Sashe 175
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Firgigit ta farka kamar wacce tayi mummunan mafarki, ko da ta bud'a ido juyawa tayi inda yarinyar ke kwanciya bata ganta ba, ganin lokacin sallah ma ya kusa saita ta tashi ta shiga ban d'aki tayi alwala ta dawo, har ta bud'a wajen kayanta da niyyar sake na jikinta na bacci, a hankali a hankali sai take jin kamar sautin kuka k'asa k'asa, shiru tayi tana saurarawa har dai ta fito daga d'akin, a lokacin da Ameera ta farka ta k'ara fashewa da kuka mai gadi ya ganta, matsowa yayi yana dubawa da kyau, cikin tsoron ko dai ba yarinyar bace yace "Wacece nan?"
D'aga kanta tayi ta kalleshi fuskarta duk tayi jina jina da hawaye da bacci a idonta, cike da mamaki ya sake cewa "Hajia k'arama ce? Me kike yi anan?"
Cikin kuka da maganarta bata ko fita tace tace "Wajen Ummy zani."
Sai lokacin ya saki jikinshi ya matso sosai ya fara buga k'ofar, daidai lokacin Hamna ta fito taji ana buga k'ofar, take a wurin ta sawa ranta Ammar ya dawo da Ameera ta tashi a bacci kenan, sam mantawa tayi da riga da wandon dake jikinta, wando iya gwiwa yake na sojawa ne sai rigarshi bak'a mai k'ananan hannu amma ba sirara ba, da sauri ta shiga saukowa zata nufi k'ofar sai ga Labaran shima ya fito tare da yaranshi maza ya iza k'eyarsu gaba zuwa masallaci, karo suka ci sai Kamal da shima ya fito daga nashi d'akin daga sama, rage saurinta tayi ta kalli Labaran da yace "Ina zaki tafi kike sauri haka?"
Cikin girmamawa tace "Naji ana buga k'ofa ne."
"Nan?" Ya fad'a yana nuna k'ofar, da "Eh." Ta bashi amsa tana kallo ya hanzarta zuwa ya bud'e, mai gadi ya gani tare da Ameera a hannunshi, Hamna na tsinkayarsu bata bari wani cikinsu yayi magana ba ta daka a guje ta finciko Ameera ta rumgume a jikinta, kallon fuskarta take tana share mata hawayen da har sun fara bushewa, kallon mai gadi tayi tace "Ina Abbanta yake? Daga ina ka d'aukota?"
"Wallahi nima anan na ganta ita kad'ai tana kuka, tace wajenki zata tafi."
Cike da tausayi ta kalleta tace "Abbanki ne ya kawo ki?"
Girgiza mata kai tayi hakan yasa tace "To yana ina?"
Cikin shahsek'ar kuka tace "Ban ganshi ba."
"To ya akayi kika taho nan Ameera?" Ta fad'a cikin yanayin tashin hankali, murya k'asa k'asa tace "Ban ga Abba na ba kuma ban ganki ba, shine na taho wurinki kuma k'ofar ta k'i bud'ewa."
Cikin d'aga murya kamar za tayi kuka tace "Tun yaushe Ameera? Kin jima anan d'in?"
Yarinya da babu hankali sai tace "Tun da daddare."
Zaro ido tayi da matuk'ar tsoro ta sako da hawayen tausayi tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, yanzu Ammar nan ya bar min ke kikayi kwana."
Labaran ne yace "To shiga da ita ci..." Bai gama fad'a ba ya ga Hamna ta aje Ameera ta wuce da sauri ta nufi b'angaren Ammar, Kamal ne ya kalli Labaran yace "Tonton muje muyi sallah, gobarar nan ubangiji ne kawai zai iya kashe ta."
Wucewa sukayi sallah har da mai gadi, tana zuwa da k'arfi ta bud'a k'ofar falon ta shiga, ba tsayawa komai ta tunkari k'ofar d'akin baccinshi, tana daf da kaiwa shi kuma ya bud'a ya fito zai tafi masallaci shima da doguwar riga, kamar wata zakanyar da aka cinyewa ya'yanta suna had'a ido taga shine kawai tasa k'arfinta da hannayenta ta tura shi baya da k'arfi, k'ofar d'akin ya kaiwa karo yana kallonta da mahaukacin mamakin lafiyarta.
