Sashe 192
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"An je an kunyata kun, d'an iska ne ni to da zan tsaya ina lallab'a shi, Labaran fa shaidata ne nan muka je yaron nan ya bayar da hak'uri a gama komai amma ya k'i, to ya zamu mishi?"
A hassale yace "Hak'uri? Ya bawa uban wa hak'uri? Lusari ne shi da zai bayar da hak'uri? To ni daya bayar da hak'urin ma da sai na d'aga mishi nono." 😂
Da sauri lieutenant yace "Sakarai ina kaga nonon to? Kenan ka d'aure mishi gindi ya ci gaba da d'aukar rigima."
"Yo sai me? Mu ba rigimar ce ta kawo mu duniya ba? Kaga malam karka k'ara mana irin haka, a irin wannan lamarin ba'a ma yaro haka, yanda yake da laifi shima waccen yaron da laifinshi, tunda waya aike shi kula masa matarshi sannan yasa aka ma d'an uwanshi duka, da kaima ka tsaya a wajen ka kare d'anka ka nuna musu ba bare bane shi ko marar gata, amma saboda Allah saika wulak'antashi a gaban mutane."
Cikin jin haushi yace "To ubana, yanzu yanda za ayi idan zaka dawo ka taho da bulala sai ka zaneni."
"Yo kaine da girmanka zan tsaya sawa bulala? Me ye anfanin bindiga ta to? Ai saidai kaji alburushi tsakiyar zuciyarka."
Zaiyi magana Gambo da yaga abun ya k'i k'arewa ya figi wayarshi ya d'ora a kunne yace "Malam idan fad'an zaka masa ka kira shi da wayarka amma ba da kud'i na ba."
"Au Gambo ni zaka ma iskanci? To kud'in ne bana da ko wayar? Kayi sa'a bana gabanka da na fasa wayar, ba d..."
Bai barshi ya fad'a ba ya kashe wayar yana dariya. Dan yasan yana can yanzu yana mita da jaraba.
*Da yamma* fa tsaf ya shiga ya fad'a musu gidan nan zasu bari, Ummy ce ta kalleshi tace "...
*Alhamdulillah*
04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_77_
"Ammar da gaske kake tafiya zakayi? Amma kai tsaye haka?"
Cikin ladabi yace "To Ummy ni kuwa me zan zauna nayi? Ina d'aure fa a gidan nan kuke cin kaji kuna shan faro da exotic, to dan Allah me zan zauna na muku."
Hannunshi ta kama ta jashi zuwa d'akinta, saida ta zaunar dashi kan kujera sannan ta sake shi ta samu wuri ta zauna, kallonshi tayi sosai tace "Ammar ina fata dai rigimar nan ta kwanta ko?"
Da sauri ya kalleta yace "Ta kwanta Ummy? Haba haba haba, wannan magana ai bata taso ba, kamar fa a dake ka ne kuma a hanaka kuka, Ummy ko mutum na kashe a garin nan wallahi na fi k'arfin wulak'ancin da aka min, dan haka da yaron, da jami'an, da dokar, da wanda ya bayar da shawara aka k'irk'iri dokar, da wanda yayi rubutun dokar, da wanda yana nan aka aza dokar kai har da wanda ya aza dokar ma duk sai..."
Da sauri Ummy ta rufe mishi baki tana fad'in "Rufa mana asiri karka k'arasa fad'a, iyayenka ma zasu iya shiga ciki."
Jinjina kai yayi irin haba d'in nan, d'auke hannunta tayi ta mishi kallon fahimta tace "Ammar ka yarda ni mahaifiyarka ce?"
Jinjina kai yayi yace "Na yarda mana Ummy."
Kai tsaye ta d'ora da "Kuma ka yarda ina da girma da matsayin da zan iya sa ka ko hana ka?"
"Tabbas Ummy, kin isa har ma kin wuce."
Jinjina kai tayi alamar gamsuwa tace "In dai hakane to ina so maganar nan ta wuce, wucewa ta har abada Ammar, ka bawa al'amarin nan baya ka fuskanci rayuwarka ta gaba, 'ya'yanka da matarka ka rumgumesu ka watsar da duk wani shirme, idan har ka yarda zaka daina to ina so ka min alk'awarin da zai sani gamsuwa."
Da sauri ya rik'o hannunta yace "Wallahi Ummy na miki alk'awari har abada babu ni babu sake fad'a da wani ko tashin hankali, hasalima Ummy ko zagi ba zaki sake ji daga bakina ba, insha Allahu Ummy na miki wannan alk'awarin."
