← Book details Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 198

Sashe 66

Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tab'e baki Kb yayi yace "Shikenan, idan baka zo ba ai nasan 'yer uwarka ta zo ita, dan duka k'unshin da akayi na ganta har ma tana kirana da yayanta, na d'auka ma kai ka fad'a mata ni abokinka ne."

Ba tare daya bud'e ido ba ya d'an saka hannu ya murzasu yace "Saboda ubanka ne shugaban k'asa saina zauna ina fad'awa mutane kai abokina ne? Ni na ma tab'a fad'a maka ina da yer uwa a duniyar nan?"

Jin dariyar da Kb keyi yasa ya kashe wayar ya mik'e ya shiga wankan shi, amma yana shiga sai zuciyarshi tace mishi "Wacece kenan?"

Tunani ya fara kan wacece a cikin yan matan, wani dogon tsaki yayi jin zuciyarshi ta mishi katsalandan da fad'in "Indai ba Hamna bace can su suka sani."

Tsakin da yayi yasa yace "To ina ruwanka inma ita ce? Can ta k'arata mana, wannan dama ai kullum cikin yawon biki da gidajen k'awaye take."

A haka ya fito daga wankan ya shirya cikin bleue riga da bak'in wando, yana d'aukar makulli da waa ya fito ya tunkari wurin aje motoci, amma sai ji yayi yana son yasan wacece a wurin taron, dawowa yayi ya shiga yar farfajiyar da zata sadaka da falon Hajia, tun anan ya ga Jamila tare da Zeinabu da kuma Soueiba da kaka Husseina, wucewa yayi yana fad'in "Barka."

Inda Jamila ta bishi da "Ina wuni yah Ammar."

Kamar bai ji me tace ba haka yasa kai falon, yana shiga kuma yayi daidai da fitowar Umaima da alama bata jima da dawowa daga aikin ba wanka ne tayi, ita ma bai sake bi ta kanta ba duk da tana fad'in "Ina wuni yah Ammar."

Saida ya wuce ta murgud'a baki tace "Surukantaka da irinka ai asara ce wallahi."

Hajia na zaune kan kujerar da kullum anan kake ganinta tana kallo da remote a hannunta tana canza tasha, kallon tvn yayi ya ga film ne na turanci tsagwaronsa amma ko ta kafe tvn da ido, murmushin jin haushi yayi ya wuce yana fad'in "Ki ba kanki lafiya, ke ba ji kike ba kuma ki tsura musu ido kamar mai ganewa."

Da kallon banda lokacin ka ta bishi tace "Uwarka nake jira ta zo ta fassara min."

Wayarshi dake hannunshi ya nuna mata yace "Na kira miki ita ne tayi sauri ta k'araso?"

K'wafa tayi dan tasan yanzun sai ranta ya b'ace a banza a wofi, ganin ya tunkari sama inda d'akin su Amna yake yasa ta d'aga murya tace "Kai me zaka je yi musu a d'aki? Jarabarce ta motsa ko? To fito daga nan kaji na fad'a maka, duk gaggawar ungozuma ai ta bari a haihu."

Wani murmushin shak'iyanci ya sake mata yace " To Hajajju mutan makka banda abinki jaraba ta motsa ai dole na samu inda zan d'ura ta, addu'arki kawai nake buk'ata ina zurawa na zura kan daidai ta yanda ba zan fito daga d'akin nan ba saina samo miki sabon shalele, ko ba komai kinga kya rabu da waccen gardin da kike kira shalele."

Hajia rasa amsar da zata bashi tayi sai kawai tace "Zan iya d'aga maka k'afa kan duk iskancin da zakayi a gidan nan, amma wallahi karka kuskura kayi gigin kawo min d'an gaba da fatiha, ba zan lamunci haka ba, kuma dama na jima da sanin cewa kana hassadar soyayyar da nakewa shalele, ka ka ci kanka wallahi."

K'ala baice mata ba ya k'arasa ya bud'a k'ofar d'akin kawai ya shiga ba tare da neman izini ba, Amna da fitowarta daga wanka kenan tana zaune bakin gado zata shafa mai, duk da towel d'in jikinta kakkaura ne kuma ya sauko har kan gwiwarta, amma tsananin tsoratar da tayi ba kad'an bace, yanda ya shigo d'akin take mamaki, a saninta dai anyiwa samarin gidan kashedi (interdit) da shiga d'akin yan matan haka kawai, suma kuma yan matan basa zuwa b'angaren su saida dalili, shi kanshi saida ya shigo d'in yaji yayi nadamar shigowa, dan kuwa mutanen k'asan nan da Hamna ta so tayarwa tunda safe sune yanzu Amna ta tayar daga kwanciyarsu, amma dayake masifa ce ta kawo shi sai yayi kamar bai wani damu ba ko yasa abun a kai, k'arasowa yayi ya rufe k'ofar ya tsaya gabanta, Amna data kasa tashi sunkuyar da kai tayi gabanta na bala'in bugawa da k'arfi, wata irin tsayuwar rashin d'a'a ce ya mata ta yanda da zai sunkuyo to fa kansu na iya had'uwa, tun daga nan ya tabbatarwa kanshi da Hamna ce dan wani lokacin baka iya tantance su duk da akwai d'an banbanci amma ba mai yawa ba, amma danya kamata sai yace "Ina Kankana."

Wani irin zabura da taji zuciyarta tayi yasa ta d'an dafe k'irjin ta ta rintse ido, cije hak'oranta tayi a ranta tace "Shikenan Hamna kinja min masifa ina zamana, da nasan shi zai nemeki wallahi da ban yarda da abinda kika fad'a min ba, ohh ni, *tawa ta same ni*."

