Sashe 133
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sallamarsu tasa wanda ke falon suka kallesu, yan biyu ne dai gasu amma duk sun canza, Hamna ta k'ara haske kan wanda take da a farko, jikin nan nata duk da tana shan wahala a wurin Aissata amma ya kwanta luf dashi, Amna kuma ta k'ara duhu sai kuma cikin yasa tayi muni ba kamar kafin ta d'auki cikin ba tsaf da ita, ana gaisawa ana mamakin tahowarta katsam haka babu sanarwa, Ummy na d'aki take jin kamar maganarta, tana lek'owa ta ga dai ita ce da gaske, saida suka gaisa da kowa sannan ta wuce d'akin Hajia dan tun sallah la'asar bata fito ba jikin ya d'an k'ara nauyi sosai bata san dai nunawa ne, kamar mai sand'a ta shiga tana sallama har ta zaune kusanta a k'asa ba tare data yarda sun had'a ido ba, bata amsa sallamarta ba bare gaisuwarta tana mamakin dawowarta bada izininta ba.
Cikin wani irin amon murya tace "Meya dawo dake? Waya baki izinin dawowa ba tare dana amince ba? Ke ce kika zab'i dawowa ko kuma shi Gambon ne yace ki dawo?"
Cikin sanyin murya tace "Gaskiya Hajia basu san da fitowa ta ba, kawai na gaji da zaman can ne saboda tanti Aissata ta mayar dani kamar wata baiwarta, kuma Abba ma har Allah ya isa ya min idan na b'ata mata rai, jiya ma mun samu sab'ani ne shiyasa na tahowa ta dan nasan Abba na iya dukana idan ta fad'a masa na mata rashin kunya."
Kallonta Hajia tayi ta mik'e tsaye cikin b'acin rai ta gaura mata mari a fuska, dafe kunci tayi da sauri ta k'ara sunkuyar da kai, cikin masifa tace "Hamna kinsan dalilin da yasa na turaki can? To saboda ina so nasan abinda ke faruwa acan d'in ne, ina so naga abinda yasa bata so kowa ya rab'eshi sai ita kad'ai, amma da yake mahaukaciya ce ke shine kika dawo min haka ko? To tashi ki bani wuri, ni kuma zanje da kaina nayi aikin dan ba zan haifi d'a a cikina ba kuma wata ta fini cin moriyarshi ba."
Fita tayi ita kuma ta shiga masifa tana fad'a, tana fita d'akin Ummy ta shiga, tana ganinta bata tsaya komai ba tace "Hamna meya dawo dake? Ya akayi kika zo baki sanar min ba?"
Marairaicewa tayi tace "Ummy wallahi Tanti Aissata ta addabeni, kawai ta b'ata min rai ne jiya shiyasa na baro mata gidan."
"Amma me Hajia tace miki da kika taho ba da umarninta ba?"
Tab'e baki tayi tace "Tana can tana masifa mana, wai zata je da kanta Niamey d'in ta ga wace irin rayuwa suke, wallahi da za taji tawa da sai nace karta tafi, dan matar nan da gangan ma zata iya d'ora mata hawan jini."
Murmushi tayi tace "Hamna ince dai ba yaron nan yasa kika dawo ba ko?"
"A'a Ummy, kawai na dawo ne." Ta fad'a idonta akan Shureim dake bacci, fitowa tayi ta d'auki jakarta ta kai d'akinsu, saida tayi sallah magriba tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar kanti da d'an kwalinta sannan ta fito, Farisa tasa ta gyara mata d'akinta ita kuma ta sauko k'asa, saida ta shiga ta ga Zeituna da Fatima masha Allah yarinyar kamar ka fizge a hannunta ga uban gashi, suna gaisawa ta fito ta nufi wajensu Umaimah.