Cikin kuka kamar an ce mata Ameera rasuwa tayi da d'aga tace "Ammar me yasa zaka min haka? Me yasa zaka bar min yarinya ta kwana a tsakar gida ita kad'ai kamar wata marar gata, me yasa baka kira ni na zo na d'auketa ba in kai ba zaka iya kai min ita ba? Haka kawai ka maidata kamar wata *marainiya*."
Cikin rashin fahimtar inda kalamanta suka dosa ya matso kusanta yace "Wace yarinyar wai? Ameera kike nufi? Amm..."
"Amma me?" Ta fad'a da k'arfi, d'orawa tayi da "Saida na kiraka nace ka kawo min ita, ko ban kira ka ba? Kasan ba zaka iya kula da ita ba shine ka k'i kawo min ita tsabar mugunta, kuma ai kasan ba wajenka suke kwana ba, amma tsabar fitina da nema na da magana ka rik'eta wajenka."
Sake matsowa yayi kusanta yace "Ke yi k'asa da muryarki, d'anki ne ni da zaki zauna kina min fad'a, dan fa yana asuba ne bana masifa a irin wannan lokacin."
"To kayi mana, na ce kayi, ni ita nake nema da kai." Duk tayi maganar ne tana turashi baya da k'arfinta, saida ta ga ya dangane da bango ta nuna shi da yatsanta mai d'auke da doguwar afaifa da bak'in lalle tace "Ya zama na k'arshe kenan da zaka k'ara k'ok'arin rabani da yarana, wannan ba samari bane da zanyi shiru idan ka shiga tsakani na dasu, akan 'ya'yana saina dafaka da ranka kuma na shanye romon."
Ido ya zaro tare da bud'e baki irin firgicin nan cike da shak'iyanci yace "Mayya ce ke dama? Yaushe kika fara cin naman mutane?"
Sama da k'asa ta daddala masa harara tace "Tun ranar da bak'in bakinka ya rairaye min k'iba ta."
Juyawa tayi zata fita yace "Ki nemi abinda ya ramar dake kankana, amma ba bakina ba, kuma nasan kema kinsan ko a ina matsalar take."
Tsayawa tayi ta juyo tace "Babban matsalata a rayuwa kai ne Ammar."
Sake juyawa tayi zata fita abinda zata iya cewa bai tab'a faruwa ba, indai kaga jikinshi a hannunta to mugunta ce zai mata, amma sai gashi ya rik'e hannunta kuma ba da k'arfi ba, hasalima yatsunta ne ya rik'e yana mammatsa su a hankali a hankali, matsowa yayi kusanta saida ya tsaya gabanta yana kallon fuskarta, tayi shiru alamar abun ya ratsata, babu wani yanayi a tare da fuskarta na bak'in ciki ko b'acin rai, fuskarta dai kamar tana bacci yanayin nutsuwa sosai.
Yana kallon fuskarta cikin yanayin fahimta shima yace "Hamna kina son yaran nan sosai, rabaki dasu abune da ba zaki ji dad'inshi ba, amma me yasa kika k'i amince da maganar iyayenmu na son had'a aurenmu?"
Da sauri ta kafe tsakiyar idonshi da kallo, kasa d'aukewa tayi kuma ba tace komai ba, shima ba tare daya rusunar da idonsa ba duk da hakan kuwa na galabaitar dashi yace "Hamna kina da girma da mahimmanci a zuciyata fiye da tunaninki, ni mai iya mallaka miki yarana ne har abada sun zama naki, amma matsalar d'aya ita ce idan kika auri wani, ba fa lallai ya barki tare da su ba kamar yanda kike so, kuma na tabbata iyayenmu ma abinda sukayi la'akari dashi kenan suka so had'a aurenmu, amma da yake mahaukaciya ce ke lamba d'aya sai kika kawo wani mai suffar yan tsaki wai shi kike so."
Har yanzu idonta na kanshi cikin taushin murya tace "Nice mahaukaciyar?"
Saida ya kawar da kansa yace "Eh mana."
A hankali ta zame hannunta daga na shi tana fad'in "Ni da kai bamu dace ba Ammar, ba zamu iya zama a inuwa d'aya ba."
Murmushi yayi yace "Tsakaninki da Allah idan na baki umarni ba zaki bi ba?"
Saida ta dafa girarta sama tace "Me zai hana ni bi, zan bi mana idan bai sab'awa Allah ba."
K'wayar idonta ya kalla yace "Tsakaninki da Allah baki jin komai a kaina?"
K'asa tayi da nata idon tace "Kamar me fa?"
