Sashe 89
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rintse ido yayi sosai hawaye wasu na bin wasu, yana kallo ta fita ta bar d'akin yana kuka kamar yaro na goye, ranar dai kamar yanda masu hidima basuyi bacci ba haka ma Hamna da tasha d'inki tana ta wani sabon kukan Ummy na rarrashi, Ammar ma kwana yayi yana kuka yana ji kamar ya kashe kanshi, amma tunani biyu ya hanashi aikata hakan, na farko ba shi ba rahamar ubangiji, na biyu kuma mahaifiyarshi yana da yak'inin ba zai samu addua'r ta ba ko bayan ba ranshi, dan haka ya bawa kanshi hak'uri sai dai kalamanta sun matuk'ar tsaya masa a rai fiye da kima.
*Washe gari* yan makaranta sun so su zauna wai tunda ana biki gidansu, amma aka ce su tafi har su dawo, Jamila da Umaimah ma drebansu ne ya aje kowace wajen sagbarta, tun a d'aki Amna ke faman yi wa Hamna magana amma tayi shiru, yanzun fa suna fitowa tace mata "Hamna yau fa a motonki zamu tafi dan ni nawa baida isashen lafiya."
Shiru ta mata ta wuce kawai tana sauka daga matakala, Amna da zuciya sai tayi hushi ta taho da sauri ta wuce ta tana fad'in "Kada Allah yasa ki min magana kiga idan ban rayu ba, ni zaki d'auka yar iska tun daren jiya da kike shigo nake miki magana kin min shiru, aikin banza kawai."
Da kallo kawai Hamna ta bita wacce take tafiya da k'yar, dan ko yanzu ma saida tasha gashin jikinta tare da magungunan da Ummy ta bata, duk da auren babban mutum ne kuma a k'urarren lokaci, amma hakan bai hana gidan fara d'aukar hayaniyar jama'a ba tunda harka ce ta masu kud'i, hakan yasa yau Hajia bata falon zaune kowa ya tafiyarshi ba tare daya gaisheta ba, Amna na fita b'angaren samari ta nufa da fad'a mishi zata tafi, Hamna ma na fitowa a farfajiya suka had'u da Ummy suna ta kai da kawowa, tayi bala'in kyau cikin tsadadden leshenta daya dace da kalar jikinta, tarbenta Ummy tayi ta shafa fuskarta wacce zaka fahimci yanayin damuwa da kuka a tare da ita, cikin sanyin jiki Ummy tace "Hamna har yanzu kina jin ciwo ne?"
Idan tace a'a k'arya tayi, idan tace eh ma k'arya ta fad'a, dan haka kawai tayi shiru tana kallon k'asa, wasu hawaye ne sukayi barazanar taho mata ta dafata tace "Kiyi hak'uri kinji Hamna, insha Allahu zai bari, yanzu ki saki fuskarki dan Allah ki d'anyi fara'a, duk da nasan dai an rabaki da farin cikinki kenan har abada, amma...Hamna kiyi hak'uri dan Allah dan annabi, ki yafe mana."
Haka Ummy ta k'arasa maganar da fashewa da kuka, jin ba dad'i yasa Hamna kallonta ita ma idonta jawur tace "Dan Allah Ummy ki daina kuka kema, Ummy ba kiyi min komai ba wallahi, ba komai zanyi murmushi, kin gani?"
Kallonta tayi ita ma tayi murmushin kamar dai yanda tayi sannan tace "Ki kula da kanki kinji, ku je Allah ya bada sa'a."
Wucewa tayi ta nufi wajen motonta, sai dai ina tana hawa taji wani bala'i daga k'asanta kamar ana sukarta saboda d'inkin da aka mata, sauka tayi kawai ta fita daga gidan ta samu adaidaita ta hau.
Amna ma na shiga sallama tayi amma shiru, Jamil dake shirin fita ne ya amsa mata suka gaisa kafin tace "Yah Ammar yana ciki ne?"
Cikin rashin sani yace "Eh to, gaskiya ban sani ba, amma bari na duba miki."
K'wank'wasa k'ofar yayi tare da "Yah Ammar, kana ciki kuwa?"
