Sashe 137
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ido ta zaro tana kallonshi, duk tsoro ya bayyana tare da ita tace "Me? Ammar lab'e kake mana dama?"
Murmushi ya mata yana girgiza kai yace "Banda wannan lokacin Hajia, watak'ila Allah yasa na jini saboda akwai abinda zan iya yi akai."
"Me kaji d'in?" Ta fad'a idonta a waje, saida ya had'e dariyarshi ya kalli idonta sosai yace *"K'uruciyarki, rayuwarki ta baya Hajia, wacce babbu wanda yasan da ita sai Alhaji sai kuma ni da naji yana fad'a a cikin addu'o'inshi."*
Cikin rawar hannu ta d'oki hannunta na dama ta rufe baki da taji numfashinta na neman gagararta, a hankali a hankali ta fara lumshe idonta da taji kanta na juyawa tare da sara mata, mik'ewa yayi ya kwantar da ita kan matashi, yatsu biyu yasa ya dafa kanta inda yaga tana dafewa da hannu, bud'a jakarshi yayi ya fara dube dube, da k'arfi ya d'aga daga sunkuyawar da yayi yace "Shiit."
Da gudun bala'i ya juya ya fita, kamar wanda kura ta biyo haka yake gudu har wanda suka ganshi suka tsaya kallonshi, b'angarensu na samartaka ya shiga cikin sauri yake bud'a kowane d'aki ya shiga, d'akin magungunanshi ya shiga cikin sauri sosai ya d'auko kwalin wata allura da abin k'arin numfashi (oxygène) haka ya rumgumoshi a jikinshi ya sake fitowa da gudu.
Yana shigowa ya sameta yanda ya barta sai jan numfashi take, cikin gaggawa ya samu wuri ya aje bunburutun oxygène d'in ya jona ya saka mata, wasu allurai ya had'a yasa a ciki take wani iska ya dinga taimakawa Hajia wajen numfashi inda daga k'asa kuma wasu ruwa ke ta tafasa, k'ura mata ido yayi yana kallo sannu sannu numfashinta ya fara saisaituwa, ajiyar zuciya ya sauke tare da jawo kujerar gaban madubinta ya zauna yana kallonta, Zeituna ce ta shigo da sallama ya amsa, kallonta yayi yace "Uwa antashi lafiya?"
Tana kallon Hajia tace "Antashi lafiya? Ya kuma naga an sa ma Hajia wannan?"
Kallonta yayi shima sai kawai ya bushe da dariya yace "Kin ganta nan fa sai alamun margaya take nunawa."
Duk da tana lumshe ido bacci na son d'aukarta saida ta kalleshi, hannun dake kusa dashi ta d'aga mishi tana son kama nashi hannun, da sauri ya had'a hannunshi da na ta, da alama magana take so tayi sai kuma ta fara lumshe ido, a haka kuma bacci ya d'auke ta ya saki sannunta, haka kawai yaji ba zai iya yin nisa da ita ba a halin da take ciki, dan haka ya kira asibiti ya fad'a musu yana da wani marar lafiyar da yake dubawa, duk wanda zai gani yau a basu rendez vous da yamma.
Sosai Labaran ya mishi fad'a da nuna baiji dad'in abinda ya faru ba, Soueiba dai abinda ta fad'a mishi shine, tunda hakan ya faru da farko dai ayi hak'uri tunda ba jiya ko yau bane haka ta faru ba, sannan su rik'e yarinyar su kula da ita tunda dai dama duk yan uwa ne, a banza ma zasu iya rik'eta bare kuma jikanyarsu ce, na biyu kuma Jamila dake ikrarin ya rabu da ita suyi k'ok'ari su ga auren bai mutu saboda wannan matsalar, da haka ta kwantar masa da hankali suka fuskanci gaba.
Bai fita ko ina ba sai wayarsa da yake dannawa yana gudanar da harkokin daga nan zaune, agogon hannunshi ya kalla sannan ya kalli Hajia, tabbatarwa da yayi daga yanzu zuwa kowane lokaci zata farka yasa shi fita daga d'akin ya fito, a falo ya gansu zaune suna ta hira abinsu cikin raha, fuska a had'e ya kalleta yace "Ke had'a ma Hajia abinda zata ci, amma kada kisa arôme (d'and'ano) tare da abinsha naturel."
Kamar bata ji ba dan haka ya sake kallonta yace "Dake nake fa."
Saida ta harari gefenta ta mik'e tana fad'in "Sai kace banda suna wani wai ke, menene ma'anar ke?"