D'an ja baya yayi yace "Ranar dana samu hatsari sai gashi naga tsoro fargaba da tausayi a idonki, ranar da zamu bar garin nan tare da margayiya kin d'aga murya akanta, sannan duk da abinda na miki baki iya d'aga muryarki kowa yaji ba, hasala dake ake ta rufa rufa, an fasa aurenki sau uku amma babu wanda kika damu dan an fasa shi, wannan duk menene *kan..ka...na*."
Yanda yaja sunan kankanar yau sai taji sunan ya mata dad'i a kunne, amma dan karta saduda a gabansa sai kawai ta yamutsa fuska tace "Kai kuma a yanda ka fahimci abun kenan? Gaskiya kana buk'atar ganin likita."
Rab'ashi tayi zata wuce ya bi bayanta da kallo, rintse idonshi yayi dan ba zai yarda alwalarsa ta karye ba yace "Kina mantawa da ni likitan zuciya ne ko?"
Tsayawa tayi ta juyo ta kalleshi, murmushi tayi ba tace komai ba dan haka yace "Shekaru na b'ata ina wannan karatun, matakan kare kai daga kamuwa da cuta har zuwa yanda zaka mu'amulanci marar lafiyarka duk a karance nayi shi, karki d'auka haka kawai na zama tantiri a gidan nan Hamna, komai da nake yi ina sane nake yinshi, duk abinda zanyi ina yi ne dan ya tsayawa kowa a rai yayi nishad'i da zulumi, lokuta dayawa kuma har ayi dariya, taya kike ganin ba zan karanci kowa da halin da yake ciki ba."
Takawa yayi ido rufe saida ya tabbatar ya kai gareta kafin ya bud'a ido ya wuce ta bai tsaya ba, fita yayi ya wuce masallaci ya barta tsaye, da kallo ta bishi tana takawa a hankali ta koma wajen Ameera, ya daki zuciyarta sosai amma taji haushinta kanta data yarda ya ganota, ko da yake ma ai k'arya yake yi bata jin komai a game dashi, abinda ya fad'a tayi kawai yayi dogaro da su ne dan ya kunyata ta, dan haka kawai ta share al'amarinshi.
*Ko da* ya dawo daga masallaci ya kira wayar Ummy, batan ta d'auka sun gaisa yake ce mata "Ummy Abbanmu na nan tafe zai zo d'aukarki, amma kinsan me?"
Daga b'angarenta ta amsa da "A'a saika fad'a."
Gyara tsayuwa yayi yace "...
*Allah yasa ba zugaki zaiyi ba uwarmu.*
*Alhamdulillah*
04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_68_
D'aga kanta tayi ta kalleshi fuskarta duk tayi jina jina da hawaye da bacci a idonta, cike da mamaki ya sake cewa "Hajia k'arama ce? Me kike yi anan?"
Cikin kuka da maganarta bata ko fita tace tace "Wajen Ummy zani."
Sai lokacin ya saki jikinshi ya matso sosai ya fara buga k'ofar, daidai lokacin Hamna ta fito taji ana buga k'ofar, take a wurin ta sawa ranta Ammar ya dawo da Ameera ta tashi a bacci kenan, sam mantawa tayi da riga da wandon dake jikinta, wando iya gwiwa yake na sojawa ne sai rigarshi bak'a mai k'ananan hannu amma ba sirara ba, da sauri ta shiga saukowa zata nufi k'ofar sai ga Labaran shima ya fito tare da yaranshi maza ya iza k'eyarsu gaba zuwa masallaci, karo suka ci sai Kamal da shima ya fito daga nashi d'akin daga sama, rage saurinta tayi ta kalli Labaran da yace "Ina zaki tafi kike sauri haka?"
Cikin girmamawa tace "Naji ana buga k'ofa ne."
"Nan?" Ya fad'a yana nuna k'ofar, da "Eh." Ta bashi amsa tana kallo ya hanzarta zuwa ya bud'e, mai gadi ya gani tare da Ameera a hannunshi, Hamna na tsinkayarsu bata bari wani cikinsu yayi magana ba ta daka a guje ta finciko Ameera ta rumgume a jikinta, kallon fuskarta take tana share mata hawayen da har sun fara bushewa, kallon mai gadi tayi tace "Ina Abbanta yake? Daga ina ka d'aukota?"
"Wallahi nima anan na ganta ita kad'ai tana kuka, tace wajenki zata tafi."
