Sashe 8
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk wanda ya shiga wanka yake farawa da shi, ga mai buk'ata kuma ya nemi abinci ya ci sannan ya kwanta ya huta, amma colonel bayan sun dawo daga masallacin juma'a tare da Ammar bayan gidan suka nufa inda ke da fili da tarin shukoki da kuma kayan motsa jiki barkatai suka fara abinda suka saba indai suna tare, haka ya zage ya dinga koya mishi horon soja wai saboda kare kai kuma tunda yana son abun, a k'alla sun d'auki awa d'aya kafin suka had'a gumi kowa ya shiga dan yin wani wankan, bayan colonel ya shiga yayi wanka ya fito ya canza kaya, zai fita Hajia Zeinabu tace "Yallab'ai ina son magana da kai fa."
Dawowa yayi ya zauna bakin gadon yana kallonta yace "Uhum."
Duk da bata had'a ido da shi ba amma gabanta fad'uwa yake, haka ta daure tace "Dama ina so na ji ko yaushe ne hutunka zai k'are?"
Fuskar nan ba fara'a yace "Tun yaushe nake garin nan? Ba kya lissafi ne?"
Cikin rarraba ido tace "Ba haka bane, dan naga yanayin aikin naku ana iya kiranku ma ko wa'adin bai cika ba."
Tsura mata ido yayi yace "Me kike so ki fad'a?"
"Kawai zaman gidan nan ne ya gundure ni, ina buk'atar wani abu da zai rik'a deb'e min kewa, tunda na ga ita Sa'ada tana zuwa aiki, kuma ba finmu tayi ba karatu ne kawai bamuyi ba."
Wani kallo ya sake mata kamar zai had'e ta kafin ya mik'e yace "Alhamdulillah da Allah yasa da mai hankali nake magana ba mahaukaciya, ashe kinsan sai wanda yayi karatu ne zai iya shiryawa yace zai tafi wajen aiki?"
A tak'aice tace "Kai ma ci mana mutumci zakayi?"
"Kinga Zeinabu, matsalata dake tsegumi, kuma rashin wayewarki ne ya haddasa miki haka, shiyasa na so tun farko ki shiga ko da makarantar yak'ida jahilci ce amma ki ka k'i, ga Jibril nan kina ganin aikinsu kenan kullum, idan kinso ko shi zai iya yi miki hanyar samun hasken k'wak'walwa."
Kallonshi tayi da takaicin abinda yake fad'a mata tace "Dan bana da ilimi shiyasa dama ba ka iya zuwa ko ina dani, to ai sai ka d'auki karuwan naka ka dinga yawo da su tunda sun fini."
D'an cije leb'en shi yayi yana kallonta yace "Ni kike fad'awa ina da karuwai Zeinabu?"
A yanda yake kallonta tasan tsaf zai mareta dan ba bak'on abu bane a wurinsu, duk da baka shaidar mutum amma a zahirance zata iya cewa mijinta baya shan giya ko neman mata duk da kasancewarshi soji, dan duk inda yake ya ji shaid'an na neman kaishi ga aikata zina haka zai biyo jirgi ya zo wajenta, dan har doguwar tafiya ya tab'a yi ya zo kuma ko awa baiyi ba ya koma, matsalarshi d'aya saurin hushi da marin fuska ko harbi da k'afa idan ta mishi nisa, shi ma kuma ya fad'a mata ta dinga kiyayewa tana sanin me zata fad'a mishi saboda yana da zuciya tun fil'azal daman ba wai dan yana soja ba, amma inda aka samu matsalar Zeinabu irin matan nan ne masu tsegumi da ganin an musu ba daidai ba, dama dama Hajia na gyara musu zama, amma in zaiyi shekara baya gari ya samu hutun wata uku ya zo sai tace ga abinda akayi, kuma idan ka duba sai kaga k'orafi ne kawai na banza da wofi, gashi matsayin wasu yana tsone mata ido musamman Sa'ada, ta mayar da ita kamar kishiyarta duk wani motsinta akan idonta, sanin halinshi yasa ta kawar da kai gefe tana gunguni tana fad'in "To k'arya na fad'a? Matan ne baka kul...?"
