Sashe 45
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rana ta farko data fara sanin yana da yan uwa, amma bata nuna wani damuwa ba, zaune yayi a lokacin sosai yana kallonta yace "Zeeya'atu, a k'alla yanzu muna da shekara d'aya da rabi da aure, a wannan lokacin zan iya cewa ni dake bamuyi farin ciki ba, Zeeya kinyi min abubuwa da dama a gidan nan daya kamata ace na d'auki mataki akan haka, amma ban d'auka ba saboda mahaifinki ya min komai a rayuwa, amma daga ranar da kika haifo min yaran nan, na kallesu da idona na kuma tuna wahalar da kika sha wajen haihuwarsu, sai naji kin samu wani girma da matsayi a zuciyata, Zeeya'atu duk da kin k'untata min a rayuwa amma sai naji a duk duniyar nan babu mai so na da k'aunata sama dake, zee'ayatu matsololin rayuwa da muka shiga ne harya jefoni garinku, banda kowa sai yan uwa na mata biyu, wanda har yanzu d'aya daga ciki bansan ina take ba, amma sai gashi lokaci d'aya kin haifo min magada yara maza har uku..."
Rawarda muryarshi takeyi ne yasa yayi shiru ya duk'ar da kanshi, hawaye ne suka dinga zarya a fuskarshi, hakan ne yasa Zeeya jin wani abu a zuciyarta da bata tab'a ji a game dashi ba sai yau, ji take kamar ta tashi ta rarrasheshi amma kuma tana jin ba girmanta bane, saida ya gaji dan kanshi ya share hawayenshiya d'ago ya ci gaba da cewa "Tabbas kyautar daga Allah take, amma kema kinyi k'ok'ari Zeeya, ina godiya sosai ga Allah daya bani su, sannan kema ina gode miki, Allah ya saka miki da alkairinsa, Allah ya baki lafiyar da zaki shayar dasu cikin k'oshin lafiya."
Hak'ik'a maganganunshi Sun huda zuciyarta sosai ta yanda ta kasa ko motsin kirki harya fita daga d'akin, haka aka ci gaba da tafiya duk da Zeeya na jin soyayyar mijin nata amma babu abinda ta rage a game da rashin mutumci, a haka yara sukayi wata uku da haihuwa, zuwa lokacin kuma kakarta ta koma sai Fatime ke tayata kula da yaran, ana haka Suley ya shirya sake komawa ganin iyalinshi, ya so tafiya tare da Zeeya dan taga mahaifarshi ko ya tsira daga gorin da take masa, amma sai Zeeya tace ai babu inda zataje tunda babu wanda ta sani, haka yayi ban kwana dasu ya kuma bar musu duk abin buk'ata sannan ya kama hanya.
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*
😍
06/06/2020 à 12:38 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_11_
Husseina dai dama ba nisa akayi da ita ba daga gidan iyayen ta, dan daga gidan ana hangen gidan nata iyayenta, sai dai kuma a wannan rana taga tashin hankalin da bata tab'a gani ba a tsawon rayuwarta, dan wannan daren nata na farko daren tonon asiri da tashin hankali ya zamar mata, sam *Salisou* bai mata da kyau ba a wannan rana ko nace dare, domin kuwa dukan mutuwa ya mata tare da yi mata saki har uku, daga shi har ita da sauran matanshi babu wanda yayi bacci, kumfar baki kawai yake yana fad'in shi taimakonsu ne yayi ya aureta saboda ganin ta jima babu aure, ashe dai da dalili shiyasa basu samu miji ba, tunda gudun-gudun safiya ya shiga gidan mahaifiyarshi dake had'e da nashi gidan, kaf ya kwashe ya fad'a mata abinda ke faruwa, nan fa ita ma ta d'ora ta ta kalar tijarar tana sababi, abinka ga sanyin safiya da sannan duk wanda yasan unguwar d'an gulbi yasan unguwa ce da babu sarari sosai, hakan yasa kowa kamar har gidanshi akaje aka fad'a mishi saboda yanda mutane dayawa suka fito kallon k'wam, kamar a tatsuniya haka Salisou da uwarshi suka dinga watso yan kayan da aka kaiwa Husseina wacce ita kanta suka turo k'eyar ta waje, banda kuka babu abinda take kamar zata had'e zuciya ta mutu, ga shegen dukan daya mata wanda yasa jikinta yin tsami.
