Sashe 196
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin wanda suka bashi kud'in ne yace "Ni yanzu kud'in nan daya raba ni dasu daya bar min kayana wallahi dana bawa amarya data nemi kud'in anko."
Wani ne yace "Saika bata wasu mana."
Babban aminin Ammar ne yace "Kar ma kace zaka mishi Allah ya isa, kud'inku bashi zai cisu ba, in kuma kayi gardama je ka tambayi Buharin kaji."
Tashi yayi kuwa da sauri yaje waben mai doyar Buhari, ko da ya ganshi yace "Mutumin yane?"
"Lafiya lau, wai Ammar da naga ya tsaya nan me yace maka?"
Cikin murmushi yace "Kud'i ne ya bayar yace duk magidancin da ya zo siyan abu a bashi kaza d'aya."
Cikin kafe shi da ido yace "Nawa ya baka?"
A tak'aice yace "Jaka talatin."
Juyowa yayi yana fad'in "Ta tabbata gaskiya ya fad'a, kud'inmu ne yayi sadaka dasu, to Allah ya bashi ladar da mu baki d'aya."
*Ameeeeeeeeen*.
*Alhamdulillah*
04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
*ALHAMDULILLAH Allah abin godiya, kamar jiya ne na fara BADAK'ALA yau gashi na kawo k'arshenshi cikin hukuncin mai duka, Allah ya gafarta kuraraina da zunubina, Allah yasa muyi tarayya daku a cikin ladar baki d'aya.*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
*FIN*
_80_
*Laraba* ce yau amma ko da ya fito zai tafi masallaci ya mik'ar da ita tsaye yace "D'auko hijabinki."
Kallonshi tayi tace "Hijabina kuma? Ina zamu je?"
Fuskar nan a had'e yace "Hijabinki nace ki d'auko, ko gani kike zan siyar dake ne?"
Girgiza kai tayi ta juya ta d'auko hijabin ta dawo, hannunta ya kama har sun kai k'ofa taga ba mota zasu shiga ba, gabanta ne ya shiga fad'uwa ta tsaya tace "Yallab'ai lafiya? Dan Allah ka fad'a min me ke faruwa? Ina zamu je yanzu da rana haka?"
Ba tare daya kalleta ba yace "Masallaci."
Da k'arfi tace "Masallaci? Yin me?"
Juyowa yayi ya kalleta yace "Me akeyi acan?"
Cikin tsoron kar ya zabga mata mari tace "Sallah."
"To ita zamu je muyi, yan uku nake so na haifa, ko jiya saida Hajia ta min gori wai mijinta kad'ai ke da wannan bajintar, ni kuma ina so na kafa mata tarihi."
Karantar yanayinshi ta shiga yi, indai bata amince ba zai ci ubanta, in kuma ta amince zata jawa kanta yan kallo, a k'arshe shi da kanshi zai iya mata hukunci yace ai ta shiga cikin maza, a hankali ta d'an girgiza kai a ranta tana fad'in "Ba fa yau na fara saninka ba Ammar, ka daina wahalar dani."
Saida ta dafa kafad'arshi cikin rarrashi da taushin murya tace "Duniyata, kayi hak'uri mana kai ka tafi yanzu, nima zanje nayi sallah nayi mana addu'a, insha Allahu ranar juma'a tare zamu tafi masallaci, amma yanzu kaga ni ba nik'ab gareni ba, kuma maganar gaskiya ina maka kishin kaina bana so kowa ya kalleni."
Yanda ta k'are maganar da shagwab'a saiya kalleta yana murmushi yace "Ja'ira kuma fa gaskiyarki, amma gaskiya Allah ya taimake ki dan da ace kin bini kuma naga ana kallonki...hummm da uwar mutum ta haifi wani yau."
Wani kallon ba ga irinta ba ta mishi kafin tace "Gaskiya kam, shiyasa nake kiyaye duk abinda zai tayar min da kishinka, ai bana so ka k'ara karya 'ya'yan mutane ba."
