Sashe 13
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan sunyi sallah isha'i aka fito da abinci aka ci, lokacin ne suka fara haramar komawa gida dan sun fahimci kwana anan ba zai musu ba, har cikin gida suka samu Hajia suka fad'a mata, sam Amar bai yarda ya had'u da ita ba dan saita tambayeshi meya same shi, ita kuma k'aramin aikinta ne ta musu bala'i a gidan rasuwa, da k'yar ta yarda zata kwana dan cewa tayi zafi kasheta zaiyi kafin safiya, saida Alhaji yasa baki yace shima zai kwana anan dan bai dace ta bar wurin ba daga yanzu har zuwa kwana uku, haka dai ta hak'ura amma tace ba tayi alk'awarin zama har sadakar uku ba, nan suka juyo dukansu sai Hajia da Alhaji acan, ba tare da wata matsala ba Allah ya kawosu gida lafiya, kowa wajen na shi iyali ya nufa ya samu yayi wanka, k'arfe *10:00* na dare lieutenant Hassan da colonel Hussein da Labaran suka hallara kan babban teburin cin abinci, in dai har suna gari dama sukan had'u ko dan su tattauna matsalar data shafesu, Soueba ce yau take zuba musu duk abinda zasu ci, tana cikin zuba musu ruwa da lemu ta kalli mijinta Labaran tace "...
*Mu had'u a shafi na gaba insha Allah.*✋
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe*👏
27/05/2020 à 14:46 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*SANIN MASOYI*
_(sai Allah)_
*BAYA DA K'URA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
💞 _*MASOYA NA*_💕
*😂 Nasan za ku sha mamaki sosai ganin na dawo da ci gaban sanin masoyi, to ku kwantar da hankulanku kusha kallo kawai, duba da akwai wasu abubuwa daya kamatain ace an warwaresu tun a na farko, amma Allah bai nufa ba sai yanzu idan ya ara mana rai da lafiya, insha Allahu abun zai k'ayatar da ku fiye ma da na farko, kuma wannan shi zai zama na k'arshe da yardar Allah.*
_Bismillahir rahamanir rahim_
_1_
_Idan masu karatu basu manta ba mun tsaya a waccen labarin *Sameera* na da ciki na wata biyar, sannan Abbas na shirin had'a *Raihan* aure da *Abdul* d'an wajen Abbas mai biwa *Husnah* da zaran ta kammala secondary d'in ta, to zamu d'auki labarin daga bayan haihuwar Sameera muyi gaba insha Allah._
*Abbas* ne zaune tare da Abba (mahaifin Sameera Mus'ab) da kuma Umma (mahaifiyar Abbas Falmata) a gefensu, cikin hushi Abba yace "Ina! Wannan ma maganar banza ce, wallahi ba zan tab'a bari ku had'a *Raihan* da tsatson wannan mutumin ba, *Abba*? Ina! Ba dai d'an Abba ba wallahi, mutumin daya cutar da kai ya cuce mu gaba d'aya."
Cikin taushin murya da nutsuwa Umma tace "A gaskiya nima abin bai kwanta min a rai ba, kuma naga ma du-du-du yaron shekararshi nawa? Bai ko gama mallakar hankalin kanshi ba, sannan ita kanta Raihan d'in nawa take da har zaku fara maganar aurar da ita? Shekara goma fa, ba kwa tunanin ku zo ku tsayar da magana akan ga wanda za'a bata, a k'arshe zuciyarta ta kamu da son wani kuma ba shi ba, tunda zata ci gaba da zuwa makarantarta ai."
Abba ne yace "Wannan ma abun dubawa ne, irin wannan had'in tun da k'uruciya yana da matsala gaskiya, bansan me kuka gani ba da har kuke tunani had'a su."
Cike da kulawa *Sameera* ta kalleta tace "Hakane Umma, amma ai ba yanzu za'a musu auren ba, sai nan da shekara hud'u, kunga a lokacin ya samu cikakkiyar shekara ashirin da uku, ita kuma ta koba komai dai ta zama balagaggiya, sannan ba zamu had'a su bane haka kawai, zamu fara tambayar ra'ayin du akan lamarin."
"Yanzu in banda abinki *takwarata* ina Raihan ina wani sanin so? Ko ta amsa miki da eh wallahi idan ta mallaki hankalin kanta zata iya canza magana, 'yar shekara goma fa ake miki magana ba 'yar sha shida ba ko sama da haka."