Labari ne ya samu mutanen gidansu suma suka fito dan jin ance da Husseina abin ke faruwa, a lokacin tana tafiya a hankali zata zo gidansu, tana zuwa k'ofar gidan Hassan ya tare k'ofa yace "Gidan nan kike nufin shiga? Ai in kinga haka ta faru to babu raina ne, dan haka tun wuri ma kisan inda dare ya miki, dan ni ba'a zina aka haife bi ba kuma duk zuri'ar mu babu mazinaci, dan haka wallahi ba zan haifi karuwa a gidana ba."
Ramma dake daga cikin soro ce tace "Alhaji haihuwar karuwa na nawa kuma, ai sai dai kar a k'ara, amma kam ka riga daka haifeta."
"Ai kuwa ba dai a gidan nan ba wallahi." Ya fad'a lokaci d'aya ya kalli Husseina da banda kuka babu abinda take yace "Zaki b'ace min da gani ko sai ci uwarki a wurin nan, k'ur'ani ba zaki shiga gidan nan ba, idan kuma uwarki ce ke saki duk iskancin to ki fad'a min saina turo miki ita ku tafi tare."
Zubewa tayi kan gwiwoyinta cikin tsananin kuka ta had'e hannayenta tace "Dan Allah Baba, dan annabi, ka dubi girman Allah ka barni na shiga ciki, Baba bana da inda zanje idan na bar nan."
"To ni ina ruwa na, wannan matsalarki ce ba tawa ba, da da kike iskancin baki tuna da irin wannan ranar ba."
Saratu na k'ofar d'akin ta tana hango duk abinda ke faruwa daga nan, kuka take tana addu'a tare da tunanin yanda akayi haka ta faru, tana cikin wannan tunani ne ta sake jin ihun Husseina wacce Ramma ta sake mik'owa Hassan wani ice daga nan soron wanda ake ajewa saboda lokacin damuna ya fara jibgarta a filin Allah yana fad'in "Kije ki yi karuwanci mana, wannan keta shafa bani ba, dama karuwar gida ce bamu sani bane."
Lokacin ne Saratu ta fito tana kuka tana bashi hak'uri, amma a k'arshe sai yace ta zab'a ko zama dashi ko da 'yarta, bud'ar bakin Saratu cewa tayi "Ita fa 'yata ce data fito daga jikina, ko ka manta da karin maganar nan da ake cewa *namiji goma ba uba goma bane*? Zanyi farin cikin k'arar da rayuwata a tare da 'ya'yana, dan haka na zab'i na tafi tare da ita duk inda zata saka k'afa."
Kama Husseina tayi amma saita sake sulalewa tana kuka tace "A'a Inna, ban cancanci ki ruguza rayuwar aurenki ba a kaina, shekararku talatin da hud'u tare, ba zan yarda yau na zama silar wargajewarshi ba, komai daya faru laifina ne."
"Nima kuma ba zan tab'a bari taki rayuwar ta lalace ba, dan ni tawa rayuwar dama ta jima da gurb'acewa tunda na shigo gidan mahaifinku, dan haka ba zan tab'a barinki ke kad'ai ba bayan bansan ina zaki je ba."
Hannayenta ta rik'e sosai tace "Inna kiyi hak'uri ki barni na tafi, na miki alk'awarin kare mutumci na, sannan zan dawo nan bada jimawa ba, Inna yanzu ran Baba a b'ace yake, zuwa lokacin da zai huce zan dawo nasan zai karb'e ni."
Sun jima suna wannan musayar yawun kafin Husseina ta saki hannunta ta fara tafiya, za tabi bayanta Hassan yace idan har ta tafi bada yawunshi ba Allah ya isa, juyowa Husseina tayi taga tabbas mahaifiyarta fa idonta sun rufe, hakan yasa ta kalli gabanta ta ari na kare da gudu ta ratsa mutanen dake kallonsu ta bar wurin, saboda a lokacin akwai kula da hakk'in mak'wabtaka yasa wani mak'wabcinsu ne ya bi bayanta ya tafi da ita gidanshi.