Cike da tausayi ta kalleta tace "Abbanki ne ya kawo ki?"
Girgiza mata kai tayi hakan yasa tace "To yana ina?"
Cikin shahsek'ar kuka tace "Ban ganshi ba."
"To ya akayi kika taho nan Ameera?" Ta fad'a cikin yanayin tashin hankali, murya k'asa k'asa tace "Ban ga Abba na ba kuma ban ganki ba, shine na taho wurinki kuma k'ofar ta k'i bud'ewa."
Cikin d'aga murya kamar za tayi kuka tace "Tun yaushe Ameera? Kin jima anan d'in?"
Yarinya da babu hankali sai tace "Tun da daddare."
Zaro ido tayi da matuk'ar tsoro ta sako da hawayen tausayi tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, yanzu Ammar nan ya bar min ke kikayi kwana."
Labaran ne yace "To shiga da ita ci..." Bai gama fad'a ba ya ga Hamna ta aje Ameera ta wuce da sauri ta nufi b'angaren Ammar, Kamal ne ya kalli Labaran yace "Tonton muje muyi sallah, gobarar nan ubangiji ne kawai zai iya kashe ta."
Wucewa sukayi sallah har da mai gadi, tana zuwa da k'arfi ta bud'a k'ofar falon ta shiga, ba tsayawa komai ta tunkari k'ofar d'akin baccinshi, tana daf da kaiwa shi kuma ya bud'a ya fito zai tafi masallaci shima da doguwar riga, kamar wata zakanyar da aka cinyewa ya'yanta suna had'a ido taga shine kawai tasa k'arfinta da hannayenta ta tura shi baya da k'arfi, k'ofar d'akin ya kaiwa karo yana kallonta da mahaukacin mamakin lafiyarta.
Cikin kuka kamar an ce mata Ameera rasuwa tayi da d'aga tace "Ammar me yasa zaka min haka? Me yasa zaka bar min yarinya ta kwana a tsakar gida ita kad'ai kamar wata marar gata, me yasa baka kira ni na zo na d'auketa ba in kai ba zaka iya kai min ita ba? Haka kawai ka maidata kamar wata *marainiya*."
Cikin rashin fahimtar inda kalamanta suka dosa ya matso kusanta yace "Wace yarinyar wai? Ameera kike nufi? Amm..."
"Amma me?" Ta fad'a da k'arfi, d'orawa tayi da "Saida na kiraka nace ka kawo min ita, ko ban kira ka ba? Kasan ba zaka iya kula da ita ba shine ka k'i kawo min ita tsabar mugunta, kuma ai kasan ba wajenka suke kwana ba, amma tsabar fitina da nema na da magana ka rik'eta wajenka."
Sake matsowa yayi kusanta yace "Ke yi k'asa da muryarki, d'anki ne ni da zaki zauna kina min fad'a, dan fa yana asuba ne bana masifa a irin wannan lokacin."
"To kayi mana, na ce kayi, ni ita nake nema da kai." Duk tayi maganar ne tana turashi baya da k'arfinta, saida ta ga ya dangane da bango ta nuna shi da yatsanta mai d'auke da doguwar afaifa da bak'in lalle tace "Ya zama na k'arshe kenan da zaka k'ara k'ok'arin rabani da yarana, wannan ba samari bane da zanyi shiru idan ka shiga tsakani na dasu, akan 'ya'yana saina dafaka da ranka kuma na shanye romon."
Ido ya zaro tare da bud'e baki irin firgicin nan cike da shak'iyanci yace "Mayya ce ke dama? Yaushe kika fara cin naman mutane?"
Sama da k'asa ta daddala masa harara tace "Tun ranar da bak'in bakinka ya rairaye min k'iba ta."
Juyawa tayi zata fita yace "Ki nemi abinda ya ramar dake kankana, amma ba bakina ba, kuma nasan kema kinsan ko a ina matsalar take."
Tsayawa tayi ta juyo tace "Babban matsalata a rayuwa kai ne Ammar."
Sake juyawa tayi zata fita abinda zata iya cewa bai tab'a faruwa ba, indai kaga jikinshi a hannunta to mugunta ce zai mata, amma sai gashi ya rik'e hannunta kuma ba da k'arfi ba, hasalima yatsunta ne ya rik'e yana mammatsa su a hankali a hankali, matsowa yayi kusanta saida ya tsaya gabanta yana kallon fuskarta, tayi shiru alamar abun ya ratsata, babu wani yanayi a tare da fuskarta na bak'in ciki ko b'acin rai, fuskarta dai kamar tana bacci yanayin nutsuwa sosai.