Kallonta yayi ya cije leb'en k'asa, zai matso kusanta ta rufa da sauri ta shige madafar, dariya Amna tayi ta girgiza kai tace "Naga ranar da zaku girma."
Kallonta yayi yace "Amna nine ban girma ba? Ni kike had'awa da waccen yarinyar? Ni Amna?"
Kanta yayi kamar zai mazgeta hakan yasa ta rufe fuska da hannaye cikin muryar kuka tace "Kayi hak'uri to ba kai ba, ni ita nake nufi."
Dariya yayi ya sunkuya ya sumbaceta ya juya ya koma d'akin Hajia, minti arba'in ta d'auka kafin ta shigo d'akin da sallama, d'agowa yayi yana kallonta har ta shigo ta aje farantin hannunta, juyawa tayi zata fita yace "...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_50_
"Uban waye zai zuba miki?"
Juyowa tayi ta murgud'a baki tace "Kai musaki ne?"
Tattare rigarta tayi ta tafi a guje, takon da baifi uku ba ya rik'o wuyan rigarta da k'arfi yayi baya da ita, k'ara tayi wacce tasa Hajia k'arasa bud'e idonta ta kallesu, hannu ya d'aga da niyyar kasheta da mari, amma me sai yaji ba zai iya tab'a lafiyar jikinta har haka ba, tsaki ya ma kansa kafin yasa k'arfinsa ya damk'i gashinta yana fad'in "Sa'anki ne ni?"
K'ara tayi tare da rintse ido tana k'ok'arin cire hannunshi a kanta, hannu ya d'aga kamar zai mareta, da sauri ta rik'e k'afarshi cikin kuka tace "Yi hak'uri to zanyi, zan zuba, zan zuba wallahi, dan Allah yi hak'uri."
Da k'arfi yace "Tashi to."
Tashi tayi ta dawo inda ta aje kwanukan ta fara zubawa, saida ta gama ta mik'a mishi tace "Gashi."
D'aga idonshi yayi ya mata wani kallo yace "Aje a kaina."
Saida ta turo mishi baki kafin ta aje gefen gadon, juyawa tayi saida ta bud'a k'ofar tayi shirin rufeta sannan ta zuro kai tace "Allah ya saka min cutar daka min."
Tana fad'a ta ari na kare, cikin nutsuwa ya bita da kallon rashin fahimta, cutar daya mata? Wace cutar kenan? Abinda ya faru baya ko kuma yanzu? Tab'e baki yayi ya mik'e ya kama Hajia ta tashi, saukowa tayi daga kan gadon yana rik'e da hannayenta, ta mik'e tsaye Zeituna ta shigo da sallama, da sauri ta k'araso tana kwance goyon Fatima ta aje kan gadon tace "Yah Ammar bari na kaita."
Sakinta yayi suka shiga ban d'aki shi kuma ya d'auki Fatima yana mata wasa, baki kawai ta wanko ta fitota koma ta zauna, ita ta zuba abinci ya bata da kanta ta ci tasha lemu, maganin ya bata ta bata sannan yace ta d'an zauna, amsar Fatima tayi suka fita dan aikin gabanta, kallonta yayi shima yace "Hajia nima zan tafi asibiti yanzu, dan Allah kada kiyi wasa da magunan nan."
Ya fad'a yana nuna mata su, juyawa yayi zai fita tace "Ammar zo."
Juyowa yayi ya tsaya ta nuna masa kusa da uta tace "Zauna mana."
Zaunawa yayi yana kallonta, saida ta sunkuyar da kanta tace "Ammar tun yaushe kasan da haka kuma baka fad'a ba kowa ya ji?"
Da mamaki ya kalleta yace "Subhanallah! Hajia na fad'a? Na fad'a ma wa to?"
Kallonshi tayi tace "A gani na k'iyayya na nuna maka, shiyasa nake tunanin ko zaka iya fad'a dan ka kunyata ni."
B'ata fuska yayi yace "Haba Hajia, ke fa kakata ce wacce ta haifi abun tutiyata, taya zan miki haka? Hajia duk abinda kike min gaskiya ne ina jin zafi a zuciyata, amma kuma bana rik'e ki ta yanda har zanyi tunanin d'aukar fansa a kanki ko kunyata ki, Hajia duk da kina fad'a min gaba da gaba cewa baki sona ni ban tab'a yarda ba, abu d'aya da nayi imani dashi shine babu wanda zai k'i nasa sai dai ya k'i wani halinsa."
