Sashe 129
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Washe gari* da safe kusan duk familyn ne a falon kowa da wanda ya zo ya gaisar, Ammar ma suna kusa da Zeituna zaune shi da Amna, da k'yar Junaid ya matsa mata ta zo gaishe da mutanen ba dan ta so ba, shiyasa ma ko da ta shigo ko sallama ba tayi ba, tana kallo yana gaishe da kowa amma banda ita, ganin hakan yasa Ammar k'ura mata ido, ko shi dai ai yana gaishe da kowa da girmamawa, amma tsabar rashin kunya ita ba sallama kuma ba gaishe da mutane, ba fa zai d'auka ba, wannan iskancin ba za'a yi shi dashi ba. Junaid na juyowa inda yake dan su gaisa ya kula da kallon da yake mata, cikin dubara ya d'an ja gyalenta suka koma gefe, juyawa tayi zata fita Junaid ya bita da kallo, Ammar daya kula da kowa na wurin ya bita da kallo amma babu mai k'arfin halin da zaiyi magana yasa shi kallon Junaid yace "Matarka raina mutane ne tayi?"
Ido a tsaitsaye ya kalleshi fatanshi kawai su rabu lafiya, ita kuma juyowa tayi tana mishi wanni kallo tace "Kamar ya?"
Saida ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yace "Naga kamar kinfi k'arfin ki gaishe da mutane, me kike ji dashi to?"
Cike da rainin tace "Ina da wani abu d'aya a rayuwata, duk ta yanda aka zo min haka nake zuwa nima, an nuna min ba'a k'aunata a gidan nan, shiyasa nima ban nuna ina k'aunar kowa ba."
Idonta ya kalla yace "Amma ai kinsan girmama mutum ko? Sannan nan ba gidanki bane ko na mijinki, dolenki ki girmama duk wanda kika gani a ciki inhar kina da mutumci."
Murmushi ta masa ta rumgume hannaye a k'irji tace " Idan kuma bana da mutumcin fa?"
Mik'ewar da yayi tsaye yana d'an nad'e hannun rigarshi yasa Zeituna mik'ewa tana kallonshi tace "Dan Allah rabu da ita kaji, bata gajiya da rigima da kowa."
Kallon Zeituna yayi yace "Um um uwa barni, ina so ne na fad'a mata da yaren da zata fahimta, duk rigimar da take muku ai dan bata samu daidai da ita bane, ni ba ita zan tsawatar ma ba mijin nata zan dallawa mari a gabanta ta gani, hakan zaisa ta shiga taitayinta."
Kallon Junaid yayi rai a b'ace yace "Yo ba dan ma ya d'auki mutane 'yan iska ba har wacece wannan yarinyar da zata zauna tana mana fitsara, yaushe ta shigo gidan naka har ta fara baka kulawar da kake ganin ta isa ta taka iyayenka kuma ta zauna lafiya, to in kai ka zama fanko wallahi ni akan iyayena babu yar iskar data nemi ta raina min su kuma na kalleta, dan ubanta kuma ta jaraba ta gani idan ban fizgo hanjin yarinya ba ta baki, to miye a cikin ido banda ruwa."
"Da kyau Ammar, nagode, ka tabka rashin mutumcinka yau Hajia Zeeya'atu na bayanka, tunda shi gindinta ya mishi shamaki da zuciya."
Kowa saida ya kalli Hajia da tayi maganar nan, Amna sagale ta kalle ta wacce ta tsargu da abinda ya fad'a take jin kamar da ita yake tunda dai ita ce matarshi, Ammar kuma a ranshi yace "Tunda rashin mutumci ne kenan kin d'aure min gindi? To na fasa."
Maryama ce tace "To sai me? Ka mari mijina a gabana ka gani, wallahi da nima saina tsinke matarka da mari kuma a gabanka naga me zai faru."
Juyawa yayi ya kalli Amna dake zaune ya tintsire da dariya ya nuna Amna yace "Ke wannan? Jar bala'i! Wallahi kuwa da kinja yau kowa ya kwana da yunwa, ke ki bar bala'i yayi kwana kinji, bana fad'a da mace ni sai maza mazan ma wanda suka k'osa, idan kuma kika cikani sai dai nasa 'yar aljannata ta d'aukar min ke ta cilla a garu."
Cikin taushin murya Amar yace "Dan Allah d'an uwa ka rabu da ita."