Ammar daya ji buga k'ofar ya taso ya bud'e dan k'ok'arin kawar da damuwarshi, Amna dake tsaye a bayansu kawar da kanta tayi dan tun towel d'in nan na jiya ne a jikinshi, juyowa Jamil yayi yace "Ga mai son ganinka can."
Kallon Amna yayi wacce kanta ke kallon wani wurin, ficewa Jamil yayi shi kuma ya kafeta da ido, jin shiru yasa ta d'an sunkuya tace "Ina kwana yah Ammar."
Cikin wata irin murya yace "Amna da wata matsala ne? Ko makaranta zaki tafi?"
Ba tare data kalleshi ba tace "Eh yah Ammar, dama na zo ne na fad'a maka."
Cikin matuk'ar sanyin jiki yace "Ok kije kawai, Allah ya bada sa'a, ba zan fita ba yau dana sauke ki da kaina."
Saida ta d'ago ta kalleshi saboda mamakin yanda yake mata magana cikin taushi kamar ba shi ba, jinjina kai tayi tace "Ba komai yah Ammar, sai anjima."
Juyawa tayi ta fita ita ma akan motonta ta tafi duk da yana da yar matsala, yayin da shima ya koma ciki ya sake kwantawa ya duk'ufa tunani, yana haka kiran Hajia ya shigo wayarshi, bugawar zuciyarshi ne ya tsananta yayin da gabanshi ya fara dukan tara tara, me zaisa Hajia ta kirashi bayan rabon daya ga kiranta a wayarshi tun yana France, shima idan tana son ya aiko mata da wani abu ne, mik'ewa yayi jiki a sanyaye ya zauna yana ci gaba da kallon lambar, saida kiran yayi daf da tsinkewa kafin ya d'auka ya d'ora a kunne yayi shiru, cikin yanayin rashin mutumci tace "Sai kaga dama zaka d'aga wayar ko?"
Shiru ya sake mata kafin tace "...
*Insha Allah page 25 sai nan da wani lokacin idan Allah ya bud'i ido lafiya, ina buk'atar addua'r ku.*👏
09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_25_
"Tv ta nake buk'ata ka kawo min yanzu yanzun nan, idan kuma ba haka ba wallahi sai nasa ubanka ya siyo min tv guda goma ya zube min su gabana."
Tana gama fad'a ta kashe wayar, lumshe ido yayi tare da sauke ajiyar zuciya, aje wayar yayi gefe ya mik'e a kasalance ta fad'a bayi dan yin wanka, bai wani d'auki lokaci ba ya fito ya shirya cikin shadda kalar chocolat da tasha d'inki da chocolat zare had'e da kalar ruwan madara, ba hula a kanshi sai takalman kalar ruwan madara da agogo duk da dai tafi takalmin haske, turarenshi ya d'auka *Dolby* ya fesa kafin ya d'auki wayarshi da makullin d'aki dana mota ya fito, kai tsaye wajen aje motoci ya nufa ya kuma bar gidan, saida ya fara siyan sabuwar tv a wajen wani daya sani ya bayar a kai gidan kafin ya wuce asibiti.
Sunyi mamakin ganinshi da safe a asibiti dan duk ranar juma'a sai k'arfe *02:00* yake shiga ofishinshi, yana zuwa ya shiga ciki ya rufe da makulli ya zauna, take abubuwan da suka faru jiya suka shiga dawo masa a kai, cikin zuciyarshi ya tambayi kanshi da "Ko a wane hali take yanzu? Ta tafi makarantar ne? Shin zata iya jarabawar ma?"