Cikin tafasar zuci Abba yace "Kunga, ni ba k'arancin shekarun yaron bane damuwa ta, tunda ko yanzu aka mishu aure za'a samu kyakyawan sakamako daga gareshi ta hanyar zuri'a, kuma idan da shak'uwa da fahimta duk wannan ba matsala bace a tsakaninsu, kawai dai yaron ne bai min ba saboda kasancewarshi d'an mak'iyina."
A hankali *Abbas* ya d'ago ya kallesu cikin nutsuwa da girmamawa yace "Abba, Umma, sam banyi tunanin wannan maganar zata iya rasa muhalli a zuk'atanku, Abba, ko fa ubangijin daya hallicemu baya kamamu da laifin da waninmu ya aikata, ina ganin kamar rashin adalci ne da kuma dacewa ace zamu hukunta *Abdul Malik* akan laifin da mahaifinshi ne ya aikata, duba da lokacin da abun ya faru ko kanshi bai sani ba, namiji ne shi ba kuma lallai yayi halayyar mahaifinshi ba, zamu iya cewa mu shaidane akan hallayarshi, bai kamata mu hanashi auren Raihan ba in har suna son junansu, ko 'yar uwarshi *Husna* ta samu miji tayi aure a dalilin rabin rayuwarta da tayi a gidan nan, ni da hannu na na bayar da aurenta Abba, shin kuna ganin ya kamata ace mu mun hana auren d'an su da 'yar mu saboda tunanin abinda mahaifinshi yayi? Bai dace ba hakan iyayena, kuyi hak'uri ku sawa yaran nan albarka, hak'ik'a idan kuka ce baku yarda ba za'a fasa dole, amma hakan ba zai mana dad'i ba."
A hankali Sameera tace "Gaskiya ne Abba, kuma na ga ko shi kansa Abban ai mun yafe masa laifin daya mana, kuma kuyi hak'uri ku yafe masa sannan ku manta da baya, duba da mutumin nan yanzu baya raye a doron duniya."
Kallon juna Abba da Umma sukayi kafin Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan, mun amince, amma abisa wani sharad'i guda d'aya."
Sameera ma da Abbas kallon juna sukayi kafin Abbas yace "Wane irin sharad'ine wannan Abba?"
Ba alamar wasa yace "Sai in kun amince za'a yi wa yaron gwajin cuta mai karya gwarkuwar jiki da ma sauran cututtuka masu had'ari wanda akan iya d'auka ta hanyar mu'amula."
Dafe kai Abbas yayi yana tunani, yasan halin gogon nasu in har basu amice ba to za'a fasa ne, dan haka ya d'an kalli Sameera wacce ita ma take kallonshi kafin ya kallesu yace "Shikenan Abba, mu ma mun amince."
"Shikenan, Allah ya tabbatar da alkairi." Cewar Abban, da "Ameen." Suka amsa da shi.
Sai Abba daya mik'e zai fita daga falon yana fad'in "A dole wai sai an raba mutum da matarsa, ni ina son amaryata amma kuke son saita min kishiya."
Dariya sukayi sai Umma da tace "Shi ya sa zanfi kowa farin ciki idan haka ta kasance, dan ko ba komai na rabu da kishiya d'aya."
Suma mik'ewa duka sukayi suka nufi b'angaren nasu Abbas, masha Allah falon ya had'u iya had'uwa, gashi duk yaran dake d'akin kowa harkar gabanshi yake amma cikin nutsuwa, sai Raihan dake zaune kan kujera da littafi tana karatu, sai kuma Abdul dake gefe tare da k'aninshi *Jabir* suna danna wayoyinsu, duka zaune sukayi kafin Sameera tace "Ku tashi kuje ku kwanta dare yayi."
Kusan duka yaran suka amsa da "Ok Ammie." Mik'ewa sukayi inda kowa ya nufi nashi d'akin, Raihan ma tashi tayi sai Sameera ce tace " *Mamana* zo nan."
Cikin sanyi jiki da nutsuwa wanda ya zama halitar yarinyar ta taho ko kallon idon mahaifiyarta ba tayi ba harta zaune kusa da ita, Abdul ma da Ameer zasu mik'e Abba yace "Kai Jabir kaje, Abdul ka zauna zamuyi magana."