Dariya yayi yana kallonta yace "Yar banza kice dai ba kya son jaruminki ya sake kwana a gidan maza."
Dariya tayi tana fad'in "Ina zan so haka kai ma, Allah yanza ka sake tsokano rigima aka kamaka sai na zubar da cikin nan na jikina."
Da k'arfi ya juyo yana kallonta yace "Ciki Hamna? Yaushe ki kayi cikin ban sani ba?"
Har ta juya da niyyar guduwa ya rik'o hannunta, da k'arfi ya matseta ya d'aga rigarta yana d'an tausa cikinta, ko da ya kai ga mararta ya danna tayi wata yar k'ara mai d'an k'arfi tare da ja baya, sake rik'ota yayi yana kallon idonta yace "Yanzu kankana dan kar na samu yan ukun shine kika samu ciki da wuri?"
Cikin kallon kayi hak'uri tace "Allah ba haka bane, nima ina so ka samu."
Sakinta yayi yana fad'in "Uhm, zan dage n ci gaba da addu'a idan ma d'aya ne za'a mayar dashi uku insha Allah."
Da kallo ta bishi har ya fice, komawa tayi ita ma tana dariya yau wai za'a kaita masallaci.
Da yamm lafiya lau ya fita daga gidan, amma bai jima ba sai gashi ya dawo tunda ta hange shi ya fito daga mota yana kumfar baki ta kama jikinta, ko da ya shigo ciki taji yana ta masifa, zaune yayi k'asan carpet sai fad'a yake, kuma ba komai ya jawo masifar ba si ganin Jano da yayi a gari aka, shine ya tambaya yaushe aka fito dashi aka ce masa ai ya kusa shekara biyu da fitowa, shine fa ransa ya b'ace ya dawo gida ya saukewa mi tsotsai, tana gyaran akaifu sai dai ta saci kllonshi da taga zai kalleta tayi saurin d'auke kanta.
Yara ne suka shigo da gudu da ball d'insu suna bugawa, da gudu ta taresu a k'ofar d'akin, Shureim ta kama kunnenshi ta murd'e tace "Saurare ni, kaga ubanku nan ya dawo kuma ranshi a b'ace yake, wallahi ku koma can sam kuyi wasarku hankali kwance, in kuma kuna so jikinku yayi tsami to Bismillah."
Saida ya d'an lek'a y hangeshi zaune sai k'wafa yake yana cije leb'en k'asa sannan ya kalleta yace "Ummy wai me yasa Abba ya fiya rigima ne? Sai a b'ata masa rai a waje sai ya shigo nan mu ya balbalemu da masifa."
Da sauri ta rufe masa baki tace "Shiii, maza ku wuce."
Kallon Ahmad tayi da yanzu shim yake tare dasu tace "Ku wuce kaji yarona."
Da gudu duk suka nufi komawa sama, Ameera ta kalla tace "Ki wuce d'akinki bana son wasan nan da maza ayita tsalle tsalle."
Jinjina kai tayi ta kama hanya zata shiga Ammr ya fito yana fad'in "Ke dai baki san gaskiya ba a rayuwarki, yanzu waccen da kika koresu su ba yara bane?"
Kallonshi tayi a hankali tace "Amma ita macece ai."
"To sai akayi yaya?" Ya fad'a da alamar tijara kad'an yake jira, girgiza kai tayi tace "Komai, kawai dai ba zan bar yarinyata bane a cikinsu kowane lokaci."
Cikin d'aga murya yace "Kinfi so ku zauna kullum kina koya mata kinibibi ko?"
Wani kallo ta masa tace "Yan uwa fa shida gareta kuma duk maza, idan ban jata a jikina ba ya kake so na mata to? Zata zauna tana fad'a musu damuwarta ne su?"