Bata gama fad'a ba taji saukar yatsu biyar a fuskarta, d'ago fuskarta yayi cikin d'aga murya yace "Kalleni nan ki fad'i duk abinda ke ranki, ke har ni zaki mayar d'an iska, dan kinga na zauna tare da ku har na wata biyu shine zaki d'auke ni wani mahaukaci, to yau zan bar miki garin sai ki d'auki tsiyar da kike d'auka idan bana nan, aikin banza." Ya fad'a yana barin d'akin, tana ganin fitarshi ta d'ago tace "To ka tafin mana sai me? Idan baka nan b'acin raina yana raguwa ne da kaso arba'in cikin d'ari, kai ka k'unsa min bak'in ciki mahaifiyarka ta tusa min, mun zama kamar bayi a gida duk saboda bamuyi karatu ba."
Ko da su Hamna suka dawo aka fad'a musu Abbansu ya tafi basuyi mamaki ba, dan haka basu damu ba saima shirya fita da sukayi da yamma dan su siyo ankonsu suma, baccin rana sukayi ko da suka tashi la'asar tayi sai suka shirya cikin dogayen riguna bak'ak'e iri d'aya, komai na jikinsu kala d'aya suka saka ta yanda ba zaka iya tantacewa cikin sauri ina Hamna ba ko Amna, tun a d'aki suka fara rigima moton wa za'a hau? Nan Hamna tace ai da nata aka tafi école, Amna kuma tace jiya da nata ai aka tafi, k'arshe dai dana Amna aka tafi dan dukansu basu damu da matsayinsu ba ko na mahaifinsu, shiyasa ko dreba basu damu a d'aukar musu ba bare a siya musu mota.
Tun a falo suke jiyo hayaniya a farfajiyar gidan, can suka samu yara da iyayen ana ta hira sai dai babu Hajia babba, saida suka dawo d'akin ta da sallama amma ba'a amsa ba, wata sallamar suka sake yi Hajia dake zaune tace "Ku shigo mana."
Shiga sukayi duk jikinsu yayi sanyi dan kar ta hana su fitar, Hamna ce tace "Hajia barka da yamma."
Kallonsu kawai tayi bata amsa ba dan haka Hamna tace "Hajia dama..."
"Dama me?" Ta katseta, d'orawa tayi da "Fita zakuyi ko? To ku tashi ku tafi, amma ke Hamna ki sani na barki ne saboda na ganku tare da Amna, dan na lura duk shegen bak'in halin uwarki ne kika d'auko na rashin son zama wuri d'aya."
Shiru sukayi har saida tace "Ni ku tashi ku bani wuri, saura kuma idan kun tafi karku dawo sai an aika nemanku."
Mik'ewa sukayi sai Amna da tace "Mun gode Hajia, insha Allahu ma ba zamu jima ba zamu dawo."
Suna fitowa Hamna ta yaye kallabinta ta zubo da manyan kitsonta na gashin doki har gadon baya tare da fad'in "Shikenan dan uwarmu bata gidan saiki d'auki karan tsana ki d'ora mana, dad'in ta dai bamu muka kashe musu auren ba."
Suna fitowa farfajiyar suka kalli matan suka ce "Su tanti (aunty) sai mun dawo."
Hamna ce ta tuk'a mai gadi ya bud'e musu k'ofa suka fita, a k'ofar gidan suka samu colonel da Ammar zaune kan kujeru, hira ce suke amma babu mai annuri a fuskarshi, dama kana ganin Ammar na hira ne da mutum biyu a duk fad'in gidan, ko dai colonel ko kuma Gambo, da kaga dariya ko murmushinshi to Gambo ne, tsayawa tayi tace "Kawu ana hutawa?"
"Ina zakuje kuma da yammar nan?" Ya jefo musu tambayar, cikin turo baki tace "Kawu zamu je yar kasuwa ne, amma yanzu zamu dawo."
Kunna moton tayi yace "To dan Allah ku kula da kyau, sannan karku yarda magriba ta muku a waje."
"To kawu." Ta fad'a tana murd'a moton, kallon Ammar tayi tace "Boss ba ko magana."
Sai lokacin ya d'ago idonshi ya sauke a kanta amma tuni harta ja moton da k'arfi tana mishi dariya, dariya colonel yayi yace "Saika nuna mata kai boss d'in ne ko zaku kwashe lafiya da ita."
K'ala bai ce ba shi dai dan yana so ne ya lissafa duk iskancin data masa ta yanda idan ya damk'eta zata gane shayi ruwa ne, inda shi kuma colonel yake mamakin yanda Gambo ya bar yaranshi sakaka a gari haka ba zaka tab'a cewa wasu 'ya'yan manya bane, sa'a d'aya ma yaran su kansu basu damu ba harkar gabansu suke.