Cikin tsananin fad'uwar gaba da fargaba ya zame ya zauna k'asa duk da Abbas yace ya zauna inda yake, shiru falon ya d'auka kafin Abba yace "Abdul, abinda yasa nace ka zauna dama ba wani abu bane, ni da iyaye da kuma mai sunan Mamana (Sameera) munyi wata shawara akan ku kai da Raihan, kunsan ance abinda babba ya hango yaro ko ya hau dutse ba zai hango ba, to duba da hakane yasa muka fahimci kamar da wani abu tsakaninka da Raihan, shi ya sa na ce bara mu tambayeku muji ko kuna son junanku?"
Tsaro ne matuk'a ya bayyana a fuskar Raihan duk ta zaro ido, yayin da Abdul zufa ta fara tsatsafo masa saboda jin abun banbarak'wai, wasu kirce-kirce ya fara ya rasa amsar da zai bayar, hakan yasa Abba cewa "Ka yi magana mana Abdul, ba za'a tauyeka ba ai."
Shiru ya sakeyi gabanshi na fad'uwa, Abbas ne yace "Abdul."
A hankali ya d'ago yace "Fad'a min gaskiya, kana son Raihan?"
Raihan da taji abun wani iri tashi tayi da gudu ta haura sama ta shige d'akin ta suna kallo, murmushi Sameera tayi kafin tace "Ita ta amince, saura kai."
Shima yunk'urawa yayi cike da kunya da murmushi ya nufi d'akinsu da suke sauka idan sun zo nan, Abbas ne yace "Bamu fahimci komai ba Abdul, hakan na nufin ka amince kenan?"
Juyowa yayi cike da kunya ya d'an jinjina kai alamar eh, da sauri ya k'arasa sama shima ya bi kusurwar da zata sadasu da na shi d'akin, Abba ne ya kalli Abbas yace "Amma ya kuka barshi ya tafi baku fad'a mi shi sharad'in ba?"
Abbas ne yace "Abba karku damu da wannan, na muku alk'awarin kawo muku sakamakon gwajin Abdul nan da kwana biyu insha Allahu."
"Shikenan Allah ya yarda." Suka amsa da "Ameen."
Umma da Abba b'angarensu suka koma inda Abbas ya wata kusurwar wacce ka d'auka wani sabon gida ne a ciki, sai Sameera da ta haura sama ta shiga d'akin Raihan, tsaye ta sameta ta saka kayan baccinta tana caje gashinta, zaune tayi bakin gado harta juyo ta kalleta tace "Ammie ke ce?"
Murmushi kawai ta mata, takowa tayi ta zo ta zauna tana turo baki gaba cikin shagwab'a ta rik'o hannun Sameera tace "Ammie, wai akan me Dady yake magana ne?"
Murmushi sosai Sameera tayi tace "Wai baki fahimci me yake magana akai ba? Kee 'yan matana fad'a min gaskiya kedai."
K'ara had'e rai tayi tace"Ammie, da gaske na ke fa." Shafa kanta Sameera tayi tace."To in tambayeki mana? Tsakani da Allah Abdul baya birgeki?"
Saida ta juya idonta kafin tace "Ammie, yana birgeni mana, kamar yaya na d'auke shi fa."
*Mu had'u a shafi na gaba insha Allah.*✋
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe*👏
27/05/2020 à 14:46 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*SANIN MASOYI*
_(sai Allah)_
*BAYA DA K'URA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
💞 _*MASOYA NA*_💕
*😂 Nasan za ku sha mamaki sosai ganin na dawo da ci gaban sanin masoyi, to ku kwantar da hankulanku kusha kallo kawai, duba da akwai wasu abubuwa daya kamatain ace an warwaresu tun a na farko, amma Allah bai nufa ba sai yanzu idan ya ara mana rai da lafiya, insha Allahu abun zai k'ayatar da ku fiye ma da na farko, kuma wannan shi zai zama na k'arshe da yardar Allah.*
_Bismillahir rahamanir rahim_
_1_
_Idan masu karatu basu manta ba mun tsaya a waccen labarin *Sameera* na da ciki na wata biyar, sannan Abbas na shirin had'a *Raihan* aure da *Abdul* d'an wajen Abbas mai biwa *Husnah* da zaran ta kammala secondary d'in ta, to zamu d'auki labarin daga bayan haihuwar Sameera muyi gaba insha Allah._
*Abbas* ne zaune tare da Abba (mahaifin Sameera Mus'ab) da kuma Umma (mahaifiyar Abbas Falmata) a gefensu, cikin hushi Abba yace "Ina! Wannan ma maganar banza ce, wallahi ba zan tab'a bari ku had'a *Raihan* da tsatson wannan mutumin ba, *Abba*? Ina! Ba dai d'an Abba ba wallahi, mutumin daya cutar da kai ya cuce mu gaba d'aya."