Wani tsinannen rank'washi (k'ozo) ne daya sakar mata a kai har saida taji jinin al'adarta ya bulbulo da k'arfi, cikin d'aga murya yace "Ba dake nake magana ba, 'yar banza kai mai zubin mage, kina ji ina magana zaki min shiru." Dafe kai tayi ta fashe da kuka bilhakk'i tana fad'in "To yah Ammar ai..."

Shirun da tayi yasa yace " Ai me? Fad'i ina jinki ko na cire miki hanci yanzun nan."

Cikin kukan tare da d'aga murya dan ta samu mai kawo mata agaji tace "Ni ce fa."

Sunkuyawa yayi ya lek'a fuskarta hakan kuma yasa har saida numfashinsu ya gauraya, dayake ta gama wanke bakinta ne ta fito kuma ta d'auki turaren baki mai fitar da k'amshin ayaba yasa kamar ya cabki bakinta ya tsotsa, ita kuma d'an kawar da kanta tayi gefe, cikin wata irin murya yace "Ke ce kankana kike nufi?"

D'aga kai tayi da sauri alamar eh, jinjina kai yayi dake nufin ok zaki sha mamaki, mik'ewa yayi daga sunkuyon yasa hannu ya fara cire d'amarar k'ugunshi (bel, ceinture), a matuk'ar firgice ta kalleshi dan ganin me yale shirin yi, yana zage shi gaba d'aya ta zabura ta mik'e zata zuba a guje, hannunta ya rik'o tare da wurgata kan gadon ta fad'a kwaram, a lokacin ne kuma idonshi suka sauka kan jinin daya d'an fara b'ata zanin gadon, dan ko audigarta bata saka ba ta tsaya shafa mana, wani tarrr yayi da idonshi ya nuna mata wurin da yatsa yace

"Ita sarauniyar shan kankanar nasan dai aman ruwa take🙆‍♀️, ke kuma kenan na jini kike?"

Girgiza kai tayi ba tare data daina kukan nan ba, sake dungure mata kai yayi yace "Dan ubanki ki min shiru, magana ce fa kawai muke ban kai ga dukanki ba."

Tsaf ta had'iye kukan tana wik'i-wik'i da ido, d'orawa yayi da "Amna ni k'aramin yaro ne?"

Kai ta girgiza mishi da haka yace "To meyasa zakiyi tunanin raina min hankali? Shin kinsan tayaya d'azu nasan cewa kina fashin sallah?"

Ita dai da kai kawai take amsa mishi, ci gaba da cewa yayi "Shine har zaki nuna min kanki a matsayin kankana, kenan ni sakarai ne mahaukaci? Haka ranar ma tayi shiga irin taki taje min dan na bata wayarta, shine yanzu ma ta fita daga gidan da niyyar idan wani ya tambayeta kice ita ce anan ke kuma a can."

D'aga belt d'in yayi da niyyar tsorata ta kawai, amma Amna da tsoro ya mata waya sai tayi wuf da Ammar ta rirrik'e rigarshi ta d'ora kanta a k'irjin shi tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri."

_Ai ko malam ko uba zai dakeka kayi wuf da shi to ka gama dasu aradu, bare wani Ammar😏, nifa wannan karan bana yinka._

Sanyin da jikinshi yayi yasa shi sakin belt d'in bai shirya ba, lumshe ido yayi saboda tula tulan nonuwanta da suka zauna daram kan k'irjin shi, take yaji daga k'asa anyi wani ziiiiiii da yasa shi cewa "Ya salam."

Ba tare daya bud'a ido ba cikin kasalalliyar murya yace "Amna ya kike so dani? Na mutu?"

Jin wata tattausan murya da bata tab'a ji ba yasa ta d'ago kanta, da sauri ta matsa baya ta saki rigarshi a d'an tsora ce, k'asa tayi da kanta cikin muryar kukan shagwab'a tace "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri karka dake ni, wallahi ba laifi na bane, Hamna ce tace nayi inba haka ba wai saita ja min matsala wajen Hajia, kuma ni nasan zata iya saboda tana yin kamar ni wani lokacin tayi abu."

D'ago kai tayi ta kalleshi, duk da wani sabon yanayi ta gani a tare dashi, ya wani saki ido dabaki yana kallonta kamar ya fizgota jikinshi amma haka ta daure ta sake marairaicewa tace "Kayi hak'uri dan Allah, ba zan sake ba."

Belt d'in shi ya nuna mata da ido yace "Mik'o min."

Da sauri ta d'auka amma da zata mik'a mishi saida ta ja baya, karb'a yayi tana kallo harya mayar a k'ugunshi, cikin amon muryar data kasa fahimta yace "Ai nasan inda take, zanje can na sameta na yanka mata kazar wahala sannan na d'auko ta."

Juyawa yayi da sauri harya bud'e k'ofa kuma ya juyo ya kalleta yace "Wallahi na bada baya kika kuskura kika kira kankana kika fad'a mata ina zuwa, hummm."

Saida ya gyara tsayuwa yace "Kinsan me zan miki?" A hankali ta girgiza kai, ba yanayin wasa a fuskarshi yace "Wallahi zaune zanyi na b'ata lokaci wajen cire miki duk sinadaran dake jikinki, kin gane?"

D'aga kai tayi kawai almar eh amma ba tare data fahimci sinadaren da yake nufi ba, yana fita ta sauke ajiyar zuciya tace "Yanzu da shine ake nufin nayi rayuwar aure? Amma tayaya?"

Yana fita baibi ta kan Hajia ba ya fice daga gidan ya nufi hotel d'in dan d'aukar Hamna...

*Bébé Abdul latif ba lafiya, addu'arku masoya*👏
17/06/2020 à 11:45 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨
*BADAK'ALA*
👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦

🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_18_
Chapter 66 · 0% Book details