Tashi colonel yayi ya shiga cikin gida yana jin shi sakayau, dan dama sai mutum ya zo hutu ne yake samun 'yanci da sakewa, ya shiga ne da niyyar yin wanka ya kuma had'a kayanshi, dan yayi niyya saiya bar garin ko zeinabu ta ji dad'i, ya shiga d'aki kenan ya aje wayar zai shiga ban d'aki sai wayar ta fara ruri, dawowa yayi yana kallon mai kiran, d'an uwanshi ne wanda yake da tabbacin yana garin nan wato Abban su Amar, to meyasa yake kiranshi? Tabbas ba lafiya zuciyarshi ta gaya mishi, d'auka yayi ya d'ora a kunne, daga b'angaren lieutenant yace "...
*Me kuka ya faru ko zai faru?, sai mun had'e a shafi na gaba insha Allah.*
18/05/2020 à 13:51 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
_Bismillahir rahamanir rahim_
_4_
Lieutenant ne yace "D'an uwa kaga na kiraka ko? Dama yanzu na samu wayar *Aisata* (babbar d'iyar Fatime kanwar Hajia) take fad'a min Allah yayi wa Hajia (mahaifiyarsu) rasuwa."
Takawa colonel yayi gaba yana fad'in "Subhanallah, Hajia kuma? Yaushe? Dama bata da lafiya ne?"
Wani d'an murmushi lieutenant yayi yace "Haba d'an uwa, mutuwa ai ba sai ba'a lafiya ba take zuwa, dan nima dana tambaya Aisata ta fad'a min yau da safe ma har unguwa Hajiar ta fita, kawai dai lokaci ne yayi."
"Ikon Allah, kaga wata mutuwa bagatatan, yanzu to ya zamu sanar ma da Hajia?"
"Shiyasa na kiraka d'an uwa, dan kaine soja watak'ila ka fini sanin dubarun kwantar da hankali."
Yanda ya k'arashe maganar cikin zolaya yasa colonel cewa "Ba fa nasan iskanci, ka d'auka a sojan rarrashin mata da soyayya ake koya mana ne, ai wannan aikin ko Ammar ba zan sa shi ya fad'a mata ba."
Dariya lieutenant yayi ya mik'e daga kan teburinshi wanda ke cike da tarin takardu da tarkace yace "To ni dai na fad'a maka kasan yanda zakayi karka d'aga mana hankalin uwa, yanzu haka gani nan tafe zuwa gidan zan canza kaya, dan ina so na samu bisar Hajia dan sunce k'arfe hudu da rabi za'a rufe ta."
Dawowa yayi ya zauna bakin gadon yana kallonta yace "Uhum."
Duk da bata had'a ido da shi ba amma gabanta fad'uwa yake, haka ta daure tace "Dama ina so na ji ko yaushe ne hutunka zai k'are?"
Fuskar nan ba fara'a yace "Tun yaushe nake garin nan? Ba kya lissafi ne?"
Cikin rarraba ido tace "Ba haka bane, dan naga yanayin aikin naku ana iya kiranku ma ko wa'adin bai cika ba."
Tsura mata ido yayi yace "Me kike so ki fad'a?"
"Kawai zaman gidan nan ne ya gundure ni, ina buk'atar wani abu da zai rik'a deb'e min kewa, tunda na ga ita Sa'ada tana zuwa aiki, kuma ba finmu tayi ba karatu ne kawai bamuyi ba."
Wani kallo ya sake mata kamar zai had'e ta kafin ya mik'e yace "Alhamdulillah da Allah yasa da mai hankali nake magana ba mahaukaciya, ashe kinsan sai wanda yayi karatu ne zai iya shiryawa yace zai tafi wajen aiki?"
A tak'aice tace "Kai ma ci mana mutumci zakayi?"
"Kinga Zeinabu, matsalata dake tsegumi, kuma rashin wayewarki ne ya haddasa miki haka, shiyasa na so tun farko ki shiga ko da makarantar yak'ida jahilci ce amma ki ka k'i, ga Jibril nan kina ganin aikinsu kenan kullum, idan kinso ko shi zai iya yi miki hanyar samun hasken k'wak'walwa."
Kallonshi tayi da takaicin abinda yake fad'a mata tace "Dan bana da ilimi shiyasa dama ba ka iya zuwa ko ina dani, to ai sai ka d'auki karuwan naka ka dinga yawo da su tunda sun fini."