Kallon Maryama yayi ita ma yace "Gaskiya baki kyauta ba, banyi tsammanin haka daga gareki ba."
Zaune Ammar yayi yana kallon Amar yana fad'in "To dama me kake tsammani? Baka ga kakan nan nata ba mai masifar fad'a kamar Hajiar gidanmu."
Amar da suke kallon juna ne ya mishi alama da ido cewa Hajiar fa na kallonka, duk da ya fahimci me yake nufi sai kawai ya gyara zamanshi ya ci uwar fuska kamar bashi ba, Husseina kad'ai ta iya fito da dariyarta amma sauran duk sun gimtse ta su, Hajia da kamar ta fashe ce tace "Shiyasa ba ma tab'a zama lafiya ni da kai, ba dai nice mai masifar fad'a ba? Zaka gani, akwai ranar da zaka nemi kaji ma fad'an nawa amma na maka nisa."
Kallonta yayi fuska a had'e yace "Haba Hajiata, raha ce fa kawai, ke kinsan dani dake bata b'acewa, fad'an ki ai ni jinshi nake kamar kukan tsintsaye matuk'ar dad'i a kunne."
Maryama dai basu ma san lokacin data fita ba tare da Junaid, yau ma fad'a sukayi sosai saboda yaji zafin abinda Ammar ya mishi, kuma yasan gaskiya ya fad'a mishi shiyasa ma bai biye mishi ba, amma fa daya mare shi da sai dai cikinsu d'aya ya kashe wani, yanzun ma k'ara fad'a mishi tayi dan sam zaman gidan nan nashi ya fice mata a rai, bata damu ta bar gidan ba tunda kowa na gidan baida mutumci a cewarta.
*Misalin 09:00* na safe Tanti Hadiza ta zo gidan, babban falon ta fara shiga cike da fargaban kalaman da zata ji daga Hajia, a lokacin tana d'akin Alhaji dan haka ta samu tarba mai kyau daga su Zeinabu da Soueiba da kuma Zeituna da bata tab'a ganinta ba ido da ido sai yau, a falon suke suna ta hira ta yaushe rabo inda suka cika mata gabanta da abun sha da ci, fitowar Hajia yasa duk wannan farin cikin ya b'ace kowa ta kama jikinta, duk da ta gane wacece amma bata wani kulata ba ta kalli Zeituna tace "Zaman me kuke anan? Ina ce aiki kuke a madafa."
"Eh Hajia." Ta fad'a tana mik'ewa ta nufi madafar, su Zeinabu ma mik'ewa sukayi inda Hadiza ke mamaki da maganar zuci cewa "Har yanzu bata canza ashe, yaushe matar nan zata daina bautar da matan 'ya'yanta? Allah ya kyauta."
Daga tsaye take k'are mata kallo sama da k'asa, murmushin gefen labb'a ta mata ta kawar da kai daga kallonta tana danna wayar hannunta tace "Wani ko a cikin kaskon mai ka saka shi haka zaka ciro shi a tsiyace, ank'i d'ana ba, amma sanyin ac da abincin gidanshi kad'ai ya isa ya gyara maka jiki."
Nufa tayi kan kujerarta ta zauna k'afa d'aya kan d'aya tace "Ina manta wani abu fa, wasu haka suke zuwa duniya a wahalce kuma su koma babu nasara."
Ita ma murmushin tayi wanda bai fito da hak'oranta ba ta mik'e tana kallonta tace "Ina kwana Hajia."
K'ala ba tace mata ba dan haka ta juya zata fita sai kuma ta kalleta tace "Ba wai zama a cikin daula bane ke nuna kayi nasarar zuwanka duniya, ni a gurina nasarar da soyayyata ma tayi ma nasara ce, wasu basa da sa'ar zama da wanda suke so, ni kuma yanzu haka ina cikin farin cikin da na tabbatar sauran matan gidan nan basa cikinshi, idan kuma k'arya na fad'a ki tambayi kowace kiji zata fad'a miki indai har gaskiya zasu fad'i."
Cikin ladabi ta sake kallonta tace "Kiyi hak'uri abisa abinda ya faru, ganin Amna na zo wacce kullum ke min k'orafin ban zo naga gidanta ba, kuma tace gidan jikin wannan yake shiyasa na lek'o mu gaisa kar nima na watsar daku kamar yanda kukayi, ko ba komai ina da 'ya'ya a gidan nan."