Mamaki ne ya kusa kasheta data shiga d'akin, yarinya 'yar k'walisa uwar kwalliya da tsabta, amma wai ita ce zaune k'asa da d'aurin k'irji tana cin 'ya'yan tsamiya tana tofar da yawu, kan nan nata yayi daud'a ya tsufa abun ba kyan gani, daga tsaye take k'are mata kallo tana mamaki, tafin k'afarta abinka ga farar fara yayi duhu, a take a wurin taji Umaimah ta fita a ranta, dan duk yanda kake ji dai zaka daure ka gyara jikinka tunda har kana iya cin abu kuma kana taka k'asa, ko baka gyara dan komai ba ka gyara dan kar namiji ya ga makusarka. Daga nan tsaye suka gaisa ta wuce b'angaren yer uwarta, ba wai son kai ba ko dan tana yer uwarta, amma tana dosa b'angaren ma k'amshin turaren tsintsiya ne ya mata maraba.
Tana shiga ita ma zaune take k'asa ta mik'e k'afafu da suka kumbura sumtum, cikinta yafi na Umaimah girma nesa ba kusa ba, cikin nutsuwa take cin bredinta mai yanka nan tana shafeshi da la vache qui rit, zaune tayi ta fizge bredin tana fad'in "Sakarya kawai, kina da ciki kina ta fama da abubuwan da zasu bud'a miki yaronki a cikin cikin, ki zo kisha wahala kafin ki haihu."
Hannu ta tara mata tace "Taimaka ban wannan na k'arasa to."
"An k'i." Ta fad'a tana d'auke d'an kwalin ta aje bayanta ta kalleta tace "Jamila wace asibiti take?"
Cike da shak'iyanci ta wani murgud'a mata baki tace "Asibitin mijina mana."
Sai kawai taji gabanta ya fad'i daga anbaton mijinta, da mamaki ta kalleta tace "Anya kuwa Amna bai koya miki iskanci ba, ke ma fa kin lalace yanzu."
"A'a ni bai koya min ba, kawai dai abun ne kamar a karatu, yana biya min ni kuma na hardace shi a kaina."
Tab'e baki tayi tace "Lallai mai miji." Amna ce tace "Yer uwa dama ina so ki zo, akwai matsala fa..."
Duk da ta kai k'arshen abinda take son fad'a amma saida ta juya ta kalli k'ofar da taji sallamarshi. Yana shigowa ya tsaya kamar wanda aka dakatar dashi, idonshi cikin nata wacce k'afafunta ke tank'washe tana jujjuya wayarta dake hannunta, *sanyin idaniya*, yau ne ya tabbatar da kalmar sanyin idaniya da ake fad'a, domin kuwa sanyin nan bai tsaya iya idonsa ba saida ya zarce har k'ark'ashin zuciyarsa ya isar da sak'on cewa wata mai matuk'ar mahimmanci ta iso wacce akayi kewarta na wani lokaci, dawowa yayi hayyacinshi ya fara takowa yana sauke jakarshi daga kafad'a ya kalli Amna yana fad'in "Duniyata bak'uwa kikayi?"
Kallon Hamna tayi tana dariya tare da bata gefen fumcinta da taga ya nufota tasan me zaiyi, sumbatarta yayi tana cewa "Sannu da zuwa, ya aiki, kayi hak'uri nayi nauyi ba zan iya tashi tarbanka ba."
Jakar ya aje kan kujera ya zauna daf da Amna yana rik'ota jikinshi yace "Je sais ma chérie, ya kika wuni?"
Cikin shagwab'a tace "Lafiya lau, kai fa?"
Hamna ya kalla wacce a taswirar zaman nasu suna kusan juna ne dukansu inda shi da ita suke fuskantar juna Amna ce kawai ta shiga tsakaninsu, yana kallon ita kuma tana dalla masa harara, wani bala'in haushinshi taji saika mata yake, yanda har taji ya fara tasiri wajen jin haushin yer uwarta ma data biye masa, akan me zasu raina mata wayo haka? Dan ita bata da auren ko me? D'auke idonta tayi daga kansu sai Ammar ne da yace "Ke baki iya gaishe da mutane ba?"
