Sashe 115
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Masifar da take yi ce tasa kawu Mamu fitowa daga d'aki, yana ganin Zeituna shima ya d'ora tashi masifar har da cewa "To ki fad'a min d'an uban waye shi a gidan? Wallahi sai naje har gidan da kaina na rama mata marinta, ke a gaban uwarshi da ubanshi ma zan rama mata dan ya gane tana da gata, dan ba zai kumbura min fuskar yarinya kuma ya tafi a banza ba."
Ita dai kallonsu kawai take, saida kawu ya gama sannan tace "Kawu ya jikin naka? Da sauk'i?"
Cike da tijara yace "Wane jiki kuma? Ni dama lafiyata lau, kawai nace ta fad'a miki hakane dan na samu kud'i a hannunki, dan naga baki damu da mu ba tunda kikayi auren nan, yanzu gashi wannan shegen Janu (Jano) yake ko uban wa ya saka ni gaba akan kud'in shi har yana ikrarin cewa zai rufe ni, to ba dole na samu kud'i ko ta halin yaya ba na biyashi kafin ya rufe ni."
Cikin rashin jin dad'i tace "Kawu har nawa yake biyanka ne?"
"To ni na sani ne? Kawai ba dai ya bani kud'in na karb'a ba a lokacin ina jin dad'in ganinsu, amma dai nasan zasu kai jaka d'ari biyu."
D'an zaro ido tayi tace "Kawu d'ari biyu?" Jumma ce tace "Eh, sunyi yawa ne? Ke yanzu a matsayin da kike ai wannan kud'in ba komai bane a wurink."
Kallonta tayi cike da damuwa tace "Inna Jumare wallahi bana da wannan kud'in, ina zan samu d'ari biyu ni kuma?"
Kallon sama da k'asa ta mata tace "Kiji tsoron Allah Zeituna, dubi kayan jikinki fa, dubi sark'a da d'an kunnen dake jikinki, dubi jakarki ma abar kallo ce, kuma kice baki da wannan kud'in?"
"Amma Inna..." Kawu Mamu ne ya katse da fad'in "Ni ban damu da wannan ba, ba lallai sai ke zaki bayar ba ai, ba ga mijinki ba? Ki fad'a masa halin da nake ciki mana, shi da girmanshi da komai zai bari ne a d'aure sirikinshi a garin nan, kawai ki fad'a masa ke dai zaisan abunyi."
Iska ta furzar cike da damuwa da halinsu tana tunanin yanda zata fara tambayarsa kud'i masu yawa haka, sai yanzu ta fara nadamar k'in amsar kyautar da yake yawan yi mata lokuta da dama, yakan bata kud'i yace ko zatayi wani abun ba sai ta tambaye shi ba, tunda yer uwarta na zuwa aiki ita kuma bata damu ba, amma sai tace bata so bata buk'atar komai, idan ya matsata sai tace ya rik'e idan ta tashi zata tambaye shi. Yanzu gashi bukatar kud'in ta taso mata sai dai masu yawan da ba zata iya tambayarshi ba, ajiyar zuciya tasauke kallesu tace "Shikenan kawu, zan san abunyi dai."
"Da dai yafi." Cewar kawu Mamu, Jumma ce tace "Zeituna wai uban waye ya marar min yarinya?"
D'an murmushi Zeituna tayi tace "Inna Jumare d'an shi ne fa."
"D'an shi? Kuma shine baki rama mata ba saboda kina so ki nuna mishi ba kya k'aunarta."
Wani kallo Zeituna ta mata, na rama mata? Yah Ammar d'in zan mara? Lallai baki san waye shi ba, to ai ko ni har yanzu ban wuce ya galla min mari ba, wayarta ce tayi k'ara ta fito da ita daga jaka, saida ta ga sunan kad'ai ta iya tuna ashe fa tare suke, da sauri ta juyo dan fitowa ta same shi tana fad'in "Na manta ashe yana waje."
Kallon juna sukayi inda kawu Mamu yace "Kinji shiririta, tare suke ta baro shi waje."
Duk hayaniyar da suke a cikin gidan yana ji, sai dai rabi fulatanci ne rabi kuma hausa, hakanne yasa shi cabko matsalar da suke magana akai, sannan yaji sunan d'an shi ma ya fito da kuma ta'asar da yayi, dan haka ya kirata a waya dan da alama ta manta shi a k'ofar gidan. Tana zuwa ta marairaice tace "Alhaji kayi hak'uri dan Allah na barka k'ofar gida, wallahi su kawu ne suka rik'e ni da magana."