Kwanan Husseina *takwas* a gidan nan babu wata matsala, babu wani abu da mutanen gidan ke nuna mata na k'yama ko banbanci, duk da Saratu bata zo ta ganta ba saboda tun ranar da abun nan ya faru doka mai tsanani Hassan ya kafa mata, wanda yanzu ko abincin gidan baya bata sai Suley ne idan yayi fafutuka yake kawo mata, sai Suley ne ke ziyartar Husseina yaga halin da take ciki, haka ma yar uwarta Hassana ta zo ta ganta, ana haka kuma sai wata matsalar ta kunno kai, domin kuwa ciki ne ya bayyana jikin Husseina, bayan ta tabbatarwa da kanta tana da ciki shigar wasu watanni da suka gabata sai kawai ta yanke hukunci a kai, da asuba ta bar gidan *malam Yacub* ta shiga gari, dan a tunaninta bata da ciki ma aka wulak'anta ta bare yanzu asan tana da cikin banzan malamin nan.
Yawo take babu wurin zuwa, wanda a lokacin kud'in mota kawai take nema da zai kaita Diffa wajen dangin mahaifiyarta komai rashin dad'in can d'in zaifi mata, amma sai gashi har magriba ta mata bata ma samu abinda zata saka a bakinta ba, dan duk wanda ta nema taimako sai an mata kallon tsaf, ganinta zaune da kyau tsaye da kyau amma tana neman taimako dan mutuwar zuciya, dan haka babu wanda yayi yunk'urin taimaka mata, tana cikin yawo ta had'u da wani babban mutum ta nemi taimakonshi, amma saiya nuna mata idan ita ma zata taimaka masa saiya taimaka har da wurin kwana ma, mik'ewa tayi daga durk'ushin da tayi ta juya baya zata tafi, hawaye ne suka fara mata zarya a ido inda kalmar mahaifinta ke dawo mata a k'wak'walwa ta cewa " *Kije kiyi karuwanci mana*, wannan ke ta shafa bani ba, dama karuwar gida ce ke bamu sani bane."
Wannan maganar ita ta tsaya mata a rai sosai inda shed'an kuma ya rad'a mata tashi hud'ubar a kunne, juyowa tayi da sauri wajen mutumin ta same shi yana shirin tashin motonshi, tana zuwa yace "Ke ya dai, me kika dawo yi?"
Rawarda muryarshi takeyi ne yasa yayi shiru ya duk'ar da kanshi, hawaye ne suka dinga zarya a fuskarshi, hakan ne yasa Zeeya jin wani abu a zuciyarta da bata tab'a ji a game dashi ba sai yau, ji take kamar ta tashi ta rarrasheshi amma kuma tana jin ba girmanta bane, saida ya gaji dan kanshi ya share hawayenshiya d'ago ya ci gaba da cewa "Tabbas kyautar daga Allah take, amma kema kinyi k'ok'ari Zeeya, ina godiya sosai ga Allah daya bani su, sannan kema ina gode miki, Allah ya saka miki da alkairinsa, Allah ya baki lafiyar da zaki shayar dasu cikin k'oshin lafiya."
Hak'ik'a maganganunshi Sun huda zuciyarta sosai ta yanda ta kasa ko motsin kirki harya fita daga d'akin, haka aka ci gaba da tafiya duk da Zeeya na jin soyayyar mijin nata amma babu abinda ta rage a game da rashin mutumci, a haka yara sukayi wata uku da haihuwa, zuwa lokacin kuma kakarta ta koma sai Fatime ke tayata kula da yaran, ana haka Suley ya shirya sake komawa ganin iyalinshi, ya so tafiya tare da Zeeya dan taga mahaifarshi ko ya tsira daga gorin da take masa, amma sai Zeeya tace ai babu inda zataje tunda babu wanda ta sani, haka yayi ban kwana dasu ya kuma bar musu duk abin buk'ata sannan ya kama hanya.