"Eh." Shine ta fad'a tana juya baki kamar zata tsinka shi, d'agowa yayi daga kishingid'en da yayi yana fad'in "Ke kankana ni? Ni kike ce ma eh?"
Da sauri taja baya tana fad'in "An fad'a d'in, kaga malam karka takura min fa, na fad'a maka ka daina shiga harkata, ba wajenka na zo ba ni wajen yer uwata na zo."
Jujjuyawa ya farayi alamar yana neman abunda zai jefa mata, da sauri ta tashi tsaye ta zagaya bayan kujera ta tsaya tana hararanshi, tsayawa yayi daga neman abun ya k'ura mata ido, a ranshi yace "Shegiya har tayi shirin gudu, ass kawai take jira."
Mamakin k'ibar da yaga ta k'ara yake yi, saida ya k'ara kallo da kyau yace "Ke kankana, murguzawa, yaushe kika mulmuje haka? Me tonton ya dinga baki acan kika koma haka?"
Cikin jin haushi tace "Tubarkallah maye ka ci kanka, ina ruwanka da k'ibata inba sa ido ba, to kurwata tafi k'arfinka maye kawai."
Zunbur ya mik'e ya nufeta, tana ganin haka ta tattare rigar bi ta bayan kujerar shi kuma tsalle yayi ya dira bayan kujerar da niyyar tarbanta, cikin sa'a ta zille ta fita da gudu tana fad'in "Jarababbe kawai ka shafa min lafiya mana in kana da zuciya."
Tsaye yayi ya dafe k'ugu da hannu d'aya yana binta da murmushi, wani dad'i yaji na ziyartarshi saboda yayi abinda ya jima baiyi ba, juyowa yayi kan Amna dake binsu da dariya kawai tana kallo, ita kanta tayi kewar wani abu data jima ba tayi ba, kallon dramarsu ba, dawowa yayi ya zauna yana sauke numfashi alamar gajiya.
*01:39* ta farka saboda jin kukan Shureim, tasowa tayi daga kan gadon sanye da gajerar rigar bacci, a hankali ta bud'a d'akin ta lek'o tana hangen d'akinsu Ummy, akan abun matakala ta tangale hannu d'aya ta buga tagumi, sannu sannu wani tausayin yaron taji yana shigarta, *uwa* bata tare dashi, *uba* ma haka baisan dashi ba, ta jima tsaye tana tunani da taji yayi shiru kuma ta sake jin kukanshi, kafin daga bisani ta koma d'aki ta kwanta tana jin sautin har yau.
Tunda ta dawo hayyacinta abun ya tsaya mata a rai, Huda 'yar shi ce dama, lallai ita kam kam ta gama auren Jibril kenan har abada, daga gadon asibitin nan gidansu zata wuce wajen iyayenta, kuma tayi niyya ko kasheta Hajia zatayi ba zata zauna dashi ba, bare ma tasan yanda Hajia bata k'aunarsu ba zata matsa mata ba, tana wannan tunanin ya shigo d'akin da sallama tare da wasu abokanshi su biyu, su Soueiba da Zeinabu suka amsa suka gaisa sosai, zaune yayi bakin gadon yana kallonta ita ma zaune take k'afafu mik'e sai rigarta data d'an d'age kad'an, cikin kulawa yace "Ya jikin naki?"
Kallon da take masa yasa ya fara tsarguwa da shi, saida tayi niyya sannan tace "Jiki ba sauk'i."
Kowa na d'akin kallonta sukayi inda Zeinabu tace "Jamila ba'a cewa haka, da sauk'i ake cewa duk tsananin da ake ji, ko kuma kice angode Allah."
Kallonta tayi a harzuk'e ta nuna shi da yatsa ta d'ago daga zaman da tayi tace "Bayan duk abinda ya min ne zai wani tambayeni ya jikina? Jibril akan me zaka k'i fad'a min gaskiya? Kana ji kana gani 'yar iskar nan ta dinga min buru-uba a cikin gida tana nuna min ta ma fini saninka, ashe gaskiya ta fad'a nice mahaukaciya da..."