Babu alamar wasa a tare dashi yace "Me yake faruwa? waye zai rufe shi akan kud'i? Me kuma ya had'a Ammar da Jumare?"
Baki ta saki tana kallonshi da mamaki da kuma rashin jin dad'i, kenan ya ji komai? Oh Allah, cikin taushin murya tace "Ba komai."
Kafeta yayi da ido yace "Ya zaki ce ba komai, duk da ban ji komai ba amma ai na fahimci inda zancen ya dosa, fad'a min meke faruwa?"
Cike da rangaji tace "Idan mun koma gida zan fad'a maka, amma Abban Ammar ban so kayi hushi."
"Shikenan, yanzu ya mai jikin?" Dariya ce ta kubce mata ta rufe baki, dan ya bata dariya sosai data tambaya, hakan na nufin baiji abinda aka fad'a anan ba kam, klonta yayi yace "Meye?"
Girgiza kai kawai tayi ba tace komai ba tace "Shigo muje." Girgiza kai yayi da sauri yace "A'a, idan dai zasu iya ki fad'a musu ina waje, in kuma kwance suke kawai ki gaishe min su sai ki fito mu koma."
Kamar zata fashe da kuka tace "Lahh, na d'auka fa nan zaka barni da naga mun taho da wuri."
Hararanta yayi yace "Lafiya kike? A halin da kike ciki kulawa kike buk'ata, sannan hidimar da akayi duk kin gama wahalar min da kanki da baby na, dan haka ba zan barki ba, ki shiga ki fito mu koma daga baya kya dawo ganinsu."
Juyawa tayi ta nufi ciki har da buga k'afafu take tana kukan shagwab'a, da murmushin birgewa ya bita cike da k'aunar yarinyar. Tare suka fito da kawu Mamu suka gaisa sosai, da zai tafi ma wasu kud'in ya sake bashi, babu kunya babu kawaici ya karb'a yana godiya kafin ya koma ciki suma suka tafi.
Tun a hanya ya sake tambayarta abinda ke faruwa, tsaf ta fad'a mishi amma banda marin da Ammar ya wa Jumare, dan haka yace "To ita kuma Jumare da waccen ya mareta fa?"
Cikin turo baki tace "Jumare fa rashin kunya ta min shine ya hukunta ta."
Kallonta yayi yace "Ban gane ba? To shi shi ta wa da zai mareta? Ke fa naga alama kin d'aukeshi wani mutumin arzik'i."
Wani kallo ta mishi mai kama da na tsani kalmar daka fad'a, sake kallonta yayi sai yaga ta k'ura mishi ido tana kallo, d'aga mata gira yayi yace "Lafiya?"
Had'e rai tayi sosai alamar bata ji dad'i ba tare da kawar da kanta gefe, cikin d'an d'aga murya yace "Wai meye? Wani abu na fad'a daya b'ata miki rai ne?"
Juyowa tayi cikin tsananin masifa har ta manta dawa za tayi magana sai ta fara fulatanci tana fad'in "Gaskiya ni na baku kyautawa, d'an da kuka haifa a ciki kuna fad'a mishi duk abinda ya zo bakinku, yanzu meye na wani cewa wai ina ganinshi kamar mutumin arzik'i, to mutumin banza ne dama? Akan me zaka fad'i haka a kanshi?"
Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata bakin, yanda ko wane harafi ke fita na bakinta abun birgewa, masifa take amma kuma ta mata kyau, sai dai abun takaicin baiji komai data fad'a ba, bakinta kawai ya gani yana motsawa da sautin harrufan da take furtawa, kallon gabanshi yayi yace "Idan kin gama fad'an saiki fad'a min me kika ce ko."
Sak'e tayi ta kalleshi, wai dama ba da hausa tayi magana ba? Kawar da kanta kawai tayi ita ma har suka isa gida, katari kam suna shiga sun aje motarsu Ammar shi kuma zai shiga tashi motar, da mutuntawa ta kalli Zeituna yace "Uwa barka, daga pakarey ake?"
Murmushi tayi duk da bata san me yake nufi da pakarey d'in ba, kallon lieutenant yayi yace "Alhaji ya ake ciki?"