Ta wani b'angaren kuma tunanin tattunawarshi da mahaifiyarsu yake, ya aunty Hadiza zatayi idan tasan abinda ya faru? Da wane ido zai kalleta ya mata bayani? Wace irin d'auka zata mishi? Wannan tunanin shine suka tayashi hira har tsawon wani lokaci, yana cikin wannan tunanin agogon dake jikin bangon ta sanar dashi k'arfe *12:00* daidai na rana, sosai ya jima yana mamakin yanda lokacin yayi sauri haka, a hankali ya mik'e ya d'auki makullan ya fito, ba tare da kula kowa ba ya fice duk da likitocin na gaisheshi da girmamawa, yana shiga motar gida ya koma da niyyar kwantawa, amma yana shiga a wajen aje motocin ya samu mata zaune harda Ummy ma a cikinsu, fitowa yayi a raunane yana kallonta amma tana d'aga kai suka kalli juna ta wurga masa harara tare da had'e rai, takowa ya farayi da niyyar yau dai zai gaisheta harda ma k'awayen ta, amma Ummy na ganin ya nufesu ta mik'e kamar wacce aka tsikara ta nufi hanyar falon Hajia, cak ya tsaya yana kallonta da matuk'ar rauni a tare dashi, tahowa yayi da niyyar shiga b'angaren su saiya hangi Amar ya fito daga falon Hajia, baiyi mamakin ganinshi ba dan duk samarin suna zuwa gida dan shirin zuwa masallaci, abun daya sosa zuciyarshi shine ganin Ummy tare dashi tana ta faman b'alla masa botiran rigarshi ta shadda wacce ke nuna yayi shirin zuwa masallaci da d'aurin auren babansu, da kanta ta karb'i machette d'in shi ta saka mishi tare da gyara masa zaman hula, cikin gaggawa Amar ya wuce yana fad'in "Ummy sai mun dawo."
Hannu ta d'aga masa tana fad'in "A dawo lafiya shalelen Hajia."
Wani murmushi Ammar yayi da shi kanshi baisan manufa ko fassararshi ba tare da juyawa ya koma motarshi, zai tayar Amar ya k'araso ya buga gilashin motar, saukewa yayi ba tare daya kalleshi ba shi kuma yace "Wai har ka shirya ne?"
D'ago ido yayi ya kalleshi take kuma ya d'auke idonshi, a haka Amar ya sake cewa "Ammar Abba fa yace muje da wuri masallacin, kuma kai na ga yanzu ga shigo."
Tayar da motar yayi yana cikin d'aga gilashin shi yace "Tunda dai kaje ai ba sai naje ba." Yana fad'a yayi baya baya ya daidaita hancin motar kan k'ofar fita ya fice, girgiza kai Amar yayi shima ya shiga tashi motar ya fice.
Tun a hanya ya saka a ransa zai ci gaba da zama a yanda yake, Ammar d'in sa, ba zai bari wannan damuwar ta canza shi ba, tunda dai ba zasu fahimci nadamarshi ba bare su bashi damar neman gafararsu, to kawai zai nuna kamar babu wani abu daya faru, sannan ya murje idonshi ya kalli kowa kamar yanda yake kallonsu a baya, da wannan ya isa makarantar su Hamna wanda ya samu d'alibai nata fitowa daga cikin makarantar, ta cikin gilashi ya k'urawa k'ofar ido yana jiran fitowarsu.
*Washe gari* yan makaranta sun so su zauna wai tunda ana biki gidansu, amma aka ce su tafi har su dawo, Jamila da Umaimah ma drebansu ne ya aje kowace wajen sagbarta, tun a d'aki Amna ke faman yi wa Hamna magana amma tayi shiru, yanzun fa suna fitowa tace mata "Hamna yau fa a motonki zamu tafi dan ni nawa baida isashen lafiya."
Shiru ta mata ta wuce kawai tana sauka daga matakala, Amna da zuciya sai tayi hushi ta taho da sauri ta wuce ta tana fad'in "Kada Allah yasa ki min magana kiga idan ban rayu ba, ni zaki d'auka yar iska tun daren jiya da kike shigo nake miki magana kin min shiru, aikin banza kawai."
Da kallo kawai Hamna ta bita wacce take tafiya da k'yar, dan ko yanzu ma saida tasha gashin jikinta tare da magungunan da Ummy ta bata, duk da auren babban mutum ne kuma a k'urarren lokaci, amma hakan bai hana gidan fara d'aukar hayaniyar jama'a ba tunda harka ce ta masu kud'i, hakan yasa yau Hajia bata falon zaune kowa ya tafiyarshi ba tare daya gaisheta ba, Amna na fita b'angaren samari ta nufa da fad'a mishi zata tafi, Hamna ma na fitowa a farfajiya suka had'u da Ummy suna ta kai da kawowa, tayi bala'in kyau cikin tsadadden leshenta daya dace da kalar jikinta, tarbenta Ummy tayi ta shafa fuskarta wacce zaka fahimci yanayin damuwa da kuka a tare da ita, cikin sanyin jiki Ummy tace "Hamna har yanzu kina jin ciwo ne?"