Da tsantsar farin ciki tace "Nagode sosai d'an albarka, Allah ya saka da alkairi, Allah ya maka albarka ya kareka daga sharrin masharranta."
Shima da jin dad'in addua'r ya amsa da "Ameen Ummy, ni ma nagode."
Mik'ewa tayi tana rik'e da hannunshi tace "Tashi kuje Allah ya tsare, Allah kad'e fitina a tsakaninku."
Haka suka fito suka tattara yaransu suka fita, ana yan koke koke da yan shak'e shak'e haka dai suka bar gidan da yammar nan kamar wanda aka kora.
Yanda Hamna taji ana fad'in gidan ga wanda suka je saida taje ta ga ba haka bane suna k'wauran fassarashi, ba k'arya fa Ammar yayi gini na kece raini na shiga tsara, babu ce kawai babu a cikin gidan amma hatta kayan d'aki saida ya mata sabi ya zuba, har kayan jiki kallonta kawai yake sanda take kwaso kayan jikinsu, bai hanata bane saboda tunanin tana buk'atarsu ne, amma shi babu abinda baiyi ba har yaran ma ya musu sabin kaya.
Savon gida sabuwar rayuwar ga sabon k'aramin ciki da take dashi had'e da sabbin mutane, nan suka fara rayuwarsu ta d'aukar bakin duniya da sababi, babu abinda ya rage na zamansu sai ma sababin salon shiririta da suka fito dasu.
Idan yaran na gidan kad'ai suke d'an d'aga k'afa suna rage wani abu, amma idan suka fita sai su koma yara sai abinda suka ga dama sukeyi babu mai k'wabarsu.
*Wata shida*
Yau ma ya gama shiryawa zai fita yara sun kwana wajen Ummy saboda weekend ne, tana zaune ta d'ora farantin kankana kan tulelen cikinta tana sha, ko kulata baiyi ba ya d'auki hanyar fita, baki bud'e ta kalleshi da mamakin yanda ya shareta zai fita tace "Toh! Su Ammar kuma ko magana babu shine zaka fita?"
Ba tare daya juyowa ba yace "Bani da lokacinki ne."
Ido ta zaro ta shiga kiciyar tashi tsaye rik'e da farantin tana fad'in "Wace yar iskar ce?"
Juyowa yayi ya kalleta, a hankali ya shiga takowa da wani irin kallo mai d'auke da salon mugunta, da sauri ta shiga ja baya ta fara zagaya kujerar tana fad'in "Allah karka matso nan Ammar, ka tsaya nan ka fad'a min wace shegiyar ce ta d'auki hankalinka har tasa kake jin baka da lokaci na."
Cikin dakiya yace "Zan zo ne nan saina fad'a miki yanda zaki fahimta."
Da sauri tace "Daga nan ma idan ka fad'a zan ji, fad'a min wacece ita?"
Da sauri ya d'ago k'afa da niyyar kamota hakan yasa ta juyawa zata zuba a guje d'aki, cikin d'aga murya yace "Hamna in kika tafi a guje da cikina ban yafe miki ba."
Da k'arfi ta juyo tana kallonshi tana ja baya da tsoron kar ya tardata, da k'arfi ya rik'o wuyan hannunta yana matsewa cikin k'eta yana fad'in "Ni na fad'a miki ina da yar iska ne a waje? Wai ke me yasa kishi ya miki yawa ne?"
Cikin zabga ihu kai kace idonta yake cirewa ta shiga fad'in "Ammar zaka karya min hannu, sake ni dan Allah sake ni, hannu na fa zai karye."
Saida ya zaunar da ita kan kujera yayi tsaye k'ik'am a kanta, ko da taga ya fara saita yatsunta tasan me zaiyi, zillewa ta fara yi tana kokawar k'watar hannunta tana fad'in "Na daina na daina, yi hak'uri ba zan sake ba, dan Allah yatsuna fa zasu karye."
Ai kuwa bai kulata ba ya shiga lank'wasa yatsunta yana tausasu suna k'ara da k'arfin tsiya ba tare da sun shirya ba ji kake k'was k'was k'wask'was, saida ya gama ya saketa ya sunkuya ya kama na k'afa, billi ta shiga yi da k'afafunta tana fad'in "Na tuba Ammar na tuna na tuba wallahi."
Saida ya gama tas ya mik'e ya gyara zaman rigarshi ya sunkuya ya sumbaci kumcinta yace "Je t'aime."
