya cikin sa'a, duk wanda ke d'akin a lokacin ya shida tayi kalmar shahada a matsayin kalmarta ta k'arshe a duniya, an ci kuka har an gode Allah kamar babu gobe, wasu suna son suyi dauriya amma da an kalli yaranta uwa uba Ameera sai a saka wani sabon kuka.
Hamna na zaune kan dakalin dake fuskantar cikin asibitin su Zeituna suka fito jiki a mace kowa na ta sharar hawaye, da mamaki ta taso ta tare su cikin dakusashiyar murya tace "Aunty kuma ta saka ku kuka ko? Ni bansan me yasa take haka ba, amma yanzu ya jikin nata?"
Kallon juna sukayi sai Hajia da tace "Jikin Amna yayi sauk'i Hamna."
Murmushi tayi tace "Taji sauk'i kenan Hajia?"
Sake kallon juna sukayi suka mata shiru, kallon kowane take da alamar tambaya tace "Lafiya? Wani abu ya faru ne?"
Zeinabu ce tayi k'arfin halin cewa "Hamna ciwon Amna dai ya k'are daga yau."
Kallonta take kamar irin bata gane komai a abinda take fad'a, suma duk ido suka tsura mata suga me zai faru, kusan minti d'aya tayi a haka kafin ta fara jinjina kanta, lokacin data motsa sassan jikinta ne kad'ai ta fahimci wasu sabbin hawaye masu zafi dake gangaro mata, nuna kanta tayi da yatsa kamar mai koyon magana tace "Am...na, ye..r uwata, me ya sameta?"
Hajia ce ta dafata cikin ban baki tace "Sai hak'uri Hamna, haka Allah ya so, addu'a zaki mata kinji."
Wani k'arfi ne taji ya zo mata ta tunkari d'akin da gudu, babu wanda yayi yunk'urin binta a guje sai k'wala mata kiran da suka shiga yi, a lokacin Amar da Jibril sun fito sai cikin ma'aikatan asibitin dake binsu a baya zasu tafi da gawar morgue, yanda suka ji suna k'wala mata kira gashi sunyi karo da ita a k'ofar shiga yasa Jibril k'arfin halin rik'o hannunta, da k'arfin bala'i tasa d'aya hannun ta turashi baya har yayi tangal tangal sai kuma ya tsaya cak, ta, cikin ankarewa da mazantaka Amar ya rik'ota gaba d'aya, dan inba haka yayi ba zata zille masa, k'ok'arin kubcewa ta shiga yi da wani mugun kuka da iya k'arfinta, saida ya rintse idonshi gam ya had'e yawu yayi salati ga annabi sannan yayi k'unar bak'in waken d'ora kanta a k'irjinshi amma jikinta bai had'u da na shi ba, hanya suka basu suka je wucewa da gawar, kukan kura tayi ta rik'e gadon tana shirin bud'e zanin rufar dake jikinta, wannan karan kam k'arfi yasa mata yana son b'anb'are hannunta daga jikin gadon, zubewa tayi zaune ta rik'e gadon gam tana kuka tana fad'in "Wallahi bata mutu, bata mutu ba yer uwata ku sake dubata da kyau, Amna ki tashi dan Allah karsu rufe ki kinji."
A lokacin su Hajia suka shigo suma suka fara rik'eta, da tsiya aka rabata da gadon aka turashi aka fita, daga zaunen nan tabi gadon da kallo tana zuwa k'ugunta har ta fuskanci k'ofar fitar, kuka take sosai sai Amar daya sulale ya bar wurin yana mai tausaya mata, take yaji wasu k'walla a idonshi shima daya tuna idan fa shine yau aka ce ya rasa nashi rabin jikin Ammar?.