Fita kawai tayi ta barta, tana ganin gidan tasan shine dan haka kawai ta shiga, sallama ta dinga rafkawa har Jamila da Amna suka lek'o su da su kafi kusa, dukansu rumgumeta sukayi da farin ciki, Amna har kuka tayi na ganin mahaifiyarta, haka suka shiga ciki ta zuba mata kayan tab'awa inda suka bud'e shafin hira, a k'alla awanta uku kafin ta tashi suka shiga wajen Umaimah da Maryama suka gaisa, data fito zata tafi a lokacin Amna ke cewa "Mama ki jira yah Ammar yanzu zaki ganshi tunda na fad'a mishi kin zo, ba zaiji dad'i ba idan ya samu kin tafiyarki."
Dariya ta mata tace "To ni dashi kusan kullum ba muna had'uwa ba, kowace juma'a fa sai yaje madarunfa."
Zaro ido tayi tace "Mama kowace juma'a? Amma shine bai tab'a fad'a min ba."
Dariya tayi zatayi magana sai gashi ya shigo da makullin mota a hannu, da farin ciki da ladabi suka gaisa kafin yace "Tanti har kin fito ne? Amma ai baki jima ba."
Da murmushi tace "Haba dai ina laifi ai na jima anan, zan wuce can gida ne wajensu Inna zuwa bayan sallah la'asar kuma saina koma."
"Amma kun gaisa da mutanen ciki kuwa?" Saida tayi dariya ta kalleshi tace "Mun gaisa, harda kakarka ma."
Dariya yayi shima yace "Ashe kunsha hira." Dariya tayi kafin ta kalli Amna tace "Ki koma ciki ni zan tafi, sai kuma na sake dawowa ganinki ko auta."
Cikin shagwab'a ta kwantar da kanta a kafad'arta tace "Mama yaushe zaki dawo?"
Kallon Ammar tayi da tunanin abinda zata fad'a mata sai kawai yace "Sai kin haihu mana zata dawo."
Kunya ce tasa Amna k'ara sunkuyar da kanta tana murmushi, Tanti kuma a ranta tace "D'ana kenan, anyi halin ba ."
Ammar ne yace "Muje tanti saina ajeku." Kallonshi tayi tace "A'a haba daka barshi ma, watak'ila akwai abinda kake wannan shirmammar ta taso ka."
"Ku zo muje kawai, ai babu abinda yafi mana ku." Ya fad'a yana nufa hanyar fita, rik'eta Amna tayi sosai wai babu inda zata je, abu da gaske sai kuwa tasa kuka ita sai dai ta tafi da ita, ita ma rumgumeta tayi tana fad'in "Saurare ni auta, kina ji na da kyau?"
Ido a tsaitsaye ya kalleshi fatanshi kawai su rabu lafiya, ita kuma juyowa tayi tana mishi wanni kallo tace "Kamar ya?"
Saida ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yace "Naga kamar kinfi k'arfin ki gaishe da mutane, me kike ji dashi to?"
Cike da rainin tace "Ina da wani abu d'aya a rayuwata, duk ta yanda aka zo min haka nake zuwa nima, an nuna min ba'a k'aunata a gidan nan, shiyasa nima ban nuna ina k'aunar kowa ba."
Idonta ya kalla yace "Amma ai kinsan girmama mutum ko? Sannan nan ba gidanki bane ko na mijinki, dolenki ki girmama duk wanda kika gani a ciki inhar kina da mutumci."
Murmushi ta masa ta rumgume hannaye a k'irji tace " Idan kuma bana da mutumcin fa?"
Mik'ewar da yayi tsaye yana d'an nad'e hannun rigarshi yasa Zeituna mik'ewa tana kallonshi tace "Dan Allah rabu da ita kaji, bata gajiya da rigima da kowa."
Kallon Zeituna yayi yace "Um um uwa barni, ina so ne na fad'a mata da yaren da zata fahimta, duk rigimar da take muku ai dan bata samu daidai da ita bane, ni ba ita zan tsawatar ma ba mijin nata zan dallawa mari a gabanta ta gani, hakan zaisa ta shiga taitayinta."