D'an cije leb'en shi yayi yana kallonta yace "Ni kike fad'awa ina da karuwai Zeinabu?"
A yanda yake kallonta tasan tsaf zai mareta dan ba bak'on abu bane a wurinsu, duk da baka shaidar mutum amma a zahirance zata iya cewa mijinta baya shan giya ko neman mata duk da kasancewarshi soji, dan duk inda yake ya ji shaid'an na neman kaishi ga aikata zina haka zai biyo jirgi ya zo wajenta, dan har doguwar tafiya ya tab'a yi ya zo kuma ko awa baiyi ba ya koma, matsalarshi d'aya saurin hushi da marin fuska ko harbi da k'afa idan ta mishi nisa, shi ma kuma ya fad'a mata ta dinga kiyayewa tana sanin me zata fad'a mishi saboda yana da zuciya tun fil'azal daman ba wai dan yana soja ba, amma inda aka samu matsalar Zeinabu irin matan nan ne masu tsegumi da ganin an musu ba daidai ba, dama dama Hajia na gyara musu zama, amma in zaiyi shekara baya gari ya samu hutun wata uku ya zo sai tace ga abinda akayi, kuma idan ka duba sai kaga k'orafi ne kawai na banza da wofi, gashi matsayin wasu yana tsone mata ido musamman Sa'ada, ta mayar da ita kamar kishiyarta duk wani motsinta akan idonta, sanin halinshi yasa ta kawar da kai gefe tana gunguni tana fad'in "To k'arya na fad'a? Matan ne baka kul...?"
Bata gama fad'a ba taji saukar yatsu biyar a fuskarta, d'ago fuskarta yayi cikin d'aga murya yace "Kalleni nan ki fad'i duk abinda ke ranki, ke har ni zaki mayar d'an iska, dan kinga na zauna tare da ku har na wata biyu shine zaki d'auke ni wani mahaukaci, to yau zan bar miki garin sai ki d'auki tsiyar da kike d'auka idan bana nan, aikin banza." Ya fad'a yana barin d'akin, tana ganin fitarshi ta d'ago tace "To ka tafin mana sai me? Idan baka nan b'acin raina yana raguwa ne da kaso arba'in cikin d'ari, kai ka k'unsa min bak'in ciki mahaifiyarka ta tusa min, mun zama kamar bayi a gida duk saboda bamuyi karatu ba."
Ko da su Hamna suka dawo aka fad'a musu Abbansu ya tafi basuyi mamaki ba, dan haka basu damu ba saima shirya fita da sukayi da yamma dan su siyo ankonsu suma, baccin rana sukayi ko da suka tashi la'asar tayi sai suka shirya cikin dogayen riguna bak'ak'e iri d'aya, komai na jikinsu kala d'aya suka saka ta yanda ba zaka iya tantacewa cikin sauri ina Hamna ba ko Amna, tun a d'aki suka fara rigima moton wa za'a hau? Nan Hamna tace ai da nata aka tafi école, Amna kuma tace jiya da nata ai aka tafi, k'arshe dai dana Amna aka tafi dan dukansu basu damu da matsayinsu ba ko na mahaifinsu, shiyasa ko dreba basu damu a d'aukar musu ba bare a siya musu mota.
Tun a falo suke jiyo hayaniya a farfajiyar gidan, can suka samu yara da iyayen ana ta hira sai dai babu Hajia babba, saida suka dawo d'akin ta da sallama amma ba'a amsa ba, wata sallamar suka sake yi Hajia dake zaune tace "Ku shigo mana."
Shiga sukayi duk jikinsu yayi sanyi dan kar ta hana su fitar, Hamna ce tace "Hajia barka da yamma."
Kallonsu kawai tayi bata amsa ba dan haka Hamna tace "Hajia dama..."
"Dama me?" Ta katseta, d'orawa tayi da "Fita zakuyi ko? To ku tashi ku tafi, amma ke Hamna ki sani na barki ne saboda na ganku tare da Amna, dan na lura duk shegen bak'in halin uwarki ne kika d'auko na rashin son zama wuri d'aya."
Shiru sukayi har saida tace "Ni ku tashi ku bani wuri, saura kuma idan kun tafi karku dawo sai an aika nemanku."
Mik'ewa sukayi sai Amna da tace "Mun gode Hajia, insha Allahu ma ba zamu jima ba zamu dawo."
