Sashe 7
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zeinabou na tsaye ta rasa yanda zatayi, duk da suna zaunawa su ci abinci tare da su amma a takure suke, dan duk wanda ta kalla sai kiga tana yamutsa fuska kamar tana kallon amai, abunda ya faru kuma yanzu yasa ta rasa me zatayi, tana cikin wutsil wutsil da ido Hajia tace "Malama lafiyar tsaya mana a kai? Ki zauna mana."
Da sauri ta koma kusan Husseina ta ja kujera ta zauna, ita bata ma buk'atar cin abincin amma dan kar tayi wani laifin yasa ta zauna, Gambo na ganin k'arfe tara da arba'in da biyar ya kallesu yace "Ina ganin ni zan tafi, dan nan da minti sha-biyar za'a fara taron."
Cike da dattako Alhaji yace "To ba damuwa, Allah ya taimaka, Allah ya maku jagora a cikin al'amuranku, Allah ya kiyaye ya kau da idon mak'iya a kanku."
Shima cike da jin dad'i ya amsa da "Ameen ya Allah Abba, mun gode Allah ya saka da alkairi, Allah ya k'ara lafiya da girma."
Husseina ma addu'ar tabi shi da ita har ya mik'e tsaye, har lokacin kuma Hajia Zeeya ko kallonshi ba tayi ba, saida ya sunkuya yace "Hajia ni zan wuce, sai kuma na sake dawowa, idan da wani abu da kuke buk'ata sai ku fad'a min."
A hankali ta kalleshi tare da nuna mishi wayar dake gefe akan teburin cin abincin tace "Wayar nan ta min tsufa, ina buk'atar sabuwa, kayan d'akina ma na buk'atar a canza su."
Burinshi d'aya shi dai ya samu ya kubce ya tafi karta d'ora mishi abinda ba zai iya ba, dan haka jiki na rawa yace "Hajia wannan ai ba matsala bane, yanzu za'a canza komai kamar yanda kuke buk'ata."
Alhaji ya kalla yace "Abba ku fa ko da wani abunda kuke so?"
Murmushi yayi yace "Babu komai Harouna, Allah yayi albarka, Allah yasa ku gama da duniya lafiya."
"Ameen Abba." Ya fad'a yana kallon Husseina yace "Hajia ku fa ko da abunda kuke so?"
Ita ma kai ta girgiza tace "Ba komai wallahi Gambo, Allah ya tsare mana ku."
Da ameen ya sake amsawa, da haka ya musu sallama ya fito, yana fitowa farfajiyar gidan ya samu masu tsaron lafiyarsa su biyu sai kuma dreba, mota uku ce saita tsakiya wacce yake ciki, dreban dake d'an garin ne ya had'a da neman sak'on Hajia, cikin masu tsaronshi kuma ya tuk'a motar suka nufi wurin taron.
Abunka ga idan kud'i sun kwanta a wuri, sai gashi kayan d'aki da babbar waya sun hallara a gidan ahalin Gaga cikin awa d'aya zuwa biyu, kaya ne na gani na fad'a a ledarsu, aifa nan da nan da dreban da mai gadi tare da su Zeituna da Iya da sauran ma'aikatan aka fito da waccen kayan aka zuba sabbi, Hajia na zaune tana danna sabuwar wayarta, *takaici na d'aya ba'a fad'a min me take yawon dannawa a waya ba*, su Zeinabu da suka tsaya kan gyaran ne suka fito suka tambayeta yanda za ayi da tsofaffin kayan, cikin jiji da kai da isa da tak'ama Hajia tace "Ku har yanzu baku fahimci matsayina bane? Na gama da wannan kayan kuma, su ma waccen idan na shiga naga basu min ba zan kira shi ne kuma a sake min su."
Husseina dake zaune ita ma a falon ce tace "Ai ba wani abu ba suka ce Hajia Zeeya, suna tambayar yanda za ayi da su ne, idan kika ce su zuba shara sufa cika aikinki ne kawai na su."
Juyowa tayi kamar mai ciwon wuya ta kalleta tace "Na d'auka da su nake magana ko? Meye naki na saka min baki kuma? A gidana nake dole nayi iko da komai dake cikin gidan."
Tab'e baki kawai Husseina tayi ta kawar da kanta, kallonsu tayi tace "Kuje duk yanda kuka yi wannan matsalarku ce, idan akwai mai buk'ata ma a cikinku zata iya sakawa a nata d'akin."