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*
😍
06/06/2020 à 12:38 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_11_
Husseina dai dama ba nisa akayi da ita ba daga gidan iyayen ta, dan daga gidan ana hangen gidan nata iyayenta, sai dai kuma a wannan rana taga tashin hankalin da bata tab'a gani ba a tsawon rayuwarta, dan wannan daren nata na farko daren tonon asiri da tashin hankali ya zamar mata, sam *Salisou* bai mata da kyau ba a wannan rana ko nace dare, domin kuwa dukan mutuwa ya mata tare da yi mata saki har uku, daga shi har ita da sauran matanshi babu wanda yayi bacci, kumfar baki kawai yake yana fad'in shi taimakonsu ne yayi ya aureta saboda ganin ta jima babu aure, ashe dai da dalili shiyasa basu samu miji ba, tunda gudun-gudun safiya ya shiga gidan mahaifiyarshi dake had'e da nashi gidan, kaf ya kwashe ya fad'a mata abinda ke faruwa, nan fa ita ma ta d'ora ta ta kalar tijarar tana sababi, abinka ga sanyin safiya da sannan duk wanda yasan unguwar d'an gulbi yasan unguwa ce da babu sarari sosai, hakan yasa kowa kamar har gidanshi akaje aka fad'a mishi saboda yanda mutane dayawa suka fito kallon k'wam, kamar a tatsuniya haka Salisou da uwarshi suka dinga watso yan kayan da aka kaiwa Husseina wacce ita kanta suka turo k'eyar ta waje, banda kuka babu abinda take kamar zata had'e zuciya ta mutu, ga shegen dukan daya mata wanda yasa jikinta yin tsami.
Labari ne ya samu mutanen gidansu suma suka fito dan jin ance da Husseina abin ke faruwa, a lokacin tana tafiya a hankali zata zo gidansu, tana zuwa k'ofar gidan Hassan ya tare k'ofa yace "Gidan nan kike nufin shiga? Ai in kinga haka ta faru to babu raina ne, dan haka tun wuri ma kisan inda dare ya miki, dan ni ba'a zina aka haife bi ba kuma duk zuri'ar mu babu mazinaci, dan haka wallahi ba zan haifi karuwa a gidana ba."
Ramma dake daga cikin soro ce tace "Alhaji haihuwar karuwa na nawa kuma, ai sai dai kar a k'ara, amma kam ka riga daka haifeta."
"Ai kuwa ba dai a gidan nan ba wallahi." Ya fad'a lokaci d'aya ya kalli Husseina da banda kuka babu abinda take yace "Zaki b'ace min da gani ko sai ci uwarki a wurin nan, k'ur'ani ba zaki shiga gidan nan ba, idan kuma uwarki ce ke saki duk iskancin to ki fad'a min saina turo miki ita ku tafi tare."
Zubewa tayi kan gwiwoyinta cikin tsananin kuka ta had'e hannayenta tace "Dan Allah Baba, dan annabi, ka dubi girman Allah ka barni na shiga ciki, Baba bana da inda zanje idan na bar nan."
"To ni ina ruwa na, wannan matsalarki ce ba tawa ba, da da kike iskancin baki tuna da irin wannan ranar ba."
Saratu na k'ofar d'akin ta tana hango duk abinda ke faruwa daga nan, kuka take tana addu'a tare da tunanin yanda akayi haka ta faru, tana cikin wannan tunani ne ta sake jin ihun Husseina wacce Ramma ta sake mik'owa Hassan wani ice daga nan soron wanda ake ajewa saboda lokacin damuna ya fara jibgarta a filin Allah yana fad'in "Kije ki yi karuwanci mana, wannan keta shafa bani ba, dama karuwar gida ce bamu sani bane."
Lokacin ne Saratu ta fito tana kuka tana bashi hak'uri, amma a k'arshe sai yace ta zab'a ko zama dashi ko da 'yarta, bud'ar bakin Saratu cewa tayi "Ita fa 'yata ce data fito daga jikina, ko ka manta da karin maganar nan da ake cewa *namiji goma ba uba goma bane*? Zanyi farin cikin k'arar da rayuwata a tare da 'ya'yana, dan haka na zab'i na tafi tare da ita duk inda zata saka k'afa."