Juyawa yayi zai fita ita ma ta mik'e ta nufi d'aki, saida ta kai k'ofar d'akin shima ya kai k'ofar fitar tace "Duk yarinyar daka kalla ko ka bata hannu kuka gaisa ban yafe maka ba Ammar."
Lumshe ido yayi ya juyo kamar mai jin bacci ya kalleta, gwalo ta masa tace "Naje na fad'a ka zo mana."
Gyara tsayuwa yayi yace "Ni kuma yau in na fita sai nayi budurwa, kinsan dai ba zan zauna dake kad'ai ba haka kawai, kamar yanda nake canja abinci na haka ma ina buk'atar canja wurin hutuna, dan haka zan samo yar yarinya yar cakwai da zan iya d'auka ba tare da nayi nishi ba, ke kuma a lokacin zaki san girman da nake da shi."
Hamna da taji kamar ya soketa da mashi da sauri ta manta da wajen b'uya ne ta nufa ta fito ta nufe shi gadan gadan tana shiryin kuka tana fad'in "Ammar Ammar, zo dan Allah muyi magana, zo na baka hak'uri."
Juyawa yayi cike da jin wata isa da izza wai shima akwai wanda yake wahalarwa akan son shi ya nufi k'ofa, da sauri kamar zatayi gudu ta riskeshi yana shirin shiga gabjejiyar motarshi fara tas, rik'eshi tayi ta baya tana turo baki, juyowa yayi ya kalleta fuska a had'e yace "Ya dai malama? Sake ni sauri nake."
Ba tare data saki rigarshi ba taja ta har k'asa ta durk'usa gabanshi ba tare da jin nauyin cikinta ta marairaice tace "Ammar karka min kishiya ko ta waje ce dan Allah, ina sonka ba zan iya rabaka da kowace mace ba wallahi, dan Allah kayi hak'uri ka fad'a min duk abinda kake so da wanda baka so zan yi wallahi."
Saida yayi da gaske ya cije dariyar dake son taho mishi, kallonta yayi yana d'an basarwa yace "Kin tabbatar za kiyi komai nace miki?"
"Allah kuwa zanyi, na rantse maka."
Kamo hannunta yayi ta mik'e yana kallon fuskarta yace "Da fari ina so ki daina kirana Ammar gatsau babu sayawa, in baki manta nasha fad'a mikibana so, amma dana ga kin k'i dainawa saina zuba miki ido."
A hassale yace "Hak'uri? Ya bawa uban wa hak'uri? Lusari ne shi da zai bayar da hak'uri? To ni daya bayar da hak'urin ma da sai na d'aga mishi nono." 😂
Da sauri lieutenant yace "Sakarai ina kaga nonon to? Kenan ka d'aure mishi gindi ya ci gaba da d'aukar rigima."
"Yo sai me? Mu ba rigimar ce ta kawo mu duniya ba? Kaga malam karka k'ara mana irin haka, a irin wannan lamarin ba'a ma yaro haka, yanda yake da laifi shima waccen yaron da laifinshi, tunda waya aike shi kula masa matarshi sannan yasa aka ma d'an uwanshi duka, da kaima ka tsaya a wajen ka kare d'anka ka nuna musu ba bare bane shi ko marar gata, amma saboda Allah saika wulak'antashi a gaban mutane."
Cikin jin haushi yace "To ubana, yanzu yanda za ayi idan zaka dawo ka taho da bulala sai ka zaneni."
"Yo kaine da girmanka zan tsaya sawa bulala? Me ye anfanin bindiga ta to? Ai saidai kaji alburushi tsakiyar zuciyarka."
Zaiyi magana Gambo da yaga abun ya k'i k'arewa ya figi wayarshi ya d'ora a kunne yace "Malam idan fad'an zaka masa ka kira shi da wayarka amma ba da kud'i na ba."
"Au Gambo ni zaka ma iskanci? To kud'in ne bana da ko wayar? Kayi sa'a bana gabanka da na fasa wayar, ba d..."
Bai barshi ya fad'a ba ya kashe wayar yana dariya. Dan yasan yana can yanzu yana mita da jaraba.
*Da yamma* fa tsaf ya shiga ya fad'a musu gidan nan zasu bari, Ummy ce ta kalleshi tace "...
*Alhamdulillah*
04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_77_
"Ammar da gaske kake tafiya zakayi? Amma kai tsaye haka?"
Cikin ladabi yace "To Ummy ni kuwa me zan zauna nayi? Ina d'aure fa a gidan nan kuke cin kaji kuna shan faro da exotic, to dan Allah me zan zauna na muku."