Suna fitowa Hamna ta yaye kallabinta ta zubo da manyan kitsonta na gashin doki har gadon baya tare da fad'in "Shikenan dan uwarmu bata gidan saiki d'auki karan tsana ki d'ora mana, dad'in ta dai bamu muka kashe musu auren ba."
Suna fitowa farfajiyar suka kalli matan suka ce "Su tanti (aunty) sai mun dawo."
Hamna ce ta tuk'a mai gadi ya bud'e musu k'ofa suka fita, a k'ofar gidan suka samu colonel da Ammar zaune kan kujeru, hira ce suke amma babu mai annuri a fuskarshi, dama kana ganin Ammar na hira ne da mutum biyu a duk fad'in gidan, ko dai colonel ko kuma Gambo, da kaga dariya ko murmushinshi to Gambo ne, tsayawa tayi tace "Kawu ana hutawa?"
"Ina zakuje kuma da yammar nan?" Ya jefo musu tambayar, cikin turo baki tace "Kawu zamu je yar kasuwa ne, amma yanzu zamu dawo."
Kunna moton tayi yace "To dan Allah ku kula da kyau, sannan karku yarda magriba ta muku a waje."
"To kawu." Ta fad'a tana murd'a moton, kallon Ammar tayi tace "Boss ba ko magana."
Sai lokacin ya d'ago idonshi ya sauke a kanta amma tuni harta ja moton da k'arfi tana mishi dariya, dariya colonel yayi yace "Saika nuna mata kai boss d'in ne ko zaku kwashe lafiya da ita."
K'ala bai ce ba shi dai dan yana so ne ya lissafa duk iskancin data masa ta yanda idan ya damk'eta zata gane shayi ruwa ne, inda shi kuma colonel yake mamakin yanda Gambo ya bar yaranshi sakaka a gari haka ba zaka tab'a cewa wasu 'ya'yan manya bane, sa'a d'aya ma yaran su kansu basu damu ba harkar gabansu suke.
Tashi colonel yayi ya shiga cikin gida yana jin shi sakayau, dan dama sai mutum ya zo hutu ne yake samun 'yanci da sakewa, ya shiga ne da niyyar yin wanka ya kuma had'a kayanshi, dan yayi niyya saiya bar garin ko zeinabu ta ji dad'i, ya shiga d'aki kenan ya aje wayar zai shiga ban d'aki sai wayar ta fara ruri, dawowa yayi yana kallon mai kiran, d'an uwanshi ne wanda yake da tabbacin yana garin nan wato Abban su Amar, to meyasa yake kiranshi? Tabbas ba lafiya zuciyarshi ta gaya mishi, d'auka yayi ya d'ora a kunne, daga b'angaren lieutenant yace "...
*Me kuka ya faru ko zai faru?, sai mun had'e a shafi na gaba insha Allah.*
18/05/2020 à 13:51 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
_Bismillahir rahamanir rahim_
_4_
Lieutenant ne yace "D'an uwa kaga na kiraka ko? Dama yanzu na samu wayar *Aisata* (babbar d'iyar Fatime kanwar Hajia) take fad'a min Allah yayi wa Hajia (mahaifiyarsu) rasuwa."
Takawa colonel yayi gaba yana fad'in "Subhanallah, Hajia kuma? Yaushe? Dama bata da lafiya ne?"
Wani d'an murmushi lieutenant yayi yace "Haba d'an uwa, mutuwa ai ba sai ba'a lafiya ba take zuwa, dan nima dana tambaya Aisata ta fad'a min yau da safe ma har unguwa Hajiar ta fita, kawai dai lokaci ne yayi."
"Ikon Allah, kaga wata mutuwa bagatatan, yanzu to ya zamu sanar ma da Hajia?"
"Shiyasa na kiraka d'an uwa, dan kaine soja watak'ila ka fini sanin dubarun kwantar da hankali."
Yanda ya k'arashe maganar cikin zolaya yasa colonel cewa "Ba fa nasan iskanci, ka d'auka a sojan rarrashin mata da soyayya ake koya mana ne, ai wannan aikin ko Ammar ba zan sa shi ya fad'a mata ba."
Dariya lieutenant yayi ya mik'e daga kan teburinshi wanda ke cike da tarin takardu da tarkace yace "To ni dai na fad'a maka kasan yanda zakayi karka d'aga mana hankalin uwa, yanzu haka gani nan tafe zuwa gidan zan canza kaya, dan ina so na samu bisar Hajia dan sunce k'arfe hudu da rabi za'a rufe ta."