Yana kallon fuskarta cikin yanayin fahimta shima yace "Hamna kina son yaran nan sosai, rabaki dasu abune da ba zaki ji dad'inshi ba, amma me yasa kika k'i amince da maganar iyayenmu na son had'a aurenmu?"
Da sauri ta kafe tsakiyar idonshi da kallo, kasa d'aukewa tayi kuma ba tace komai ba, shima ba tare daya rusunar da idonsa ba duk da hakan kuwa na galabaitar dashi yace "Hamna kina da girma da mahimmanci a zuciyata fiye da tunaninki, ni mai iya mallaka miki yarana ne har abada sun zama naki, amma matsalar d'aya ita ce idan kika auri wani, ba fa lallai ya barki tare da su ba kamar yanda kike so, kuma na tabbata iyayenmu ma abinda sukayi la'akari dashi kenan suka so had'a aurenmu, amma da yake mahaukaciya ce ke lamba d'aya sai kika kawo wani mai suffar yan tsaki wai shi kike so."
Har yanzu idonta na kanshi cikin taushin murya tace "Nice mahaukaciyar?"
Saida ya kawar da kansa yace "Eh mana."
A hankali ta zame hannunta daga na shi tana fad'in "Ni da kai bamu dace ba Ammar, ba zamu iya zama a inuwa d'aya ba."
Murmushi yayi yace "Tsakaninki da Allah idan na baki umarni ba zaki bi ba?"
Saida ta dafa girarta sama tace "Me zai hana ni bi, zan bi mana idan bai sab'awa Allah ba."
K'wayar idonta ya kalla yace "Tsakaninki da Allah baki jin komai a kaina?"
K'asa tayi da nata idon tace "Kamar me fa?"
D'an ja baya yayi yace "Ranar dana samu hatsari sai gashi naga tsoro fargaba da tausayi a idonki, ranar da zamu bar garin nan tare da margayiya kin d'aga murya akanta, sannan duk da abinda na miki baki iya d'aga muryarki kowa yaji ba, hasala dake ake ta rufa rufa, an fasa aurenki sau uku amma babu wanda kika damu dan an fasa shi, wannan duk menene *kan..ka...na*."
Yanda yaja sunan kankanar yau sai taji sunan ya mata dad'i a kunne, amma dan karta saduda a gabansa sai kawai ta yamutsa fuska tace "Kai kuma a yanda ka fahimci abun kenan? Gaskiya kana buk'atar ganin likita."
Rab'ashi tayi zata wuce ya bi bayanta da kallo, rintse idonshi yayi dan ba zai yarda alwalarsa ta karye ba yace "Kina mantawa da ni likitan zuciya ne ko?"
Tsayawa tayi ta juyo ta kalleshi, murmushi tayi ba tace komai ba dan haka yace "Shekaru na b'ata ina wannan karatun, matakan kare kai daga kamuwa da cuta har zuwa yanda zaka mu'amulanci marar lafiyarka duk a karance nayi shi, karki d'auka haka kawai na zama tantiri a gidan nan Hamna, komai da nake yi ina sane nake yinshi, duk abinda zanyi ina yi ne dan ya tsayawa kowa a rai yayi nishad'i da zulumi, lokuta dayawa kuma har ayi dariya, taya kike ganin ba zan karanci kowa da halin da yake ciki ba."
Takawa yayi ido rufe saida ya tabbatar ya kai gareta kafin ya bud'a ido ya wuce ta bai tsaya ba, fita yayi ya wuce masallaci ya barta tsaye, da kallo ta bishi tana takawa a hankali ta koma wajen Ameera, ya daki zuciyarta sosai amma taji haushinta kanta data yarda ya ganota, ko da yake ma ai k'arya yake yi bata jin komai a game dashi, abinda ya fad'a tayi kawai yayi dogaro da su ne dan ya kunyata ta, dan haka kawai ta share al'amarinshi.
*Ko da* ya dawo daga masallaci ya kira wayar Ummy, batan ta d'auka sun gaisa yake ce mata "Ummy Abbanmu na nan tafe zai zo d'aukarki, amma kinsan me?"
Daga b'angarenta ta amsa da "A'a saika fad'a."
Gyara tsayuwa yayi yace "...
*Allah yasa ba zugaki zaiyi ba uwarmu.*
*Alhamdulillah*
04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_68_