Haka suka wuce da tunanin yanda zasuyi dasu, sai dai sun ci alhwashin ba zasu tab'a d'aukar ko da tsinke ne su bawa ko da wani na kusa da su bare su saka a d'akin su, dan wata rana saita goranta musu, dan haka a cikin d'akunan yara aka zuba wasu, wanda basu samu wuri ba kuma aka kai su ma'ajiyar kaya.
*Wasu awanni baya*
Ammar na shiga mota ya tayar ya tsaya bakin k'ofa yana jiran mai gadi ya bud'e masa, Amar ne ya fito tare da Ummi sai Umaima a bayansu, wani matashi ne cikin kayan soja ya matso kusan Umaimai, makulli ta bashi tace "Zan tafi tare da yah Amar, kai kaje ka dubo motar idan an gama gyaran saika d'auko." Tana fad'a ta wuce shi kuma ya bi bayanta ya fita, aikinsa kenan dama tuk'a iyalin colonel Hussein, Ummi na ganin motar Ammar tayi saurin k'arasawa ta bud'e ta zauna, da wutsiyar ido kawai ya kalleta dan yasan ta shigo ne dan ta fad'i abinda ke ranta, mai gadi na gama bud'e masa ya danna hancin motar waje ya harbata zuwa titi, ana d'aukar hanya Ummi ta kalleshi tace "Ammar hankalinka ya kwanta yanzu da aka ci mutumci na? Ka ji dad'i yanzu? To ka zuba ruwa k'asa ka sha dan farin ciki."
Shiru yayi kamar ba dashi take ba, hakan yasa ta ci gaba da cewa "Ammar ku uku na haifa a duniyar nan, amma hatta k'aramin k'aninku da kuka bashi shekaru sha takwas ya fika sanin takamata, Ammar so kake sai bak'in cikinka ya kashe ni sannan ka huta? Gaba d'aya a cikin iyali ka zama wani baud'add'e ba'a gane gabanka, burinka kullum kasa Hajia ta min rashin mutumci akan laifin da ka aikata."
Jingina tayi akan kujera ta ci gaba da cewa "Ka ci gaba dayi, kaga ranar daka tunzurata tasa mahaifinka ya sakeni sai kasa ya auro maka wata uwar, ko kuma idan na had'iye zuciya na mutu shikenan ai saiku huta."
Kallonta yayi lokaci d'aya kuma ya d'auke kan shi ya mayar kan tuk'i, kallonshi ita ma tayi cikin jin zafi saboda yayi kamar ba dashi take ba, haushi ne yasa ta kai hannu da nufin kashe shi da mari ta bayan hannu, shi kuma dama yana kallonta ta wutsiyar ido dan haka yayi saurin gocewa, kallonta yayi yace "Ummi wai meye haka dan Allah, matar nan ya kamata ace ta daina damunku fa, haba."
Da mamaki ta kalleshi tace "Ba zaka canza ba Ammar, idan kuma har akwai ranar bansan ko zan ganta ba."
Ba tare daya kalleta ba yace "Duk da kun barni na tafi aikin da raina yake so da ku da ganina ma sai kun fara addu'a, idan kuma na mutu wajen daga to fa kune zakuyi kukan mutuwa ta."
Da haka suka isa asibiti, suna zuwa Ummi ce baya shi kuma gaba, takaici ne ya rufeta ganin daga ma'aikata masu gadi da shara har zuwa malaman asibitin babu wanda ya kalla bare ya mishi magana, girgiza kai tayi a ranta tana fad'in "Da ace ba kama da mahaifinka kake ba, to ko ni kaina dana fara kokonto anya ni na haifeka."