Banza yayi da shi zai wuce Zeituna ta d'an rik'o rigarshi, tsayawa yayi ya juyo ya kalleta da alamar tambayar lafiya, saida tayi kamar zata fad'a jikinshi ta kashe murya sosai tace "Magana fa yake maka, dan Allah ka amsa mishi, laifin me yayi maka?"
Cikin fad'a yace "Ke baki ji me yayi bane? Ina ubanshi zai wani ce min ya ake ciki, dallah rabu dani."
Fizge rigarshi yayi ya juya zai wuce, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in "Shikenan nagode da abinda ka min."
Juyowa yayi yana ganinta ya dawo yana fad'in "Wai ke meye haka? Dan Allah wuce muje."
Juyawa tayi ta kalli Ammar daya ke daf da shiga mota sannan ta kalle shi tace "Babu inda zanje yau sai na gani da ido na kuma naji da kunnuwa na ka lokacin da zaka sa mishi albarka, inba haka ba kuma yanzun nan na koma inda muka je yanzun."
Yanda tayi maganar ya nuna rigima take ji, sai dai shi a wurin shi ba wani abu bane da ita take kambama shi har haka, turo baki yayi kamar yaro yace "Kira shi to."
Take murmushi ya maye gurbin fuskar shanun nan, sam farin ciki yasa ta manta sai ta k'walla kiran sunan Ammar daya shiga mota har ya tayar, bai ji kiran farko ba saida ta kura shi sau uku sannan ya fito daga motar, cike da takon k'asaita ya zo gabansu ya tsaya yana kallonsu.
Kallonshi lieutenant yayi babu annuri yace "...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
✪{T . N}✪📖🖊️
https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl
_Bismillahir rahamanir rahim_
_40_
"Ina zaka je yanzu da dare? Baka san yanzu ka girma bane?"
Wata yar banzar dariya ya bushe da ita kamar da bakin k'warya, galala Zeituna ke kallonshi inda lieutenant ya nuna mata da yatsa yace " Kin gani? Ina fatan yanzu kin fahimci wani abu."
Babu alamar wasa a fuskarta ta kalleshi tace "Tambayar daka mishi ai tana nuna damuwarka ne a kanshi, shi kuma abun ya zo mishi a bazata ne, na tabbata abinda ya bashi dariya kenan, idan kuma baka yarda ba ka tambaye shi kaji."
Kallon Ammar yayi da har yanzu ke dariya har da rik'e ciki yace "Dallah ka mana shiru malam."
Ita dai kallonsu kawai take, saida kawu ya gama sannan tace "Kawu ya jikin naka? Da sauk'i?"
Cike da tijara yace "Wane jiki kuma? Ni dama lafiyata lau, kawai nace ta fad'a miki hakane dan na samu kud'i a hannunki, dan naga baki damu da mu ba tunda kikayi auren nan, yanzu gashi wannan shegen Janu (Jano) yake ko uban wa ya saka ni gaba akan kud'in shi har yana ikrarin cewa zai rufe ni, to ba dole na samu kud'i ko ta halin yaya ba na biyashi kafin ya rufe ni."
Cikin rashin jin dad'i tace "Kawu har nawa yake biyanka ne?"
"To ni na sani ne? Kawai ba dai ya bani kud'in na karb'a ba a lokacin ina jin dad'in ganinsu, amma dai nasan zasu kai jaka d'ari biyu."
D'an zaro ido tayi tace "Kawu d'ari biyu?" Jumma ce tace "Eh, sunyi yawa ne? Ke yanzu a matsayin da kike ai wannan kud'in ba komai bane a wurink."
Kallonta tayi cike da damuwa tace "Inna Jumare wallahi bana da wannan kud'in, ina zan samu d'ari biyu ni kuma?"
Kallon sama da k'asa ta mata tace "Kiji tsoron Allah Zeituna, dubi kayan jikinki fa, dubi sark'a da d'an kunnen dake jikinki, dubi jakarki ma abar kallo ce, kuma kice baki da wannan kud'in?"
"Amma Inna..." Kawu Mamu ne ya katse da fad'in "Ni ban damu da wannan ba, ba lallai sai ke zaki bayar ba ai, ba ga mijinki ba? Ki fad'a masa halin da nake ciki mana, shi da girmanshi da komai zai bari ne a d'aure sirikinshi a garin nan, kawai ki fad'a masa ke dai zaisan abunyi."