Jinjina kai tayi alamar gamsuwa kafin tace "Tun yaushe kasan da maganar nan Ammar kuma kayi shiru?"
Murmushi yayi yace "A k'alla wata goma yanzu, wani dare ne naji yana fad'a tsakaninshi da mahalincinsa, dare ne da ni kaina ya shiga cikin tarihin rayuwata, domin abinda ya faru a daren bayan naji abinda ya fad'a ne ya tabbatar min da lallai duk abinda magabatanmu suka aikata yana iya dawowa kanmu, sannan na tabbatar da abinda ya fad'a miki yanzu cewa dole sai kin tuba Hajia, inba haka ba akwai wasu abubuwan da zaki k'ara ji nan gaba wanda a gaskiya zasu iya k'arasaki ga kushewarki."
Abun mamaki da al'ajabi, abunda ko a mafarki baiyi tsammani ba shine ya faru, Hajia Zeeya'atu, Hajia dai sarauniyar izza ji da kai tak'ama da alfahari, ita ce wai ke kuka da idonta tana rik'e hannunshi tana fad'in "Ammar ka fad'a min dan Allah me yake faruwa a cikin iyalina? Ammar na fara jin tsoro, sai nake ganin kamar shashashar uwa ce ni."
Da sauri yace "A'a Hajia, ke uwa ce tsayayya kan iyalinta, Hajia akwai wuya samun uwa kamarki, ba kowace uwa bace ke tsayawa har kan tarbiyar jikokinta ma bayan ta tarbiyaccin 'ya'yanta, kawai dai yar matsala ce aka samu daga wani wurin."
Ba tare data saki hannunshi ba tace "Ka fad'a min Ammar idan kasan wani abu dake faruwa, dan Allah ka fad'a min kaji."
Girgiza kai yayi yace "Hajia bana so hankalinki ya sake tashi, k'azantar da baki ganta ba kuma baki jita ba tsabtace a gareki."
Cikin kuka mai matuk'ar nuna nadama tace "A'a Ammar ka fad'a min zan d'auka, zunubi na ne bai kamata ya shafeku ba, nayi alk'awarin tuba ga Allah abisa cin amanar mahaifina da nayi da kuma zina, zan rok'i Allah ya yafe min zubar da cikin dana tab'a yi, dan Allah ka fad'a min Ammar ko zan samu na nemi iyalina gafara."
Murmushi ya mata yana girgiza kai yace "Banda wannan lokacin Hajia, watak'ila Allah yasa na jini saboda akwai abinda zan iya yi akai."
"Me kaji d'in?" Ta fad'a idonta a waje, saida ya had'e dariyarshi ya kalli idonta sosai yace *"K'uruciyarki, rayuwarki ta baya Hajia, wacce babbu wanda yasan da ita sai Alhaji sai kuma ni da naji yana fad'a a cikin addu'o'inshi."*
Cikin rawar hannu ta d'oki hannunta na dama ta rufe baki da taji numfashinta na neman gagararta, a hankali a hankali ta fara lumshe idonta da taji kanta na juyawa tare da sara mata, mik'ewa yayi ya kwantar da ita kan matashi, yatsu biyu yasa ya dafa kanta inda yaga tana dafewa da hannu, bud'a jakarshi yayi ya fara dube dube, da k'arfi ya d'aga daga sunkuyawar da yayi yace "Shiit."
Da gudun bala'i ya juya ya fita, kamar wanda kura ta biyo haka yake gudu har wanda suka ganshi suka tsaya kallonshi, b'angarensu na samartaka ya shiga cikin sauri yake bud'a kowane d'aki ya shiga, d'akin magungunanshi ya shiga cikin sauri sosai ya d'auko kwalin wata allura da abin k'arin numfashi (oxygène) haka ya rumgumoshi a jikinshi ya sake fitowa da gudu.
Yana shigowa ya sameta yanda ya barta sai jan numfashi take, cikin gaggawa ya samu wuri ya aje bunburutun oxygène d'in ya jona ya saka mata, wasu allurai ya had'a yasa a ciki take wani iska ya dinga taimakawa Hajia wajen numfashi inda daga k'asa kuma wasu ruwa ke ta tafasa, k'ura mata ido yayi yana kallo sannu sannu numfashinta ya fara saisaituwa, ajiyar zuciya ya sauke tare da jawo kujerar gaban madubinta ya zauna yana kallonta, Zeituna ce ta shigo da sallama ya amsa, kallonta yayi yace "Uwa antashi lafiya?"