Idan tace a'a k'arya tayi, idan tace eh ma k'arya ta fad'a, dan haka kawai tayi shiru tana kallon k'asa, wasu hawaye ne sukayi barazanar taho mata ta dafata tace "Kiyi hak'uri kinji Hamna, insha Allahu zai bari, yanzu ki saki fuskarki dan Allah ki d'anyi fara'a, duk da nasan dai an rabaki da farin cikinki kenan har abada, amma...Hamna kiyi hak'uri dan Allah dan annabi, ki yafe mana."
Haka Ummy ta k'arasa maganar da fashewa da kuka, jin ba dad'i yasa Hamna kallonta ita ma idonta jawur tace "Dan Allah Ummy ki daina kuka kema, Ummy ba kiyi min komai ba wallahi, ba komai zanyi murmushi, kin gani?"
Kallonta tayi ita ma tayi murmushin kamar dai yanda tayi sannan tace "Ki kula da kanki kinji, ku je Allah ya bada sa'a."
Wucewa tayi ta nufi wajen motonta, sai dai ina tana hawa taji wani bala'i daga k'asanta kamar ana sukarta saboda d'inkin da aka mata, sauka tayi kawai ta fita daga gidan ta samu adaidaita ta hau.
Amna ma na shiga sallama tayi amma shiru, Jamil dake shirin fita ne ya amsa mata suka gaisa kafin tace "Yah Ammar yana ciki ne?"
Cikin rashin sani yace "Eh to, gaskiya ban sani ba, amma bari na duba miki."
K'wank'wasa k'ofar yayi tare da "Yah Ammar, kana ciki kuwa?"
Ammar daya ji buga k'ofar ya taso ya bud'e dan k'ok'arin kawar da damuwarshi, Amna dake tsaye a bayansu kawar da kanta tayi dan tun towel d'in nan na jiya ne a jikinshi, juyowa Jamil yayi yace "Ga mai son ganinka can."
Kallon Amna yayi wacce kanta ke kallon wani wurin, ficewa Jamil yayi shi kuma ya kafeta da ido, jin shiru yasa ta d'an sunkuya tace "Ina kwana yah Ammar."
Cikin wata irin murya yace "Amna da wata matsala ne? Ko makaranta zaki tafi?"
Ba tare data kalleshi ba tace "Eh yah Ammar, dama na zo ne na fad'a maka."
Cikin matuk'ar sanyin jiki yace "Ok kije kawai, Allah ya bada sa'a, ba zan fita ba yau dana sauke ki da kaina."
Saida ta d'ago ta kalleshi saboda mamakin yanda yake mata magana cikin taushi kamar ba shi ba, jinjina kai tayi tace "Ba komai yah Ammar, sai anjima."
Juyawa tayi ta fita ita ma akan motonta ta tafi duk da yana da yar matsala, yayin da shima ya koma ciki ya sake kwantawa ya duk'ufa tunani, yana haka kiran Hajia ya shigo wayarshi, bugawar zuciyarshi ne ya tsananta yayin da gabanshi ya fara dukan tara tara, me zaisa Hajia ta kirashi bayan rabon daya ga kiranta a wayarshi tun yana France, shima idan tana son ya aiko mata da wani abu ne, mik'ewa yayi jiki a sanyaye ya zauna yana ci gaba da kallon lambar, saida kiran yayi daf da tsinkewa kafin ya d'auka ya d'ora a kunne yayi shiru, cikin yanayin rashin mutumci tace "Sai kaga dama zaka d'aga wayar ko?"
Shiru ya sake mata kafin tace "...
*Insha Allah page 25 sai nan da wani lokacin idan Allah ya bud'i ido lafiya, ina buk'atar addua'r ku.*👏
09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_25_
"Tv ta nake buk'ata ka kawo min yanzu yanzun nan, idan kuma ba haka ba wallahi sai nasa ubanka ya siyo min tv guda goma ya zube min su gabana."