Kallon Junaid yayi rai a b'ace yace "Yo ba dan ma ya d'auki mutane 'yan iska ba har wacece wannan yarinyar da zata zauna tana mana fitsara, yaushe ta shigo gidan naka har ta fara baka kulawar da kake ganin ta isa ta taka iyayenka kuma ta zauna lafiya, to in kai ka zama fanko wallahi ni akan iyayena babu yar iskar data nemi ta raina min su kuma na kalleta, dan ubanta kuma ta jaraba ta gani idan ban fizgo hanjin yarinya ba ta baki, to miye a cikin ido banda ruwa."
"Da kyau Ammar, nagode, ka tabka rashin mutumcinka yau Hajia Zeeya'atu na bayanka, tunda shi gindinta ya mishi shamaki da zuciya."
Kowa saida ya kalli Hajia da tayi maganar nan, Amna sagale ta kalle ta wacce ta tsargu da abinda ya fad'a take jin kamar da ita yake tunda dai ita ce matarshi, Ammar kuma a ranshi yace "Tunda rashin mutumci ne kenan kin d'aure min gindi? To na fasa."
Maryama ce tace "To sai me? Ka mari mijina a gabana ka gani, wallahi da nima saina tsinke matarka da mari kuma a gabanka naga me zai faru."
Juyawa yayi ya kalli Amna dake zaune ya tintsire da dariya ya nuna Amna yace "Ke wannan? Jar bala'i! Wallahi kuwa da kinja yau kowa ya kwana da yunwa, ke ki bar bala'i yayi kwana kinji, bana fad'a da mace ni sai maza mazan ma wanda suka k'osa, idan kuma kika cikani sai dai nasa 'yar aljannata ta d'aukar min ke ta cilla a garu."
Cikin taushin murya Amar yace "Dan Allah d'an uwa ka rabu da ita."
Kallon Maryama yayi ita ma yace "Gaskiya baki kyauta ba, banyi tsammanin haka daga gareki ba."
Zaune Ammar yayi yana kallon Amar yana fad'in "To dama me kake tsammani? Baka ga kakan nan nata ba mai masifar fad'a kamar Hajiar gidanmu."
Amar da suke kallon juna ne ya mishi alama da ido cewa Hajiar fa na kallonka, duk da ya fahimci me yake nufi sai kawai ya gyara zamanshi ya ci uwar fuska kamar bashi ba, Husseina kad'ai ta iya fito da dariyarta amma sauran duk sun gimtse ta su, Hajia da kamar ta fashe ce tace "Shiyasa ba ma tab'a zama lafiya ni da kai, ba dai nice mai masifar fad'a ba? Zaka gani, akwai ranar da zaka nemi kaji ma fad'an nawa amma na maka nisa."
Kallonta yayi fuska a had'e yace "Haba Hajiata, raha ce fa kawai, ke kinsan dani dake bata b'acewa, fad'an ki ai ni jinshi nake kamar kukan tsintsaye matuk'ar dad'i a kunne."
Maryama dai basu ma san lokacin data fita ba tare da Junaid, yau ma fad'a sukayi sosai saboda yaji zafin abinda Ammar ya mishi, kuma yasan gaskiya ya fad'a mishi shiyasa ma bai biye mishi ba, amma fa daya mare shi da sai dai cikinsu d'aya ya kashe wani, yanzun ma k'ara fad'a mishi tayi dan sam zaman gidan nan nashi ya fice mata a rai, bata damu ta bar gidan ba tunda kowa na gidan baida mutumci a cewarta.
*Misalin 09:00* na safe Tanti Hadiza ta zo gidan, babban falon ta fara shiga cike da fargaban kalaman da zata ji daga Hajia, a lokacin tana d'akin Alhaji dan haka ta samu tarba mai kyau daga su Zeinabu da Soueiba da kuma Zeituna da bata tab'a ganinta ba ido da ido sai yau, a falon suke suna ta hira ta yaushe rabo inda suka cika mata gabanta da abun sha da ci, fitowar Hajia yasa duk wannan farin cikin ya b'ace kowa ta kama jikinta, duk da ta gane wacece amma bata wani kulata ba ta kalli Zeituna tace "Zaman me kuke anan? Ina ce aiki kuke a madafa."
"Eh Hajia." Ta fad'a tana mik'ewa ta nufi madafar, su Zeinabu ma mik'ewa sukayi inda Hadiza ke mamaki da maganar zuci cewa "Har yanzu bata canza ashe, yaushe matar nan zata daina bautar da matan 'ya'yanta? Allah ya kyauta."