Tana kallon Hajia tace "Antashi lafiya? Ya kuma naga an sa ma Hajia wannan?"
Kallonta yayi shima sai kawai ya bushe da dariya yace "Kin ganta nan fa sai alamun margaya take nunawa."
Duk da tana lumshe ido bacci na son d'aukarta saida ta kalleshi, hannun dake kusa dashi ta d'aga mishi tana son kama nashi hannun, da sauri ya had'a hannunshi da na ta, da alama magana take so tayi sai kuma ta fara lumshe ido, a haka kuma bacci ya d'auke ta ya saki sannunta, haka kawai yaji ba zai iya yin nisa da ita ba a halin da take ciki, dan haka ya kira asibiti ya fad'a musu yana da wani marar lafiyar da yake dubawa, duk wanda zai gani yau a basu rendez vous da yamma.
Sosai Labaran ya mishi fad'a da nuna baiji dad'in abinda ya faru ba, Soueiba dai abinda ta fad'a mishi shine, tunda hakan ya faru da farko dai ayi hak'uri tunda ba jiya ko yau bane haka ta faru ba, sannan su rik'e yarinyar su kula da ita tunda dai dama duk yan uwa ne, a banza ma zasu iya rik'eta bare kuma jikanyarsu ce, na biyu kuma Jamila dake ikrarin ya rabu da ita suyi k'ok'ari su ga auren bai mutu saboda wannan matsalar, da haka ta kwantar masa da hankali suka fuskanci gaba.
Bai fita ko ina ba sai wayarsa da yake dannawa yana gudanar da harkokin daga nan zaune, agogon hannunshi ya kalla sannan ya kalli Hajia, tabbatarwa da yayi daga yanzu zuwa kowane lokaci zata farka yasa shi fita daga d'akin ya fito, a falo ya gansu zaune suna ta hira abinsu cikin raha, fuska a had'e ya kalleta yace "Ke had'a ma Hajia abinda zata ci, amma kada kisa arôme (d'and'ano) tare da abinsha naturel."
Kamar bata ji ba dan haka ya sake kallonta yace "Dake nake fa."
Saida ta harari gefenta ta mik'e tana fad'in "Sai kace banda suna wani wai ke, menene ma'anar ke?"
Kallonta yayi ya cije leb'en k'asa, zai matso kusanta ta rufa da sauri ta shige madafar, dariya Amna tayi ta girgiza kai tace "Naga ranar da zaku girma."
Kallonta yayi yace "Amna nine ban girma ba? Ni kike had'awa da waccen yarinyar? Ni Amna?"
Kanta yayi kamar zai mazgeta hakan yasa ta rufe fuska da hannaye cikin muryar kuka tace "Kayi hak'uri to ba kai ba, ni ita nake nufi."
Dariya yayi ya sunkuya ya sumbaceta ya juya ya koma d'akin Hajia, minti arba'in ta d'auka kafin ta shigo d'akin da sallama, d'agowa yayi yana kallonta har ta shigo ta aje farantin hannunta, juyawa tayi zata fita yace "...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_50_
"Uban waye zai zuba miki?"
Juyowa tayi ta murgud'a baki tace "Kai musaki ne?"
Tattare rigarta tayi ta tafi a guje, takon da baifi uku ba ya rik'o wuyan rigarta da k'arfi yayi baya da ita, k'ara tayi wacce tasa Hajia k'arasa bud'e idonta ta kallesu, hannu ya d'aga da niyyar kasheta da mari, amma me sai yaji ba zai iya tab'a lafiyar jikinta har haka ba, tsaki ya ma kansa kafin yasa k'arfinsa ya damk'i gashinta yana fad'in "Sa'anki ne ni?"
K'ara tayi tare da rintse ido tana k'ok'arin cire hannunshi a kanta, hannu ya d'aga kamar zai mareta, da sauri ta rik'e k'afarshi cikin kuka tace "Yi hak'uri to zanyi, zan zuba, zan zuba wallahi, dan Allah yi hak'uri."
Da k'arfi yace "Tashi to."
Tashi tayi ta dawo inda ta aje kwanukan ta fara zubawa, saida ta gama ta mik'a mishi tace "Gashi."
D'aga idonshi yayi ya mata wani kallo yace "Aje a kaina."
Saida ta turo mishi baki kafin ta aje gefen gadon, juyawa tayi saida ta bud'a k'ofar tayi shirin rufeta sannan ta zuro kai tace "Allah ya saka min cutar daka min."