Faran faran ta gaisa da kowa ita ma ta shiga ciki, yau ma dai kamar kullum majinyata ya fara dubawa, duk wanda ke buk'atar wani agaji na gaggawa kuma saiya rubuta abinda yake buk'ata a kaiwa secrétaire ita kuma ta had'a ka da likitan da zai duba ka, daga cikin wanda Ammar ke bayar da umarni su duba majinyatan har da mahaifiyarshi wacce a gida ita ke iko, a asibiti kuma dole sai abinda yace domin kuwa shi docteur ne ita kuma infirmière ce, dan Ammar saida ya kwashe shekara sha hud'u a *France* yana karantar *Cardiologue* kafin ya zama cikakken likitan zuciya, duk da Sa'ada ita ta so zama *doctorat* amma daya zama sai ta tsallake k'asarta taje wata k'asar yin karatu na shekara takwas sai kawai Hajia tace sam ba da ita ba, idan kuma suka ce zasuyi to ba da yawunta ba, dole ta hak'ura sai shi Ammar ya tafi, da wannan diplôme d'in ne suka samu damar bud'a asibiti ta su ta kansu.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Misalin *10:00* gwamna Gambo ya sauka babban birnin niamey, nan ma motoci ne suka iso d'aukar shi harda motar sojawa dan tsaron lafiyarsa, tun a hanya ya kira Amar ya fad'a mishi a cire kud'i a counte d'in shi ya bawa su Hamna saboda kusan wata uku bai musu aike ba, kuma gashi yanzu suna ecole ya taho, Amar da a lokacin ke tsaye gaban teburin Umaima yana d'an nuna mata wani abu daya shige mata duhu ya amsa da to, ba b'ata lokaci Hamna da Amna dake cikin aji sak'o ya shigo wayoyinsu na an turo musu da kud'i zasu iya zuwa su cira, farin ciki wurin Hamna ba magana dan dama bikin k'awar ta ake daf da farawa nan da kwana uku, har yanzu ko anko bata siya ba kuma bata damu ba dan tasan zata siya.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Misalin *12:20* dreba ya d'auko yara da daga ecole, zuwansu yayi daidai da zuwan Ammar dan sha biyu yake saukowa, wani lokaci kuma ya kan koma k'arfe hud'u ya ga wasu, wani likaci kuma sai takwas na dare, yana fitowa daga mota yaran suka dinga gaishe shi, da ido ya bi kowane yana kallo har suka shige ciki, juyawa yayi yana kalkad'a makullinshi ya nufi na su b'angaren.
*12:50* motoci uku suka tsaya k'ofar gidan, biyu daga cikin motocin na sojoji ne sai wacce ke tsakiya ita ce babba k'irar *Prado*, da sauri sojan dake tuk'a motar ya fito tare da zuro hannu ya bud'e mazaunin baya, colonel Hussein ne ya fito da k'arfin shi, yana fitowa sojojin suka k'ame suna sara mishi, saida ya kallesu ya sara musu sai suka saki na su hannu shi kuma ya wuce ciki tare da rakiyar soji biyu, saida ya kai k'ofar shiga falo suka tsaya shi kuma ya juyo ya kallesu yace "Dukanku zaku iya tafiya, amma *sajan* (sergent) Idris zai iya tsayawa." Yana fad'a ya wuce suka bishi da "Ok chef."
Da sauri ta koma kusan Husseina ta ja kujera ta zauna, ita bata ma buk'atar cin abincin amma dan kar tayi wani laifin yasa ta zauna, Gambo na ganin k'arfe tara da arba'in da biyar ya kallesu yace "Ina ganin ni zan tafi, dan nan da minti sha-biyar za'a fara taron."
Cike da dattako Alhaji yace "To ba damuwa, Allah ya taimaka, Allah ya maku jagora a cikin al'amuranku, Allah ya kiyaye ya kau da idon mak'iya a kanku."
Shima cike da jin dad'i ya amsa da "Ameen ya Allah Abba, mun gode Allah ya saka da alkairi, Allah ya k'ara lafiya da girma."
Husseina ma addu'ar tabi shi da ita har ya mik'e tsaye, har lokacin kuma Hajia Zeeya ko kallonshi ba tayi ba, saida ya sunkuya yace "Hajia ni zan wuce, sai kuma na sake dawowa, idan da wani abu da kuke buk'ata sai ku fad'a min."
A hankali ta kalleshi tare da nuna mishi wayar dake gefe akan teburin cin abincin tace "Wayar nan ta min tsufa, ina buk'atar sabuwa, kayan d'akina ma na buk'atar a canza su."
Burinshi d'aya shi dai ya samu ya kubce ya tafi karta d'ora mishi abinda ba zai iya ba, dan haka jiki na rawa yace "Hajia wannan ai ba matsala bane, yanzu za'a canza komai kamar yanda kuke buk'ata."
Alhaji ya kalla yace "Abba ku fa ko da wani abunda kuke so?"
Murmushi yayi yace "Babu komai Harouna, Allah yayi albarka, Allah yasa ku gama da duniya lafiya."
"Ameen Abba." Ya fad'a yana kallon Husseina yace "Hajia ku fa ko da abunda kuke so?"
Ita ma kai ta girgiza tace "Ba komai wallahi Gambo, Allah ya tsare mana ku."