Iska ta furzar cike da damuwa da halinsu tana tunanin yanda zata fara tambayarsa kud'i masu yawa haka, sai yanzu ta fara nadamar k'in amsar kyautar da yake yawan yi mata lokuta da dama, yakan bata kud'i yace ko zatayi wani abun ba sai ta tambaye shi ba, tunda yer uwarta na zuwa aiki ita kuma bata damu ba, amma sai tace bata so bata buk'atar komai, idan ya matsata sai tace ya rik'e idan ta tashi zata tambaye shi. Yanzu gashi bukatar kud'in ta taso mata sai dai masu yawan da ba zata iya tambayarshi ba, ajiyar zuciya tasauke kallesu tace "Shikenan kawu, zan san abunyi dai."
"Da dai yafi." Cewar kawu Mamu, Jumma ce tace "Zeituna wai uban waye ya marar min yarinya?"
D'an murmushi Zeituna tayi tace "Inna Jumare d'an shi ne fa."
"D'an shi? Kuma shine baki rama mata ba saboda kina so ki nuna mishi ba kya k'aunarta."
Wani kallo Zeituna ta mata, na rama mata? Yah Ammar d'in zan mara? Lallai baki san waye shi ba, to ai ko ni har yanzu ban wuce ya galla min mari ba, wayarta ce tayi k'ara ta fito da ita daga jaka, saida ta ga sunan kad'ai ta iya tuna ashe fa tare suke, da sauri ta juyo dan fitowa ta same shi tana fad'in "Na manta ashe yana waje."
Kallon juna sukayi inda kawu Mamu yace "Kinji shiririta, tare suke ta baro shi waje."
Duk hayaniyar da suke a cikin gidan yana ji, sai dai rabi fulatanci ne rabi kuma hausa, hakanne yasa shi cabko matsalar da suke magana akai, sannan yaji sunan d'an shi ma ya fito da kuma ta'asar da yayi, dan haka ya kirata a waya dan da alama ta manta shi a k'ofar gidan. Tana zuwa ta marairaice tace "Alhaji kayi hak'uri dan Allah na barka k'ofar gida, wallahi su kawu ne suka rik'e ni da magana."
Babu alamar wasa a tare dashi yace "Me yake faruwa? waye zai rufe shi akan kud'i? Me kuma ya had'a Ammar da Jumare?"
Baki ta saki tana kallonshi da mamaki da kuma rashin jin dad'i, kenan ya ji komai? Oh Allah, cikin taushin murya tace "Ba komai."
Kafeta yayi da ido yace "Ya zaki ce ba komai, duk da ban ji komai ba amma ai na fahimci inda zancen ya dosa, fad'a min meke faruwa?"
Cike da rangaji tace "Idan mun koma gida zan fad'a maka, amma Abban Ammar ban so kayi hushi."
"Shikenan, yanzu ya mai jikin?" Dariya ce ta kubce mata ta rufe baki, dan ya bata dariya sosai data tambaya, hakan na nufin baiji abinda aka fad'a anan ba kam, klonta yayi yace "Meye?"
Girgiza kai kawai tayi ba tace komai ba tace "Shigo muje." Girgiza kai yayi da sauri yace "A'a, idan dai zasu iya ki fad'a musu ina waje, in kuma kwance suke kawai ki gaishe min su sai ki fito mu koma."
Kamar zata fashe da kuka tace "Lahh, na d'auka fa nan zaka barni da naga mun taho da wuri."
Hararanta yayi yace "Lafiya kike? A halin da kike ciki kulawa kike buk'ata, sannan hidimar da akayi duk kin gama wahalar min da kanki da baby na, dan haka ba zan barki ba, ki shiga ki fito mu koma daga baya kya dawo ganinsu."
Juyawa tayi ta nufi ciki har da buga k'afafu take tana kukan shagwab'a, da murmushin birgewa ya bita cike da k'aunar yarinyar. Tare suka fito da kawu Mamu suka gaisa sosai, da zai tafi ma wasu kud'in ya sake bashi, babu kunya babu kawaici ya karb'a yana godiya kafin ya koma ciki suma suka tafi.
Tun a hanya ya sake tambayarta abinda ke faruwa, tsaf ta fad'a mishi amma banda marin da Ammar ya wa Jumare, dan haka yace "To ita kuma Jumare da waccen ya mareta fa?"
Cikin turo baki tace "Jumare fa rashin kunya ta min shine ya hukunta ta."