Cikin taushin murya da nutsuwa Umma tace "A gaskiya nima abin bai kwanta min a rai ba, kuma naga ma du-du-du yaron shekararshi nawa? Bai ko gama mallakar hankalin kanshi ba, sannan ita kanta Raihan d'in nawa take da har zaku fara maganar aurar da ita? Shekara goma fa, ba kwa tunanin ku zo ku tsayar da magana akan ga wanda za'a bata, a k'arshe zuciyarta ta kamu da son wani kuma ba shi ba, tunda zata ci gaba da zuwa makarantarta ai."
Abba ne yace "Wannan ma abun dubawa ne, irin wannan had'in tun da k'uruciya yana da matsala gaskiya, bansan me kuka gani ba da har kuke tunani had'a su."
Cike da kulawa *Sameera* ta kalleta tace "Hakane Umma, amma ai ba yanzu za'a musu auren ba, sai nan da shekara hud'u, kunga a lokacin ya samu cikakkiyar shekara ashirin da uku, ita kuma ta koba komai dai ta zama balagaggiya, sannan ba zamu had'a su bane haka kawai, zamu fara tambayar ra'ayin du akan lamarin."
"Yanzu in banda abinki *takwarata* ina Raihan ina wani sanin so? Ko ta amsa miki da eh wallahi idan ta mallaki hankalin kanta zata iya canza magana, 'yar shekara goma fa ake miki magana ba 'yar sha shida ba ko sama da haka."
Cikin tafasar zuci Abba yace "Kunga, ni ba k'arancin shekarun yaron bane damuwa ta, tunda ko yanzu aka mishu aure za'a samu kyakyawan sakamako daga gareshi ta hanyar zuri'a, kuma idan da shak'uwa da fahimta duk wannan ba matsala bace a tsakaninsu, kawai dai yaron ne bai min ba saboda kasancewarshi d'an mak'iyina."
A hankali *Abbas* ya d'ago ya kallesu cikin nutsuwa da girmamawa yace "Abba, Umma, sam banyi tunanin wannan maganar zata iya rasa muhalli a zuk'atanku, Abba, ko fa ubangijin daya hallicemu baya kamamu da laifin da waninmu ya aikata, ina ganin kamar rashin adalci ne da kuma dacewa ace zamu hukunta *Abdul Malik* akan laifin da mahaifinshi ne ya aikata, duba da lokacin da abun ya faru ko kanshi bai sani ba, namiji ne shi ba kuma lallai yayi halayyar mahaifinshi ba, zamu iya cewa mu shaidane akan hallayarshi, bai kamata mu hanashi auren Raihan ba in har suna son junansu, ko 'yar uwarshi *Husna* ta samu miji tayi aure a dalilin rabin rayuwarta da tayi a gidan nan, ni da hannu na na bayar da aurenta Abba, shin kuna ganin ya kamata ace mu mun hana auren d'an su da 'yar mu saboda tunanin abinda mahaifinshi yayi? Bai dace ba hakan iyayena, kuyi hak'uri ku sawa yaran nan albarka, hak'ik'a idan kuka ce baku yarda ba za'a fasa dole, amma hakan ba zai mana dad'i ba."
A hankali Sameera tace "Gaskiya ne Abba, kuma na ga ko shi kansa Abban ai mun yafe masa laifin daya mana, kuma kuyi hak'uri ku yafe masa sannan ku manta da baya, duba da mutumin nan yanzu baya raye a doron duniya."
Kallon juna Abba da Umma sukayi kafin Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan, mun amince, amma abisa wani sharad'i guda d'aya."
Sameera ma da Abbas kallon juna sukayi kafin Abbas yace "Wane irin sharad'ine wannan Abba?"
Ba alamar wasa yace "Sai in kun amince za'a yi wa yaron gwajin cuta mai karya gwarkuwar jiki da ma sauran cututtuka masu had'ari wanda akan iya d'auka ta hanyar mu'amula."
Dafe kai Abbas yayi yana tunani, yasan halin gogon nasu in har basu amice ba to za'a fasa ne, dan haka ya d'an kalli Sameera wacce ita ma take kallonshi kafin ya kallesu yace "Shikenan Abba, mu ma mun amince."
"Shikenan, Allah ya tabbatar da alkairi." Cewar Abban, da "Ameen." Suka amsa da shi.
Sai Abba daya mik'e zai fita daga falon yana fad'in "A dole wai sai an raba mutum da matarsa, ni ina son amaryata amma kuke son saita min kishiya."