Da ameen ya sake amsawa, da haka ya musu sallama ya fito, yana fitowa farfajiyar gidan ya samu masu tsaron lafiyarsa su biyu sai kuma dreba, mota uku ce saita tsakiya wacce yake ciki, dreban dake d'an garin ne ya had'a da neman sak'on Hajia, cikin masu tsaronshi kuma ya tuk'a motar suka nufi wurin taron.
Abunka ga idan kud'i sun kwanta a wuri, sai gashi kayan d'aki da babbar waya sun hallara a gidan ahalin Gaga cikin awa d'aya zuwa biyu, kaya ne na gani na fad'a a ledarsu, aifa nan da nan da dreban da mai gadi tare da su Zeituna da Iya da sauran ma'aikatan aka fito da waccen kayan aka zuba sabbi, Hajia na zaune tana danna sabuwar wayarta, *takaici na d'aya ba'a fad'a min me take yawon dannawa a waya ba*, su Zeinabu da suka tsaya kan gyaran ne suka fito suka tambayeta yanda za ayi da tsofaffin kayan, cikin jiji da kai da isa da tak'ama Hajia tace "Ku har yanzu baku fahimci matsayina bane? Na gama da wannan kayan kuma, su ma waccen idan na shiga naga basu min ba zan kira shi ne kuma a sake min su."
Husseina dake zaune ita ma a falon ce tace "Ai ba wani abu ba suka ce Hajia Zeeya, suna tambayar yanda za ayi da su ne, idan kika ce su zuba shara sufa cika aikinki ne kawai na su."
Juyowa tayi kamar mai ciwon wuya ta kalleta tace "Na d'auka da su nake magana ko? Meye naki na saka min baki kuma? A gidana nake dole nayi iko da komai dake cikin gidan."
Tab'e baki kawai Husseina tayi ta kawar da kanta, kallonsu tayi tace "Kuje duk yanda kuka yi wannan matsalarku ce, idan akwai mai buk'ata ma a cikinku zata iya sakawa a nata d'akin."
Haka suka wuce da tunanin yanda zasuyi dasu, sai dai sun ci alhwashin ba zasu tab'a d'aukar ko da tsinke ne su bawa ko da wani na kusa da su bare su saka a d'akin su, dan wata rana saita goranta musu, dan haka a cikin d'akunan yara aka zuba wasu, wanda basu samu wuri ba kuma aka kai su ma'ajiyar kaya.
*Wasu awanni baya*
Ammar na shiga mota ya tayar ya tsaya bakin k'ofa yana jiran mai gadi ya bud'e masa, Amar ne ya fito tare da Ummi sai Umaima a bayansu, wani matashi ne cikin kayan soja ya matso kusan Umaimai, makulli ta bashi tace "Zan tafi tare da yah Amar, kai kaje ka dubo motar idan an gama gyaran saika d'auko." Tana fad'a ta wuce shi kuma ya bi bayanta ya fita, aikinsa kenan dama tuk'a iyalin colonel Hussein, Ummi na ganin motar Ammar tayi saurin k'arasawa ta bud'e ta zauna, da wutsiyar ido kawai ya kalleta dan yasan ta shigo ne dan ta fad'i abinda ke ranta, mai gadi na gama bud'e masa ya danna hancin motar waje ya harbata zuwa titi, ana d'aukar hanya Ummi ta kalleshi tace "Ammar hankalinka ya kwanta yanzu da aka ci mutumci na? Ka ji dad'i yanzu? To ka zuba ruwa k'asa ka sha dan farin ciki."
Shiru yayi kamar ba dashi take ba, hakan yasa ta ci gaba da cewa "Ammar ku uku na haifa a duniyar nan, amma hatta k'aramin k'aninku da kuka bashi shekaru sha takwas ya fika sanin takamata, Ammar so kake sai bak'in cikinka ya kashe ni sannan ka huta? Gaba d'aya a cikin iyali ka zama wani baud'add'e ba'a gane gabanka, burinka kullum kasa Hajia ta min rashin mutumci akan laifin da ka aikata."
Jingina tayi akan kujera ta ci gaba da cewa "Ka ci gaba dayi, kaga ranar daka tunzurata tasa mahaifinka ya sakeni sai kasa ya auro maka wata uwar, ko kuma idan na had'iye zuciya na mutu shikenan ai saiku huta."