Juyawa tayi ta kama hannunta suka shige ciki ta tura ta d'akinta. Kallon juna sukayi shi da Shureim da ko da yaga ya fito ya tsaya, ido ciki ido yake kallonshi babu rusunawa, shi ko a abokanshi yana wuya yag wanda suke kallon juna haka bare uwarsu, amma ga babban d'anshi na kallon idonshi kamar yanda shima yake kallon kowa a haka, hararanshi yayi yace "Kai kuma lafiyar kallona?"
Me zaiyi sai kawai ya jawo hannunshi suna gaisawa a dole yana dariya yana fad'in "Haba Abba rabu da su dan Allah, wallahi in kana masifa ba kya kyau, yi dariya mana."
Kallon yaron yayi sosai, in yana *masifa* baya kyau? Shine d'ansa ke fad'a masa haka? Lallai *Ammar* d'in da Hajia ke addua'r kar a samu gashi za'a samu.
K'ok'arin k'watar hannunshi ya shiga yi yana fad'in "Kai d'an uwarka sake ni, tsaranka ne ni."
Rik'e hannun yayi gam yana fad'in "Abba ni fa abokinka ne, fad'a min meye damuwar dan Allah."
Fizgo hannunshi yayi yana fad'in "Je ka tambayi uwarka mana."
Kallonshi yayi yace "Abba wai me yasa ita Ummy sai tace abbanku? Amma kai sai ka dinga cewa uwarmu uwarmu?"
Shima kallonshi yayi yace "Bari to zan ma uwar taku kishiya, kaga sain dinga cewa auntynku."
Da sauri yayi tsalle ya mak'ale a wuyanshi yana fad'in "A'a wallahi Abba bari wannan magana ma, karna saukewa yarinya kafad'a."
Dariya Ammar ya shiga yi dan yasan a bakinshi yaji kalmar sauke kafad'ar nan, lallai iko sai Allah, yana mak'ale a wuyanshi ya shiga falon dashi yana fad'in "Ke zo ki min tsakani da yaron nan naki, kinga dai kin lalata shi nema yake y zama wani iri."
Wani kallo ta masa tace "Kai da kan irin hka way rabak da Abba? Dubarun zama dashi kawai zaka koya kaima, dan ba lallai kayi hak'uri kamar yanda su Abba sukayi ba."
Zaune yayi dashi suna hira da k'yak'yata dariya, duk abinda Ammar ya fad'a Shureim na da amsa ko abin cewa akai shima, baya waske mishi saiya taroshi, basira fikira da zalak'a da kuma wayo, rashin kunyar jarabar da kwatirar duk babu abinda ya rago daga ubanshi, ita kam fatanta bai wuce su jashi a jikinsu ba su raka shi da addu'a, dan ranar mai zuwa tana musu wankin kaya duk sati ya kalla ido cikin ido yace "Habbi ki dinga wanka dan Allah ko kya samu bazawari kema."
Ce mishi tayi "To wani bazawari nake nema bayan gaka anan?"
Wata dariya ya mata yace "Haba Hajia Habbi, yo ni matar da zan aura ma ai yanzu ne ubanta ke k'uruciyarsa."
Sallah magriba kad'ai ta fitar dasu daga gidan basu dawo ba kuma har akayi isha'i, suna kan teburin cin abinci Sayyada ta shigo fa sallama, kai tsaye can ta nufa tana fad'in "Yara ku ce na zo a sa'a?"
Hamna ce ta kalleta tace "Su waye yaran?"
Kallonta tayi tace "Ku mana, ko ba yarana bane da jikokina anan?"
Duka yaran ne suka gaisheta ta amsa da sakin fuska, kallonta Ammar yayi yace "K'aramar uwa daga ina haka a daren nan? Kinsan fa bana son yawon nan saboda ina kishinki."
Saida ta kalli Hamna ta bashi hannu tana fad'in "Bamu gaisa ba ma d'an albarka."