Tana fad'a ta ari na kare, cikin nutsuwa ya bita da kallon rashin fahimta, cutar daya mata? Wace cutar kenan? Abinda ya faru baya ko kuma yanzu? Tab'e baki yayi ya mik'e ya kama Hajia ta tashi, saukowa tayi daga kan gadon yana rik'e da hannayenta, ta mik'e tsaye Zeituna ta shigo da sallama, da sauri ta k'araso tana kwance goyon Fatima ta aje kan gadon tace "Yah Ammar bari na kaita."
Sakinta yayi suka shiga ban d'aki shi kuma ya d'auki Fatima yana mata wasa, baki kawai ta wanko ta fitota koma ta zauna, ita ta zuba abinci ya bata da kanta ta ci tasha lemu, maganin ya bata ta bata sannan yace ta d'an zauna, amsar Fatima tayi suka fita dan aikin gabanta, kallonta yayi shima yace "Hajia nima zan tafi asibiti yanzu, dan Allah kada kiyi wasa da magunan nan."
Ya fad'a yana nuna mata su, juyawa yayi zai fita tace "Ammar zo."
Juyowa yayi ya tsaya ta nuna masa kusa da uta tace "Zauna mana."
Zaunawa yayi yana kallonta, saida ta sunkuyar da kanta tace "Ammar tun yaushe kasan da haka kuma baka fad'a ba kowa ya ji?"
Da mamaki ya kalleta yace "Subhanallah! Hajia na fad'a? Na fad'a ma wa to?"
Kallonshi tayi tace "A gani na k'iyayya na nuna maka, shiyasa nake tunanin ko zaka iya fad'a dan ka kunyata ni."
B'ata fuska yayi yace "Haba Hajia, ke fa kakata ce wacce ta haifi abun tutiyata, taya zan miki haka? Hajia duk abinda kike min gaskiya ne ina jin zafi a zuciyata, amma kuma bana rik'e ki ta yanda har zanyi tunanin d'aukar fansa a kanki ko kunyata ki, Hajia duk da kina fad'a min gaba da gaba cewa baki sona ni ban tab'a yarda ba, abu d'aya da nayi imani dashi shine babu wanda zai k'i nasa sai dai ya k'i wani halinsa."
Jinjina kai tayi alamar gamsuwa kafin tace "Tun yaushe kasan da maganar nan Ammar kuma kayi shiru?"
Murmushi yayi yace "A k'alla wata goma yanzu, wani dare ne naji yana fad'a tsakaninshi da mahalincinsa, dare ne da ni kaina ya shiga cikin tarihin rayuwata, domin abinda ya faru a daren bayan naji abinda ya fad'a ne ya tabbatar min da lallai duk abinda magabatanmu suka aikata yana iya dawowa kanmu, sannan na tabbatar da abinda ya fad'a miki yanzu cewa dole sai kin tuba Hajia, inba haka ba akwai wasu abubuwan da zaki k'ara ji nan gaba wanda a gaskiya zasu iya k'arasaki ga kushewarki."
Abun mamaki da al'ajabi, abunda ko a mafarki baiyi tsammani ba shine ya faru, Hajia Zeeya'atu, Hajia dai sarauniyar izza ji da kai tak'ama da alfahari, ita ce wai ke kuka da idonta tana rik'e hannunshi tana fad'in "Ammar ka fad'a min dan Allah me yake faruwa a cikin iyalina? Ammar na fara jin tsoro, sai nake ganin kamar shashashar uwa ce ni."
Da sauri yace "A'a Hajia, ke uwa ce tsayayya kan iyalinta, Hajia akwai wuya samun uwa kamarki, ba kowace uwa bace ke tsayawa har kan tarbiyar jikokinta ma bayan ta tarbiyaccin 'ya'yanta, kawai dai yar matsala ce aka samu daga wani wurin."
Ba tare data saki hannunshi ba tace "Ka fad'a min Ammar idan kasan wani abu dake faruwa, dan Allah ka fad'a min kaji."
Girgiza kai yayi yace "Hajia bana so hankalinki ya sake tashi, k'azantar da baki ganta ba kuma baki jita ba tsabtace a gareki."
Cikin kuka mai matuk'ar nuna nadama tace "A'a Ammar ka fad'a min zan d'auka, zunubi na ne bai kamata ya shafeku ba, nayi alk'awarin tuba ga Allah abisa cin amanar mahaifina da nayi da kuma zina, zan rok'i Allah ya yafe min zubar da cikin dana tab'a yi, dan Allah ka fad'a min Ammar ko zan samu na nemi iyalina gafara."