Kallonta yayi lokaci d'aya kuma ya d'auke kan shi ya mayar kan tuk'i, kallonshi ita ma tayi cikin jin zafi saboda yayi kamar ba dashi take ba, haushi ne yasa ta kai hannu da nufin kashe shi da mari ta bayan hannu, shi kuma dama yana kallonta ta wutsiyar ido dan haka yayi saurin gocewa, kallonta yayi yace "Ummi wai meye haka dan Allah, matar nan ya kamata ace ta daina damunku fa, haba."
Da mamaki ta kalleshi tace "Ba zaka canza ba Ammar, idan kuma har akwai ranar bansan ko zan ganta ba."
Ba tare daya kalleta ba yace "Duk da kun barni na tafi aikin da raina yake so da ku da ganina ma sai kun fara addu'a, idan kuma na mutu wajen daga to fa kune zakuyi kukan mutuwa ta."
Da haka suka isa asibiti, suna zuwa Ummi ce baya shi kuma gaba, takaici ne ya rufeta ganin daga ma'aikata masu gadi da shara har zuwa malaman asibitin babu wanda ya kalla bare ya mishi magana, girgiza kai tayi a ranta tana fad'in "Da ace ba kama da mahaifinka kake ba, to ko ni kaina dana fara kokonto anya ni na haifeka."
Faran faran ta gaisa da kowa ita ma ta shiga ciki, yau ma dai kamar kullum majinyata ya fara dubawa, duk wanda ke buk'atar wani agaji na gaggawa kuma saiya rubuta abinda yake buk'ata a kaiwa secrétaire ita kuma ta had'a ka da likitan da zai duba ka, daga cikin wanda Ammar ke bayar da umarni su duba majinyatan har da mahaifiyarshi wacce a gida ita ke iko, a asibiti kuma dole sai abinda yace domin kuwa shi docteur ne ita kuma infirmière ce, dan Ammar saida ya kwashe shekara sha hud'u a *France* yana karantar *Cardiologue* kafin ya zama cikakken likitan zuciya, duk da Sa'ada ita ta so zama *doctorat* amma daya zama sai ta tsallake k'asarta taje wata k'asar yin karatu na shekara takwas sai kawai Hajia tace sam ba da ita ba, idan kuma suka ce zasuyi to ba da yawunta ba, dole ta hak'ura sai shi Ammar ya tafi, da wannan diplôme d'in ne suka samu damar bud'a asibiti ta su ta kansu.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Misalin *10:00* gwamna Gambo ya sauka babban birnin niamey, nan ma motoci ne suka iso d'aukar shi harda motar sojawa dan tsaron lafiyarsa, tun a hanya ya kira Amar ya fad'a mishi a cire kud'i a counte d'in shi ya bawa su Hamna saboda kusan wata uku bai musu aike ba, kuma gashi yanzu suna ecole ya taho, Amar da a lokacin ke tsaye gaban teburin Umaima yana d'an nuna mata wani abu daya shige mata duhu ya amsa da to, ba b'ata lokaci Hamna da Amna dake cikin aji sak'o ya shigo wayoyinsu na an turo musu da kud'i zasu iya zuwa su cira, farin ciki wurin Hamna ba magana dan dama bikin k'awar ta ake daf da farawa nan da kwana uku, har yanzu ko anko bata siya ba kuma bata damu ba dan tasan zata siya.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Misalin *12:20* dreba ya d'auko yara da daga ecole, zuwansu yayi daidai da zuwan Ammar dan sha biyu yake saukowa, wani lokaci kuma ya kan koma k'arfe hud'u ya ga wasu, wani likaci kuma sai takwas na dare, yana fitowa daga mota yaran suka dinga gaishe shi, da ido ya bi kowane yana kallo har suka shige ciki, juyawa yayi yana kalkad'a makullinshi ya nufi na su b'angaren.
*12:50* motoci uku suka tsaya k'ofar gidan, biyu daga cikin motocin na sojoji ne sai wacce ke tsakiya ita ce babba k'irar *Prado*, da sauri sojan dake tuk'a motar ya fito tare da zuro hannu ya bud'e mazaunin baya, colonel Hussein ne ya fito da k'arfin shi, yana fitowa sojojin suka k'ame suna sara mishi, saida ya kallesu ya sara musu sai suka saki na su hannu shi kuma ya wuce ciki tare da rakiyar soji biyu, saida ya kai k'ofar shiga falo suka tsaya shi kuma ya juyo ya kallesu yace "Dukanku zaku iya tafiya, amma *sajan* (sergent) Idris zai iya tsayawa." Yana fad'a ya wuce suka bishi da "Ok chef."