Duk k'ok'arinsu na son su lailayeta zuwa mota su tafi gida sun kasa, sunyi juyin duniya ta k'i basu had'in kai, gashi sun dai babu mai iya d'aukarta, mai iyawa mutum d'aya ne kuma shima baisan a inda yake ba yanzu, hatta lieutenant da ya zo cikin mutuwar jiki bai iya cewa komai ba kallonsu kawai yake suna jata, zuwa Labaran ne kad'ai ya kwakwafeta ya lallab'ata ta tashi suka tafi gida.
Hamna kowa yafi tausayinta, tayi kuka kamar ita ma zata mutu, muryarta ta disashe idonta da fuskarta sun kumbura sumtum, ta k'i ci ta k'i sha sai kuka kawai, tana uwar d'akin Amna zaune rumgume da Ameera wacce yanzu ita kad'ai take yarda da ita. Hadiza da Ummy an rasa ina uwar Amna a cikinsu, dukansu sunyi juriya wajen tak'aita mata kuka,
Tunda aka kwantar dashi bai sake sanin me ke faruwa ba saida ya kwana ya hantse, tunda ya bud'a ido ya kafe wuri d'aya yana kallo, tashi yayi zaune ya sauko da k'afafunshi, kanshi na kallon k'asa yana tariyar abinda ya faru, a hankali yaji siraren hawaye na fita a idonshi, cikin zuciyarsa yake fad'in "Ta tafi? Da gaske ta tafi? Ya zanyi? Me yasa zata tafi a wannan lokacin?"
K'ofar da yaji an bud'e yasa shi d'ago kai amma bai kalli me shigowa ba, har saida suka k'araso suka tsaya kanshi suna kallonshi, a hankali Junaid yace "Ammar ya jikin na ka?"
Cikin girgiza kai yace "Ni ma ban sani ba?"
Amar ne ya zauna kan gadon yana kallonshi yace "D'an uwa, kayi hak'uri kaji, dama duk..."
Katseshi yayi da cewa "Ina take?"
Shiru sukayi na dak'ik'u kafin Jibril yace "Gidanta na gaskiya."
Lumshe ido yayi, muguwar yunwar da yake ji ce ta had'u da wani zafin zuciya da yaji ya taso mishi, dafe k'irji yayi da d'aya hannu kua yana matsar cikinshi, ba tare daya bud'e ido ba yace "Me yasa baku bari na mata kallon k'arshe ba? Ina son ganin kyakyawar fuskarta."
Dafa kafad'arshi Amar yayi yace "Kayi hak'uri Ammar, ka mata addu'a shine soyayyar da zaka nuna mata."
Jinjina kai ya shiga yi kamar k'adangare yana fad'in "To, to naji, zan mata."
Bud'a ido yayi ya zura k'afafunshi ya sauka daga kan gadon, jiri ne ya d'ebe shi yayi gefen da Junaid ke tsaye kamar zai fad'a masa, da sauri ya rik'e shi yace "Sannu, Ammar jiri ke damunka ka kwanta ka huta mana."
Amar ne ya kalleshi yace "Ina ga fa kamar harda yunwa, mu kaishi gida sai a samar masa wani abu ya ci."
Zamewa yayi daga rik'on da Junaid ya masa ya nufi k'ofa, layi yayi tare da neman fad'uwa a wurin Amar yayi saurin rik'eshi ta baya, saida ya gyara shi da kyau ya matseshi a hannunshi suka fita a d'akin.
Gashi dai zaune yana kallon mutane amma tunaninshi da hankalinshi na wani wurin daban, rayuwa bata da tabbas, ya gamsu ya rasa wani b'angare na jikinshi, ta tafi ta barsa da yaran da kullum ya kallesu zai tuna da ita, ta zauna dashi cikin aminci, tayi zama dashi zaman daya zama a tarihi a cikin rayuwarsu, ta mishi alkairin da shi dai bai ga abinda zai iya saka mata dashi ba, addu'a, addu'a ce kawai abu mai mahimmancin daya rage tsakaninshi da ita. Tun yana zama a wajen makokin har zazzab'i ya ci galaba kan shi ya kai kanshi d'akin maganinshi ya burmawa kanshi allura, anan ya kwanta kan gadon dake d'akin yana tuna ranar da Hajia ta yanke hukucin aurensu, ranar auren ta su da irin zamantakewarsu har ranar data yi nak'uda kan gadon nan da yake kwance yanzu.