Hannunshi ta kama ta jashi zuwa d'akinta, saida ta zaunar dashi kan kujera sannan ta sake shi ta samu wuri ta zauna, kallonshi tayi sosai tace "Ammar ina fata dai rigimar nan ta kwanta ko?"
Da sauri ya kalleta yace "Ta kwanta Ummy? Haba haba haba, wannan magana ai bata taso ba, kamar fa a dake ka ne kuma a hanaka kuka, Ummy ko mutum na kashe a garin nan wallahi na fi k'arfin wulak'ancin da aka min, dan haka da yaron, da jami'an, da dokar, da wanda ya bayar da shawara aka k'irk'iri dokar, da wanda yayi rubutun dokar, da wanda yana nan aka aza dokar kai har da wanda ya aza dokar ma duk sai..."
Da sauri Ummy ta rufe mishi baki tana fad'in "Rufa mana asiri karka k'arasa fad'a, iyayenka ma zasu iya shiga ciki."
Jinjina kai yayi irin haba d'in nan, d'auke hannunta tayi ta mishi kallon fahimta tace "Ammar ka yarda ni mahaifiyarka ce?"
Jinjina kai yayi yace "Na yarda mana Ummy."
Kai tsaye ta d'ora da "Kuma ka yarda ina da girma da matsayin da zan iya sa ka ko hana ka?"
"Tabbas Ummy, kin isa har ma kin wuce."
Jinjina kai tayi alamar gamsuwa tace "In dai hakane to ina so maganar nan ta wuce, wucewa ta har abada Ammar, ka bawa al'amarin nan baya ka fuskanci rayuwarka ta gaba, 'ya'yanka da matarka ka rumgumesu ka watsar da duk wani shirme, idan har ka yarda zaka daina to ina so ka min alk'awarin da zai sani gamsuwa."
Da sauri ya rik'o hannunta yace "Wallahi Ummy na miki alk'awari har abada babu ni babu sake fad'a da wani ko tashin hankali, hasalima Ummy ko zagi ba zaki sake ji daga bakina ba, insha Allahu Ummy na miki wannan alk'awarin."
Da tsantsar farin ciki tace "Nagode sosai d'an albarka, Allah ya saka da alkairi, Allah ya maka albarka ya kareka daga sharrin masharranta."
Shima da jin dad'in addua'r ya amsa da "Ameen Ummy, ni ma nagode."
Mik'ewa tayi tana rik'e da hannunshi tace "Tashi kuje Allah ya tsare, Allah kad'e fitina a tsakaninku."
Haka suka fito suka tattara yaransu suka fita, ana yan koke koke da yan shak'e shak'e haka dai suka bar gidan da yammar nan kamar wanda aka kora.
Yanda Hamna taji ana fad'in gidan ga wanda suka je saida taje ta ga ba haka bane suna k'wauran fassarashi, ba k'arya fa Ammar yayi gini na kece raini na shiga tsara, babu ce kawai babu a cikin gidan amma hatta kayan d'aki saida ya mata sabi ya zuba, har kayan jiki kallonta kawai yake sanda take kwaso kayan jikinsu, bai hanata bane saboda tunanin tana buk'atarsu ne, amma shi babu abinda baiyi ba har yaran ma ya musu sabin kaya.
Savon gida sabuwar rayuwar ga sabon k'aramin ciki da take dashi had'e da sabbin mutane, nan suka fara rayuwarsu ta d'aukar bakin duniya da sababi, babu abinda ya rage na zamansu sai ma sababin salon shiririta da suka fito dasu.
Idan yaran na gidan kad'ai suke d'an d'aga k'afa suna rage wani abu, amma idan suka fita sai su koma yara sai abinda suka ga dama sukeyi babu mai k'wabarsu.
*Wata shida*
Yau ma ya gama shiryawa zai fita yara sun kwana wajen Ummy saboda weekend ne, tana zaune ta d'ora farantin kankana kan tulelen cikinta tana sha, ko kulata baiyi ba ya d'auki hanyar fita, baki bud'e ta kalleshi da mamakin yanda ya shareta zai fita tace "Toh! Su Ammar kuma ko magana babu shine zaka fita?"
Ba tare daya juyowa ba yace "Bani da lokacinki ne."
Ido ta zaro ta shiga kiciyar tashi tsaye rik'e da farantin tana fad'in "Wace yar iskar ce?"