Da sauri Hamna ta taso ta rik'e hannunshi tace "Aunty bana son iskanci fa, mijin nawa kuma a gabana?"
Wani ne yace "Saika bata wasu mana."
Babban aminin Ammar ne yace "Kar ma kace zaka mishi Allah ya isa, kud'inku bashi zai cisu ba, in kuma kayi gardama je ka tambayi Buharin kaji."
Tashi yayi kuwa da sauri yaje waben mai doyar Buhari, ko da ya ganshi yace "Mutumin yane?"
"Lafiya lau, wai Ammar da naga ya tsaya nan me yace maka?"
Cikin murmushi yace "Kud'i ne ya bayar yace duk magidancin da ya zo siyan abu a bashi kaza d'aya."
Cikin kafe shi da ido yace "Nawa ya baka?"
A tak'aice yace "Jaka talatin."
Juyowa yayi yana fad'in "Ta tabbata gaskiya ya fad'a, kud'inmu ne yayi sadaka dasu, to Allah ya bashi ladar da mu baki d'aya."
*Ameeeeeeeeen*.
*Alhamdulillah*
04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
*ALHAMDULILLAH Allah abin godiya, kamar jiya ne na fara BADAK'ALA yau gashi na kawo k'arshenshi cikin hukuncin mai duka, Allah ya gafarta kuraraina da zunubina, Allah yasa muyi tarayya daku a cikin ladar baki d'aya.*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
*FIN*
_80_
*Laraba* ce yau amma ko da ya fito zai tafi masallaci ya mik'ar da ita tsaye yace "D'auko hijabinki."
Kallonshi tayi tace "Hijabina kuma? Ina zamu je?"
Fuskar nan a had'e yace "Hijabinki nace ki d'auko, ko gani kike zan siyar dake ne?"
Girgiza kai tayi ta juya ta d'auko hijabin ta dawo, hannunta ya kama har sun kai k'ofa taga ba mota zasu shiga ba, gabanta ne ya shiga fad'uwa ta tsaya tace "Yallab'ai lafiya? Dan Allah ka fad'a min me ke faruwa? Ina zamu je yanzu da rana haka?"
Ba tare daya kalleta ba yace "Masallaci."
Da k'arfi tace "Masallaci? Yin me?"
Juyowa yayi ya kalleta yace "Me akeyi acan?"
Cikin tsoron kar ya zabga mata mari tace "Sallah."
"To ita zamu je muyi, yan uku nake so na haifa, ko jiya saida Hajia ta min gori wai mijinta kad'ai ke da wannan bajintar, ni kuma ina so na kafa mata tarihi."
Karantar yanayinshi ta shiga yi, indai bata amince ba zai ci ubanta, in kuma ta amince zata jawa kanta yan kallo, a k'arshe shi da kanshi zai iya mata hukunci yace ai ta shiga cikin maza, a hankali ta d'an girgiza kai a ranta tana fad'in "Ba fa yau na fara saninka ba Ammar, ka daina wahalar dani."
Saida ta dafa kafad'arshi cikin rarrashi da taushin murya tace "Duniyata, kayi hak'uri mana kai ka tafi yanzu, nima zanje nayi sallah nayi mana addu'a, insha Allahu ranar juma'a tare zamu tafi masallaci, amma yanzu kaga ni ba nik'ab gareni ba, kuma maganar gaskiya ina maka kishin kaina bana so kowa ya kalleni."
Yanda ta k'are maganar da shagwab'a saiya kalleta yana murmushi yace "Ja'ira kuma fa gaskiyarki, amma gaskiya Allah ya taimake ki dan da ace kin bini kuma naga ana kallonki...hummm da uwar mutum ta haifi wani yau."
Wani kallon ba ga irinta ba ta mishi kafin tace "Gaskiya kam, shiyasa nake kiyaye duk abinda zai tayar min da kishinka, ai bana so ka k'ara karya 'ya'yan mutane ba."