_Lumshe ido yayi hawaye suka shiga sintiri kan fuskarshi, ba tare daya bud'a ido ba ya hasko ranar da yace mata "Duniya ta yanzu idan nace zan k'ara aure dan Allah ya zakiyi?"_
_Dariya ta masa tace "Ya zanyi kuwa daya wuce na tayaka k'wato zuciyar ko ma wacece har kayi nasara."_
_Had'e fuska yayi yace "Kenan ba zakiyi kishi na ba?"_
_Sajenshi ta shafa tace "Zan yi mana, amma ba irin wanda kake tunanin zan yi ba."_
D'agowa tayi tace "Na ji Amna, kiyi ta kalmar shahada a bakinki, bari na kira miki Ammar d'in."
Tashi tayi da sauri ta fita, amma tana fitowa ita ma ta tsaya cikin wani d'aki da babu kowa ta shiga rera kuka, ta d'auki kusan minti ashirin tana kuka kafin ta fita ta same shi zaune ya had'a kai da gwiwa, da sauri tace "Ammar, ka zo dan Allah Amna tana son ganinka."
Tasowa yayi daga cikin masallacin ya matso kusanta cikin layi na galabaita yace "Mama dan Allah ku rabu da ita, zafin ciwo ne ke damunta kawai."
"A'a Ammar, ka zo kawai tunda tace tana buk'atar ganinka."
Cike da kasala yace "Shikenan muje."
Juyawa tayi ya saka takalminsa ya bi bayanta, ji yake gabanshi na tsananta fad'uwa, ko da suka isa d'akin suka ji ana ta kalmar shahada da kabbara, babbar kalmar data daki zuciyarsa ita ce ta"Allah yasa anyi sa'ar tafiya."
Suna shiga tare suka ganta ruf, da d'aya d'aya ya shiga kallon mutanen d'akin, yanayin kowa da furucin bakunansu ya tabbatar masa da abinda zuciyarsa ke raya masa, wani tartsatsi yaji daga kanshi har zuwa k'afarshi, kamar wani ne ya turashi sai ganinshi sukayi ya fad'i warwasss...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_64_
Da sauri Ummy tayi kanshi ta durk'usa tana duba shi, mik'ewa tayi da sauri zata fita daga d'akin saiga Amar da Jibril sun shigo da sallama, da sauri ta kallesu tace "Yawwa ku kama shi dan Allah, ina zuwa."
Fita tayi daga d'akins
su kuma suka tallabe shi suka fito dashi, a wani d'akin aka kwantar da shi Ummy duk ta rikice sai wasu likitocin ne suka diba shi suka saka masa ruwa.
*Allah mai girma*, jinjiga, girgiza, d'imuwa da zautuwa babu wanda baiyi ba, Amna dai ta tafi gidanta na gaskiya cikin sa'a, duk wanda ke d'akin a lokacin ya shida tayi kalmar shahada a matsayin kalmarta ta k'arshe a duniya, an ci kuka har an gode Allah kamar babu gobe, wasu suna son suyi dauriya amma da an kalli yaranta uwa uba Ameera sai a saka wani sabon kuka.
Hamna na zaune kan dakalin dake fuskantar cikin asibitin su Zeituna suka fito jiki a mace kowa na ta sharar hawaye, da mamaki ta taso ta tare su cikin dakusashiyar murya tace "Aunty kuma ta saka ku kuka ko? Ni bansan me yasa take haka ba, amma yanzu ya jikin nata?"
Kallon juna sukayi sai Hajia da tace "Jikin Amna yayi sauk'i Hamna."
Murmushi tayi tace "Taji sauk'i kenan Hajia?"