Tana gama fad'a ta kashe wayar, lumshe ido yayi tare da sauke ajiyar zuciya, aje wayar yayi gefe ya mik'e a kasalance ta fad'a bayi dan yin wanka, bai wani d'auki lokaci ba ya fito ya shirya cikin shadda kalar chocolat da tasha d'inki da chocolat zare had'e da kalar ruwan madara, ba hula a kanshi sai takalman kalar ruwan madara da agogo duk da dai tafi takalmin haske, turarenshi ya d'auka *Dolby* ya fesa kafin ya d'auki wayarshi da makullin d'aki dana mota ya fito, kai tsaye wajen aje motoci ya nufa ya kuma bar gidan, saida ya fara siyan sabuwar tv a wajen wani daya sani ya bayar a kai gidan kafin ya wuce asibiti.
Sunyi mamakin ganinshi da safe a asibiti dan duk ranar juma'a sai k'arfe *02:00* yake shiga ofishinshi, yana zuwa ya shiga ciki ya rufe da makulli ya zauna, take abubuwan da suka faru jiya suka shiga dawo masa a kai, cikin zuciyarshi ya tambayi kanshi da "Ko a wane hali take yanzu? Ta tafi makarantar ne? Shin zata iya jarabawar ma?"
Ta wani b'angaren kuma tunanin tattunawarshi da mahaifiyarsu yake, ya aunty Hadiza zatayi idan tasan abinda ya faru? Da wane ido zai kalleta ya mata bayani? Wace irin d'auka zata mishi? Wannan tunanin shine suka tayashi hira har tsawon wani lokaci, yana cikin wannan tunanin agogon dake jikin bangon ta sanar dashi k'arfe *12:00* daidai na rana, sosai ya jima yana mamakin yanda lokacin yayi sauri haka, a hankali ya mik'e ya d'auki makullan ya fito, ba tare da kula kowa ba ya fice duk da likitocin na gaisheshi da girmamawa, yana shiga motar gida ya koma da niyyar kwantawa, amma yana shiga a wajen aje motocin ya samu mata zaune harda Ummy ma a cikinsu, fitowa yayi a raunane yana kallonta amma tana d'aga kai suka kalli juna ta wurga masa harara tare da had'e rai, takowa ya farayi da niyyar yau dai zai gaisheta harda ma k'awayen ta, amma Ummy na ganin ya nufesu ta mik'e kamar wacce aka tsikara ta nufi hanyar falon Hajia, cak ya tsaya yana kallonta da matuk'ar rauni a tare dashi, tahowa yayi da niyyar shiga b'angaren su saiya hangi Amar ya fito daga falon Hajia, baiyi mamakin ganinshi ba dan duk samarin suna zuwa gida dan shirin zuwa masallaci, abun daya sosa zuciyarshi shine ganin Ummy tare dashi tana ta faman b'alla masa botiran rigarshi ta shadda wacce ke nuna yayi shirin zuwa masallaci da d'aurin auren babansu, da kanta ta karb'i machette d'in shi ta saka mishi tare da gyara masa zaman hula, cikin gaggawa Amar ya wuce yana fad'in "Ummy sai mun dawo."
Hannu ta d'aga masa tana fad'in "A dawo lafiya shalelen Hajia."
Wani murmushi Ammar yayi da shi kanshi baisan manufa ko fassararshi ba tare da juyawa ya koma motarshi, zai tayar Amar ya k'araso ya buga gilashin motar, saukewa yayi ba tare daya kalleshi ba shi kuma yace "Wai har ka shirya ne?"
D'ago ido yayi ya kalleshi take kuma ya d'auke idonshi, a haka Amar ya sake cewa "Ammar Abba fa yace muje da wuri masallacin, kuma kai na ga yanzu ga shigo."
Tayar da motar yayi yana cikin d'aga gilashin shi yace "Tunda dai kaje ai ba sai naje ba." Yana fad'a yayi baya baya ya daidaita hancin motar kan k'ofar fita ya fice, girgiza kai Amar yayi shima ya shiga tashi motar ya fice.
Tun a hanya ya saka a ransa zai ci gaba da zama a yanda yake, Ammar d'in sa, ba zai bari wannan damuwar ta canza shi ba, tunda dai ba zasu fahimci nadamarshi ba bare su bashi damar neman gafararsu, to kawai zai nuna kamar babu wani abu daya faru, sannan ya murje idonshi ya kalli kowa kamar yanda yake kallonsu a baya, da wannan ya isa makarantar su Hamna wanda ya samu d'alibai nata fitowa daga cikin makarantar, ta cikin gilashi ya k'urawa k'ofar ido yana jiran fitowarsu.