Dariya yayi yana kallonta yace "Yar banza kice dai ba kya son jaruminki ya sake kwana a gidan maza."
Dariya tayi tana fad'in "Ina zan so haka kai ma, Allah yanza ka sake tsokano rigima aka kamaka sai na zubar da cikin nan na jikina."
Da k'arfi ya juyo yana kallonta yace "Ciki Hamna? Yaushe ki kayi cikin ban sani ba?"
Har ta juya da niyyar guduwa ya rik'o hannunta, da k'arfi ya matseta ya d'aga rigarta yana d'an tausa cikinta, ko da ya kai ga mararta ya danna tayi wata yar k'ara mai d'an k'arfi tare da ja baya, sake rik'ota yayi yana kallon idonta yace "Yanzu kankana dan kar na samu yan ukun shine kika samu ciki da wuri?"
Cikin kallon kayi hak'uri tace "Allah ba haka bane, nima ina so ka samu."
Sakinta yayi yana fad'in "Uhm, zan dage n ci gaba da addu'a idan ma d'aya ne za'a mayar dashi uku insha Allah."
Da kallo ta bishi har ya fice, komawa tayi ita ma tana dariya yau wai za'a kaita masallaci.
Da yamm lafiya lau ya fita daga gidan, amma bai jima ba sai gashi ya dawo tunda ta hange shi ya fito daga mota yana kumfar baki ta kama jikinta, ko da ya shigo ciki taji yana ta masifa, zaune yayi k'asan carpet sai fad'a yake, kuma ba komai ya jawo masifar ba si ganin Jano da yayi a gari aka, shine ya tambaya yaushe aka fito dashi aka ce masa ai ya kusa shekara biyu da fitowa, shine fa ransa ya b'ace ya dawo gida ya saukewa mi tsotsai, tana gyaran akaifu sai dai ta saci kllonshi da taga zai kalleta tayi saurin d'auke kanta.
Yara ne suka shigo da gudu da ball d'insu suna bugawa, da gudu ta taresu a k'ofar d'akin, Shureim ta kama kunnenshi ta murd'e tace "Saurare ni, kaga ubanku nan ya dawo kuma ranshi a b'ace yake, wallahi ku koma can sam kuyi wasarku hankali kwance, in kuma kuna so jikinku yayi tsami to Bismillah."
Saida ya d'an lek'a y hangeshi zaune sai k'wafa yake yana cije leb'en k'asa sannan ya kalleta yace "Ummy wai me yasa Abba ya fiya rigima ne? Sai a b'ata masa rai a waje sai ya shigo nan mu ya balbalemu da masifa."
Da sauri ta rufe masa baki tace "Shiii, maza ku wuce."
Kallon Ahmad tayi da yanzu shim yake tare dasu tace "Ku wuce kaji yarona."
Da gudu duk suka nufi komawa sama, Ameera ta kalla tace "Ki wuce d'akinki bana son wasan nan da maza ayita tsalle tsalle."
Jinjina kai tayi ta kama hanya zata shiga Ammr ya fito yana fad'in "Ke dai baki san gaskiya ba a rayuwarki, yanzu waccen da kika koresu su ba yara bane?"
Kallonshi tayi a hankali tace "Amma ita macece ai."
"To sai akayi yaya?" Ya fad'a da alamar tijara kad'an yake jira, girgiza kai tayi tace "Komai, kawai dai ba zan bar yarinyata bane a cikinsu kowane lokaci."
Cikin d'aga murya yace "Kinfi so ku zauna kullum kina koya mata kinibibi ko?"
Wani kallo ta masa tace "Yan uwa fa shida gareta kuma duk maza, idan ban jata a jikina ba ya kake so na mata to? Zata zauna tana fad'a musu damuwarta ne su?"