Sake kallon juna sukayi suka mata shiru, kallon kowane take da alamar tambaya tace "Lafiya? Wani abu ya faru ne?"
Zeinabu ce tayi k'arfin halin cewa "Hamna ciwon Amna dai ya k'are daga yau."
Kallonta take kamar irin bata gane komai a abinda take fad'a, suma duk ido suka tsura mata suga me zai faru, kusan minti d'aya tayi a haka kafin ta fara jinjina kanta, lokacin data motsa sassan jikinta ne kad'ai ta fahimci wasu sabbin hawaye masu zafi dake gangaro mata, nuna kanta tayi da yatsa kamar mai koyon magana tace "Am...na, ye..r uwata, me ya sameta?"
Hajia ce ta dafata cikin ban baki tace "Sai hak'uri Hamna, haka Allah ya so, addu'a zaki mata kinji."
Wani k'arfi ne taji ya zo mata ta tunkari d'akin da gudu, babu wanda yayi yunk'urin binta a guje sai k'wala mata kiran da suka shiga yi, a lokacin Amar da Jibril sun fito sai cikin ma'aikatan asibitin dake binsu a baya zasu tafi da gawar morgue, yanda suka ji suna k'wala mata kira gashi sunyi karo da ita a k'ofar shiga yasa Jibril k'arfin halin rik'o hannunta, da k'arfin bala'i tasa d'aya hannun ta turashi baya har yayi tangal tangal sai kuma ya tsaya cak, ta, cikin ankarewa da mazantaka Amar ya rik'ota gaba d'aya, dan inba haka yayi ba zata zille masa, k'ok'arin kubcewa ta shiga yi da wani mugun kuka da iya k'arfinta, saida ya rintse idonshi gam ya had'e yawu yayi salati ga annabi sannan yayi k'unar bak'in waken d'ora kanta a k'irjinshi amma jikinta bai had'u da na shi ba, hanya suka basu suka je wucewa da gawar, kukan kura tayi ta rik'e gadon tana shirin bud'e zanin rufar dake jikinta, wannan karan kam k'arfi yasa mata yana son b'anb'are hannunta daga jikin gadon, zubewa tayi zaune ta rik'e gadon gam tana kuka tana fad'in "Wallahi bata mutu, bata mutu ba yer uwata ku sake dubata da kyau, Amna ki tashi dan Allah karsu rufe ki kinji."
A lokacin su Hajia suka shigo suma suka fara rik'eta, da tsiya aka rabata da gadon aka turashi aka fita, daga zaunen nan tabi gadon da kallo tana zuwa k'ugunta har ta fuskanci k'ofar fitar, kuka take sosai sai Amar daya sulale ya bar wurin yana mai tausaya mata, take yaji wasu k'walla a idonshi shima daya tuna idan fa shine yau aka ce ya rasa nashi rabin jikin Ammar?.
Duk k'ok'arinsu na son su lailayeta zuwa mota su tafi gida sun kasa, sunyi juyin duniya ta k'i basu had'in kai, gashi sun dai babu mai iya d'aukarta, mai iyawa mutum d'aya ne kuma shima baisan a inda yake ba yanzu, hatta lieutenant da ya zo cikin mutuwar jiki bai iya cewa komai ba kallonsu kawai yake suna jata, zuwa Labaran ne kad'ai ya kwakwafeta ya lallab'ata ta tashi suka tafi gida.
Hamna kowa yafi tausayinta, tayi kuka kamar ita ma zata mutu, muryarta ta disashe idonta da fuskarta sun kumbura sumtum, ta k'i ci ta k'i sha sai kuka kawai, tana uwar d'akin Amna zaune rumgume da Ameera wacce yanzu ita kad'ai take yarda da ita. Hadiza da Ummy an rasa ina uwar Amna a cikinsu, dukansu sunyi juriya wajen tak'aita mata kuka,
Tunda aka kwantar dashi bai sake sanin me ke faruwa ba saida ya kwana ya hantse, tunda ya bud'a ido ya kafe wuri d'aya yana kallo, tashi yayi zaune ya sauko da k'afafunshi, kanshi na kallon k'asa yana tariyar abinda ya faru, a hankali yaji siraren hawaye na fita a idonshi, cikin zuciyarsa yake fad'in "Ta tafi? Da gaske ta tafi? Ya zanyi? Me yasa zata tafi a wannan lokacin?"