Juyowa yayi ya kalleta, a hankali ya shiga takowa da wani irin kallo mai d'auke da salon mugunta, da sauri ta shiga ja baya ta fara zagaya kujerar tana fad'in "Allah karka matso nan Ammar, ka tsaya nan ka fad'a min wace shegiyar ce ta d'auki hankalinka har tasa kake jin baka da lokaci na."
Cikin dakiya yace "Zan zo ne nan saina fad'a miki yanda zaki fahimta."
Da sauri tace "Daga nan ma idan ka fad'a zan ji, fad'a min wacece ita?"
Da sauri ya d'ago k'afa da niyyar kamota hakan yasa ta juyawa zata zuba a guje d'aki, cikin d'aga murya yace "Hamna in kika tafi a guje da cikina ban yafe miki ba."
Da k'arfi ta juyo tana kallonshi tana ja baya da tsoron kar ya tardata, da k'arfi ya rik'o wuyan hannunta yana matsewa cikin k'eta yana fad'in "Ni na fad'a miki ina da yar iska ne a waje? Wai ke me yasa kishi ya miki yawa ne?"
Cikin zabga ihu kai kace idonta yake cirewa ta shiga fad'in "Ammar zaka karya min hannu, sake ni dan Allah sake ni, hannu na fa zai karye."
Saida ya zaunar da ita kan kujera yayi tsaye k'ik'am a kanta, ko da taga ya fara saita yatsunta tasan me zaiyi, zillewa ta fara yi tana kokawar k'watar hannunta tana fad'in "Na daina na daina, yi hak'uri ba zan sake ba, dan Allah yatsuna fa zasu karye."
Ai kuwa bai kulata ba ya shiga lank'wasa yatsunta yana tausasu suna k'ara da k'arfin tsiya ba tare da sun shirya ba ji kake k'was k'was k'wask'was, saida ya gama ya saketa ya sunkuya ya kama na k'afa, billi ta shiga yi da k'afafunta tana fad'in "Na tuba Ammar na tuna na tuba wallahi."
Saida ya gama tas ya mik'e ya gyara zaman rigarshi ya sunkuya ya sumbaci kumcinta yace "Je t'aime."
Juyawa yayi zai fita ita ma ta mik'e ta nufi d'aki, saida ta kai k'ofar d'akin shima ya kai k'ofar fitar tace "Duk yarinyar daka kalla ko ka bata hannu kuka gaisa ban yafe maka ba Ammar."
Lumshe ido yayi ya juyo kamar mai jin bacci ya kalleta, gwalo ta masa tace "Naje na fad'a ka zo mana."
Gyara tsayuwa yayi yace "Ni kuma yau in na fita sai nayi budurwa, kinsan dai ba zan zauna dake kad'ai ba haka kawai, kamar yanda nake canja abinci na haka ma ina buk'atar canja wurin hutuna, dan haka zan samo yar yarinya yar cakwai da zan iya d'auka ba tare da nayi nishi ba, ke kuma a lokacin zaki san girman da nake da shi."
Hamna da taji kamar ya soketa da mashi da sauri ta manta da wajen b'uya ne ta nufa ta fito ta nufe shi gadan gadan tana shiryin kuka tana fad'in "Ammar Ammar, zo dan Allah muyi magana, zo na baka hak'uri."
Juyawa yayi cike da jin wata isa da izza wai shima akwai wanda yake wahalarwa akan son shi ya nufi k'ofa, da sauri kamar zatayi gudu ta riskeshi yana shirin shiga gabjejiyar motarshi fara tas, rik'eshi tayi ta baya tana turo baki, juyowa yayi ya kalleta fuska a had'e yace "Ya dai malama? Sake ni sauri nake."
Ba tare data saki rigarshi ba taja ta har k'asa ta durk'usa gabanshi ba tare da jin nauyin cikinta ta marairaice tace "Ammar karka min kishiya ko ta waje ce dan Allah, ina sonka ba zan iya rabaka da kowace mace ba wallahi, dan Allah kayi hak'uri ka fad'a min duk abinda kake so da wanda baka so zan yi wallahi."
Saida yayi da gaske ya cije dariyar dake son taho mishi, kallonta yayi yana d'an basarwa yace "Kin tabbatar za kiyi komai nace miki?"
"Allah kuwa zanyi, na rantse maka."
Kamo hannunta yayi ta mik'e yana kallon fuskarta yace "Da fari ina so ki daina kirana Ammar gatsau babu sayawa, in baki manta nasha fad'a mikibana so, amma dana ga kin k'i dainawa saina zuba miki ido."