Juyawa tayi ta kama hannunta suka shige ciki ta tura ta d'akinta. Kallon juna sukayi shi da Shureim da ko da yaga ya fito ya tsaya, ido ciki ido yake kallonshi babu rusunawa, shi ko a abokanshi yana wuya yag wanda suke kallon juna haka bare uwarsu, amma ga babban d'anshi na kallon idonshi kamar yanda shima yake kallon kowa a haka, hararanshi yayi yace "Kai kuma lafiyar kallona?"
Me zaiyi sai kawai ya jawo hannunshi suna gaisawa a dole yana dariya yana fad'in "Haba Abba rabu da su dan Allah, wallahi in kana masifa ba kya kyau, yi dariya mana."
Kallon yaron yayi sosai, in yana *masifa* baya kyau? Shine d'ansa ke fad'a masa haka? Lallai *Ammar* d'in da Hajia ke addua'r kar a samu gashi za'a samu.
K'ok'arin k'watar hannunshi ya shiga yi yana fad'in "Kai d'an uwarka sake ni, tsaranka ne ni."
Rik'e hannun yayi gam yana fad'in "Abba ni fa abokinka ne, fad'a min meye damuwar dan Allah."
Fizgo hannunshi yayi yana fad'in "Je ka tambayi uwarka mana."
Kallonshi yayi yace "Abba wai me yasa ita Ummy sai tace abbanku? Amma kai sai ka dinga cewa uwarmu uwarmu?"
Shima kallonshi yayi yace "Bari to zan ma uwar taku kishiya, kaga sain dinga cewa auntynku."
Da sauri yayi tsalle ya mak'ale a wuyanshi yana fad'in "A'a wallahi Abba bari wannan magana ma, karna saukewa yarinya kafad'a."
Dariya Ammar ya shiga yi dan yasan a bakinshi yaji kalmar sauke kafad'ar nan, lallai iko sai Allah, yana mak'ale a wuyanshi ya shiga falon dashi yana fad'in "Ke zo ki min tsakani da yaron nan naki, kinga dai kin lalata shi nema yake y zama wani iri."
Wani kallo ta masa tace "Kai da kan irin hka way rabak da Abba? Dubarun zama dashi kawai zaka koya kaima, dan ba lallai kayi hak'uri kamar yanda su Abba sukayi ba."
Zaune yayi dashi suna hira da k'yak'yata dariya, duk abinda Ammar ya fad'a Shureim na da amsa ko abin cewa akai shima, baya waske mishi saiya taroshi, basira fikira da zalak'a da kuma wayo, rashin kunyar jarabar da kwatirar duk babu abinda ya rago daga ubanshi, ita kam fatanta bai wuce su jashi a jikinsu ba su raka shi da addu'a, dan ranar mai zuwa tana musu wankin kaya duk sati ya kalla ido cikin ido yace "Habbi ki dinga wanka dan Allah ko kya samu bazawari kema."
Ce mishi tayi "To wani bazawari nake nema bayan gaka anan?"
Wata dariya ya mata yace "Haba Hajia Habbi, yo ni matar da zan aura ma ai yanzu ne ubanta ke k'uruciyarsa."
Sallah magriba kad'ai ta fitar dasu daga gidan basu dawo ba kuma har akayi isha'i, suna kan teburin cin abinci Sayyada ta shigo fa sallama, kai tsaye can ta nufa tana fad'in "Yara ku ce na zo a sa'a?"
Hamna ce ta kalleta tace "Su waye yaran?"
Kallonta tayi tace "Ku mana, ko ba yarana bane da jikokina anan?"
Duka yaran ne suka gaisheta ta amsa da sakin fuska, kallonta Ammar yayi yace "K'aramar uwa daga ina haka a daren nan? Kinsan fa bana son yawon nan saboda ina kishinki."
Saida ta kalli Hamna ta bashi hannu tana fad'in "Bamu gaisa ba ma d'an albarka."
Da sauri Hamna ta taso ta rik'e hannunshi tace "Aunty bana son iskanci fa, mijin nawa kuma a gabana?"