K'ofar da yaji an bud'e yasa shi d'ago kai amma bai kalli me shigowa ba, har saida suka k'araso suka tsaya kanshi suna kallonshi, a hankali Junaid yace "Ammar ya jikin na ka?"
Cikin girgiza kai yace "Ni ma ban sani ba?"
Amar ne ya zauna kan gadon yana kallonshi yace "D'an uwa, kayi hak'uri kaji, dama duk..."
Katseshi yayi da cewa "Ina take?"
Shiru sukayi na dak'ik'u kafin Jibril yace "Gidanta na gaskiya."
Lumshe ido yayi, muguwar yunwar da yake ji ce ta had'u da wani zafin zuciya da yaji ya taso mishi, dafe k'irji yayi da d'aya hannu kua yana matsar cikinshi, ba tare daya bud'e ido ba yace "Me yasa baku bari na mata kallon k'arshe ba? Ina son ganin kyakyawar fuskarta."
Dafa kafad'arshi Amar yayi yace "Kayi hak'uri Ammar, ka mata addu'a shine soyayyar da zaka nuna mata."
Jinjina kai ya shiga yi kamar k'adangare yana fad'in "To, to naji, zan mata."
Bud'a ido yayi ya zura k'afafunshi ya sauka daga kan gadon, jiri ne ya d'ebe shi yayi gefen da Junaid ke tsaye kamar zai fad'a masa, da sauri ya rik'e shi yace "Sannu, Ammar jiri ke damunka ka kwanta ka huta mana."
Amar ne ya kalleshi yace "Ina ga fa kamar harda yunwa, mu kaishi gida sai a samar masa wani abu ya ci."
Zamewa yayi daga rik'on da Junaid ya masa ya nufi k'ofa, layi yayi tare da neman fad'uwa a wurin Amar yayi saurin rik'eshi ta baya, saida ya gyara shi da kyau ya matseshi a hannunshi suka fita a d'akin.
Gashi dai zaune yana kallon mutane amma tunaninshi da hankalinshi na wani wurin daban, rayuwa bata da tabbas, ya gamsu ya rasa wani b'angare na jikinshi, ta tafi ta barsa da yaran da kullum ya kallesu zai tuna da ita, ta zauna dashi cikin aminci, tayi zama dashi zaman daya zama a tarihi a cikin rayuwarsu, ta mishi alkairin da shi dai bai ga abinda zai iya saka mata dashi ba, addu'a, addu'a ce kawai abu mai mahimmancin daya rage tsakaninshi da ita. Tun yana zama a wajen makokin har zazzab'i ya ci galaba kan shi ya kai kanshi d'akin maganinshi ya burmawa kanshi allura, anan ya kwanta kan gadon dake d'akin yana tuna ranar da Hajia ta yanke hukucin aurensu, ranar auren ta su da irin zamantakewarsu har ranar data yi nak'uda kan gadon nan da yake kwance yanzu.
_Lumshe ido yayi hawaye suka shiga sintiri kan fuskarshi, ba tare daya bud'a ido ba ya hasko ranar da yace mata "Duniya ta yanzu idan nace zan k'ara aure dan Allah ya zakiyi?"_
_Dariya ta masa tace "Ya zanyi kuwa daya wuce na tayaka k'wato zuciyar ko ma wacece har kayi nasara."_
_Had'e fuska yayi yace "Kenan ba zakiyi kishi na ba?"_
_Sajenshi ta shafa tace "Zan yi mana, amma ba irin wanda kake tunanin zan yi ba."_