Kama Husseina tayi amma saita sake sulalewa tana kuka tace "A'a Inna, ban cancanci ki ruguza rayuwar aurenki ba a kaina, shekararku talatin da hud'u tare, ba zan yarda yau na zama silar wargajewarshi ba, komai daya faru laifina ne."
"Nima kuma ba zan tab'a bari taki rayuwar ta lalace ba, dan ni tawa rayuwar dama ta jima da gurb'acewa tunda na shigo gidan mahaifinku, dan haka ba zan tab'a barinki ke kad'ai ba bayan bansan ina zaki je ba."
Hannayenta ta rik'e sosai tace "Inna kiyi hak'uri ki barni na tafi, na miki alk'awarin kare mutumci na, sannan zan dawo nan bada jimawa ba, Inna yanzu ran Baba a b'ace yake, zuwa lokacin da zai huce zan dawo nasan zai karb'e ni."
Sun jima suna wannan musayar yawun kafin Husseina ta saki hannunta ta fara tafiya, za tabi bayanta Hassan yace idan har ta tafi bada yawunshi ba Allah ya isa, juyowa Husseina tayi taga tabbas mahaifiyarta fa idonta sun rufe, hakan yasa ta kalli gabanta ta ari na kare da gudu ta ratsa mutanen dake kallonsu ta bar wurin, saboda a lokacin akwai kula da hakk'in mak'wabtaka yasa wani mak'wabcinsu ne ya bi bayanta ya tafi da ita gidanshi.
Kwanan Husseina *takwas* a gidan nan babu wata matsala, babu wani abu da mutanen gidan ke nuna mata na k'yama ko banbanci, duk da Saratu bata zo ta ganta ba saboda tun ranar da abun nan ya faru doka mai tsanani Hassan ya kafa mata, wanda yanzu ko abincin gidan baya bata sai Suley ne idan yayi fafutuka yake kawo mata, sai Suley ne ke ziyartar Husseina yaga halin da take ciki, haka ma yar uwarta Hassana ta zo ta ganta, ana haka kuma sai wata matsalar ta kunno kai, domin kuwa ciki ne ya bayyana jikin Husseina, bayan ta tabbatarwa da kanta tana da ciki shigar wasu watanni da suka gabata sai kawai ta yanke hukunci a kai, da asuba ta bar gidan *malam Yacub* ta shiga gari, dan a tunaninta bata da ciki ma aka wulak'anta ta bare yanzu asan tana da cikin banzan malamin nan.
Yawo take babu wurin zuwa, wanda a lokacin kud'in mota kawai take nema da zai kaita Diffa wajen dangin mahaifiyarta komai rashin dad'in can d'in zaifi mata, amma sai gashi har magriba ta mata bata ma samu abinda zata saka a bakinta ba, dan duk wanda ta nema taimako sai an mata kallon tsaf, ganinta zaune da kyau tsaye da kyau amma tana neman taimako dan mutuwar zuciya, dan haka babu wanda yayi yunk'urin taimaka mata, tana cikin yawo ta had'u da wani babban mutum ta nemi taimakonshi, amma saiya nuna mata idan ita ma zata taimaka masa saiya taimaka har da wurin kwana ma, mik'ewa tayi daga durk'ushin da tayi ta juya baya zata tafi, hawaye ne suka fara mata zarya a ido inda kalmar mahaifinta ke dawo mata a k'wak'walwa ta cewa " *Kije kiyi karuwanci mana*, wannan ke ta shafa bani ba, dama karuwar gida ce ke bamu sani bane."
Wannan maganar ita ta tsaya mata a rai sosai inda shed'an kuma ya rad'a mata tashi hud'ubar a kunne, juyowa tayi da sauri wajen mutumin ta same shi yana shirin tashin motonshi, tana zuwa yace "Ke ya dai, me kika dawo yi?"