Kallonta yayi yace "Ban gane ba? To shi shi ta wa da zai mareta? Ke fa naga alama kin d'aukeshi wani mutumin arzik'i."
Wani kallo ta mishi mai kama da na tsani kalmar daka fad'a, sake kallonta yayi sai yaga ta k'ura mishi ido tana kallo, d'aga mata gira yayi yace "Lafiya?"
Had'e rai tayi sosai alamar bata ji dad'i ba tare da kawar da kanta gefe, cikin d'an d'aga murya yace "Wai meye? Wani abu na fad'a daya b'ata miki rai ne?"
Juyowa tayi cikin tsananin masifa har ta manta dawa za tayi magana sai ta fara fulatanci tana fad'in "Gaskiya ni na baku kyautawa, d'an da kuka haifa a ciki kuna fad'a mishi duk abinda ya zo bakinku, yanzu meye na wani cewa wai ina ganinshi kamar mutumin arzik'i, to mutumin banza ne dama? Akan me zaka fad'i haka a kanshi?"
Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata bakin, yanda ko wane harafi ke fita na bakinta abun birgewa, masifa take amma kuma ta mata kyau, sai dai abun takaicin baiji komai data fad'a ba, bakinta kawai ya gani yana motsawa da sautin harrufan da take furtawa, kallon gabanshi yayi yace "Idan kin gama fad'an saiki fad'a min me kika ce ko."
Sak'e tayi ta kalleshi, wai dama ba da hausa tayi magana ba? Kawar da kanta kawai tayi ita ma har suka isa gida, katari kam suna shiga sun aje motarsu Ammar shi kuma zai shiga tashi motar, da mutuntawa ta kalli Zeituna yace "Uwa barka, daga pakarey ake?"
Murmushi tayi duk da bata san me yake nufi da pakarey d'in ba, kallon lieutenant yayi yace "Alhaji ya ake ciki?"
Banza yayi da shi zai wuce Zeituna ta d'an rik'o rigarshi, tsayawa yayi ya juyo ya kalleta da alamar tambayar lafiya, saida tayi kamar zata fad'a jikinshi ta kashe murya sosai tace "Magana fa yake maka, dan Allah ka amsa mishi, laifin me yayi maka?"
Cikin fad'a yace "Ke baki ji me yayi bane? Ina ubanshi zai wani ce min ya ake ciki, dallah rabu dani."
Fizge rigarshi yayi ya juya zai wuce, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in "Shikenan nagode da abinda ka min."
Juyowa yayi yana ganinta ya dawo yana fad'in "Wai ke meye haka? Dan Allah wuce muje."
Juyawa tayi ta kalli Ammar daya ke daf da shiga mota sannan ta kalle shi tace "Babu inda zanje yau sai na gani da ido na kuma naji da kunnuwa na ka lokacin da zaka sa mishi albarka, inba haka ba kuma yanzun nan na koma inda muka je yanzun."
Yanda tayi maganar ya nuna rigima take ji, sai dai shi a wurin shi ba wani abu bane da ita take kambama shi har haka, turo baki yayi kamar yaro yace "Kira shi to."
Take murmushi ya maye gurbin fuskar shanun nan, sam farin ciki yasa ta manta sai ta k'walla kiran sunan Ammar daya shiga mota har ya tayar, bai ji kiran farko ba saida ta kura shi sau uku sannan ya fito daga motar, cike da takon k'asaita ya zo gabansu ya tsaya yana kallonsu.
Kallonshi lieutenant yayi babu annuri yace "...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
✪{T . N}✪📖🖊️
https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl
_Bismillahir rahamanir rahim_
_40_
"Ina zaka je yanzu da dare? Baka san yanzu ka girma bane?"
Wata yar banzar dariya ya bushe da ita kamar da bakin k'warya, galala Zeituna ke kallonshi inda lieutenant ya nuna mata da yatsa yace " Kin gani? Ina fatan yanzu kin fahimci wani abu."
Babu alamar wasa a fuskarta ta kalleshi tace "Tambayar daka mishi ai tana nuna damuwarka ne a kanshi, shi kuma abun ya zo mishi a bazata ne, na tabbata abinda ya bashi dariya kenan, idan kuma baka yarda ba ka tambaye shi kaji."
Kallon Ammar yayi da har yanzu ke dariya har da rik'e ciki yace "Dallah ka mana shiru malam."