Dariya sukayi sai Umma da tace "Shi ya sa zanfi kowa farin ciki idan haka ta kasance, dan ko ba komai na rabu da kishiya d'aya."
Suma mik'ewa duka sukayi suka nufi b'angaren nasu Abbas, masha Allah falon ya had'u iya had'uwa, gashi duk yaran dake d'akin kowa harkar gabanshi yake amma cikin nutsuwa, sai Raihan dake zaune kan kujera da littafi tana karatu, sai kuma Abdul dake gefe tare da k'aninshi *Jabir* suna danna wayoyinsu, duka zaune sukayi kafin Sameera tace "Ku tashi kuje ku kwanta dare yayi."
Kusan duka yaran suka amsa da "Ok Ammie." Mik'ewa sukayi inda kowa ya nufi nashi d'akin, Raihan ma tashi tayi sai Sameera ce tace " *Mamana* zo nan."
Cikin sanyi jiki da nutsuwa wanda ya zama halitar yarinyar ta taho ko kallon idon mahaifiyarta ba tayi ba harta zaune kusa da ita, Abdul ma da Ameer zasu mik'e Abba yace "Kai Jabir kaje, Abdul ka zauna zamuyi magana."
Cikin tsananin fad'uwar gaba da fargaba ya zame ya zauna k'asa duk da Abbas yace ya zauna inda yake, shiru falon ya d'auka kafin Abba yace "Abdul, abinda yasa nace ka zauna dama ba wani abu bane, ni da iyaye da kuma mai sunan Mamana (Sameera) munyi wata shawara akan ku kai da Raihan, kunsan ance abinda babba ya hango yaro ko ya hau dutse ba zai hango ba, to duba da hakane yasa muka fahimci kamar da wani abu tsakaninka da Raihan, shi ya sa na ce bara mu tambayeku muji ko kuna son junanku?"
Tsaro ne matuk'a ya bayyana a fuskar Raihan duk ta zaro ido, yayin da Abdul zufa ta fara tsatsafo masa saboda jin abun banbarak'wai, wasu kirce-kirce ya fara ya rasa amsar da zai bayar, hakan yasa Abba cewa "Ka yi magana mana Abdul, ba za'a tauyeka ba ai."
Shiru ya sakeyi gabanshi na fad'uwa, Abbas ne yace "Abdul."
A hankali ya d'ago yace "Fad'a min gaskiya, kana son Raihan?"
Raihan da taji abun wani iri tashi tayi da gudu ta haura sama ta shige d'akin ta suna kallo, murmushi Sameera tayi kafin tace "Ita ta amince, saura kai."
Shima yunk'urawa yayi cike da kunya da murmushi ya nufi d'akinsu da suke sauka idan sun zo nan, Abbas ne yace "Bamu fahimci komai ba Abdul, hakan na nufin ka amince kenan?"
Juyowa yayi cike da kunya ya d'an jinjina kai alamar eh, da sauri ya k'arasa sama shima ya bi kusurwar da zata sadasu da na shi d'akin, Abba ne ya kalli Abbas yace "Amma ya kuka barshi ya tafi baku fad'a mi shi sharad'in ba?"
Abbas ne yace "Abba karku damu da wannan, na muku alk'awarin kawo muku sakamakon gwajin Abdul nan da kwana biyu insha Allahu."
"Shikenan Allah ya yarda." Suka amsa da "Ameen."
Umma da Abba b'angarensu suka koma inda Abbas ya wata kusurwar wacce ka d'auka wani sabon gida ne a ciki, sai Sameera da ta haura sama ta shiga d'akin Raihan, tsaye ta sameta ta saka kayan baccinta tana caje gashinta, zaune tayi bakin gado harta juyo ta kalleta tace "Ammie ke ce?"
Murmushi kawai ta mata, takowa tayi ta zo ta zauna tana turo baki gaba cikin shagwab'a ta rik'o hannun Sameera tace "Ammie, wai akan me Dady yake magana ne?"
Murmushi sosai Sameera tayi tace "Wai baki fahimci me yake magana akai ba? Kee 'yan matana fad'a min gaskiya kedai."
K'ara had'e rai tayi tace"Ammie, da gaske na ke fa." Shafa kanta Sameera tayi tace."To in tambayeki mana? Tsakani da Allah Abdul baya birgeki?"
Saida ta juya idonta kafin tace "Ammie, yana birgeni mana, kamar yaya na d'auke shi fa."