Daga tsaye take k'are mata kallo sama da k'asa, murmushin gefen labb'a ta mata ta kawar da kai daga kallonta tana danna wayar hannunta tace "Wani ko a cikin kaskon mai ka saka shi haka zaka ciro shi a tsiyace, ank'i d'ana ba, amma sanyin ac da abincin gidanshi kad'ai ya isa ya gyara maka jiki."
Nufa tayi kan kujerarta ta zauna k'afa d'aya kan d'aya tace "Ina manta wani abu fa, wasu haka suke zuwa duniya a wahalce kuma su koma babu nasara."
Ita ma murmushin tayi wanda bai fito da hak'oranta ba ta mik'e tana kallonta tace "Ina kwana Hajia."
K'ala ba tace mata ba dan haka ta juya zata fita sai kuma ta kalleta tace "Ba wai zama a cikin daula bane ke nuna kayi nasarar zuwanka duniya, ni a gurina nasarar da soyayyata ma tayi ma nasara ce, wasu basa da sa'ar zama da wanda suke so, ni kuma yanzu haka ina cikin farin cikin da na tabbatar sauran matan gidan nan basa cikinshi, idan kuma k'arya na fad'a ki tambayi kowace kiji zata fad'a miki indai har gaskiya zasu fad'i."
Cikin ladabi ta sake kallonta tace "Kiyi hak'uri abisa abinda ya faru, ganin Amna na zo wacce kullum ke min k'orafin ban zo naga gidanta ba, kuma tace gidan jikin wannan yake shiyasa na lek'o mu gaisa kar nima na watsar daku kamar yanda kukayi, ko ba komai ina da 'ya'ya a gidan nan."
Fita kawai tayi ta barta, tana ganin gidan tasan shine dan haka kawai ta shiga, sallama ta dinga rafkawa har Jamila da Amna suka lek'o su da su kafi kusa, dukansu rumgumeta sukayi da farin ciki, Amna har kuka tayi na ganin mahaifiyarta, haka suka shiga ciki ta zuba mata kayan tab'awa inda suka bud'e shafin hira, a k'alla awanta uku kafin ta tashi suka shiga wajen Umaimah da Maryama suka gaisa, data fito zata tafi a lokacin Amna ke cewa "Mama ki jira yah Ammar yanzu zaki ganshi tunda na fad'a mishi kin zo, ba zaiji dad'i ba idan ya samu kin tafiyarki."
Dariya ta mata tace "To ni dashi kusan kullum ba muna had'uwa ba, kowace juma'a fa sai yaje madarunfa."
Zaro ido tayi tace "Mama kowace juma'a? Amma shine bai tab'a fad'a min ba."
Dariya tayi zatayi magana sai gashi ya shigo da makullin mota a hannu, da farin ciki da ladabi suka gaisa kafin yace "Tanti har kin fito ne? Amma ai baki jima ba."
Da murmushi tace "Haba dai ina laifi ai na jima anan, zan wuce can gida ne wajensu Inna zuwa bayan sallah la'asar kuma saina koma."
"Amma kun gaisa da mutanen ciki kuwa?" Saida tayi dariya ta kalleshi tace "Mun gaisa, harda kakarka ma."
Dariya yayi shima yace "Ashe kunsha hira." Dariya tayi kafin ta kalli Amna tace "Ki koma ciki ni zan tafi, sai kuma na sake dawowa ganinki ko auta."
Cikin shagwab'a ta kwantar da kanta a kafad'arta tace "Mama yaushe zaki dawo?"
Kallon Ammar tayi da tunanin abinda zata fad'a mata sai kawai yace "Sai kin haihu mana zata dawo."
Kunya ce tasa Amna k'ara sunkuyar da kanta tana murmushi, Tanti kuma a ranta tace "D'ana kenan, anyi halin ba ."
Ammar ne yace "Muje tanti saina ajeku." Kallonshi tayi tace "A'a haba daka barshi ma, watak'ila akwai abinda kake wannan shirmammar ta taso ka."
"Ku zo muje kawai, ai babu abinda yafi mana ku." Ya fad'a yana nufa hanyar fita, rik'eta Amna tayi sosai wai babu inda zata je, abu da gaske sai kuwa tasa kuka ita sai dai ta tafi da ita, ita ma rumgumeta tayi tana fad'in "Saurare ni auta, kina ji na da kyau?"