Cikin wani irin amon murya tace "Meya dawo dake? Waya baki izinin dawowa ba tare dana amince ba? Ke ce kika zab'i dawowa ko kuma shi Gambon ne yace ki dawo?"
Cikin sanyin murya tace "Gaskiya Hajia basu san da fitowa ta ba, kawai na gaji da zaman can ne saboda tanti Aissata ta mayar dani kamar wata baiwarta, kuma Abba ma har Allah ya isa ya min idan na b'ata mata rai, jiya ma mun samu sab'ani ne shiyasa na tahowa ta dan nasan Abba na iya dukana idan ta fad'a masa na mata rashin kunya."
Kallonta Hajia tayi ta mik'e tsaye cikin b'acin rai ta gaura mata mari a fuska, dafe kunci tayi da sauri ta k'ara sunkuyar da kai, cikin masifa tace "Hamna kinsan dalilin da yasa na turaki can? To saboda ina so nasan abinda ke faruwa acan d'in ne, ina so naga abinda yasa bata so kowa ya rab'eshi sai ita kad'ai, amma da yake mahaukaciya ce ke shine kika dawo min haka ko? To tashi ki bani wuri, ni kuma zanje da kaina nayi aikin dan ba zan haifi d'a a cikina ba kuma wata ta fini cin moriyarshi ba."
Fita tayi ita kuma ta shiga masifa tana fad'a, tana fita d'akin Ummy ta shiga, tana ganinta bata tsaya komai ba tace "Hamna meya dawo dake? Ya akayi kika zo baki sanar min ba?"
Marairaicewa tayi tace "Ummy wallahi Tanti Aissata ta addabeni, kawai ta b'ata min rai ne jiya shiyasa na baro mata gidan."
"Amma me Hajia tace miki da kika taho ba da umarninta ba?"
Tab'e baki tayi tace "Tana can tana masifa mana, wai zata je da kanta Niamey d'in ta ga wace irin rayuwa suke, wallahi da za taji tawa da sai nace karta tafi, dan matar nan da gangan ma zata iya d'ora mata hawan jini."
Murmushi tayi tace "Hamna ince dai ba yaron nan yasa kika dawo ba ko?"
"A'a Ummy, kawai na dawo ne." Ta fad'a idonta akan Shureim dake bacci, fitowa tayi ta d'auki jakarta ta kai d'akinsu, saida tayi sallah magriba tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar kanti da d'an kwalinta sannan ta fito, Farisa tasa ta gyara mata d'akinta ita kuma ta sauko k'asa, saida ta shiga ta ga Zeituna da Fatima masha Allah yarinyar kamar ka fizge a hannunta ga uban gashi, suna gaisawa ta fito ta nufi wajensu Umaimah.
Mamaki ne ya kusa kasheta data shiga d'akin, yarinya 'yar k'walisa uwar kwalliya da tsabta, amma wai ita ce zaune k'asa da d'aurin k'irji tana cin 'ya'yan tsamiya tana tofar da yawu, kan nan nata yayi daud'a ya tsufa abun ba kyan gani, daga tsaye take k'are mata kallo tana mamaki, tafin k'afarta abinka ga farar fara yayi duhu, a take a wurin taji Umaimah ta fita a ranta, dan duk yanda kake ji dai zaka daure ka gyara jikinka tunda har kana iya cin abu kuma kana taka k'asa, ko baka gyara dan komai ba ka gyara dan kar namiji ya ga makusarka. Daga nan tsaye suka gaisa ta wuce b'angaren yer uwarta, ba wai son kai ba ko dan tana yer uwarta, amma tana dosa b'angaren ma k'amshin turaren tsintsiya ne ya mata maraba.
Tana shiga ita ma zaune take k'asa ta mik'e k'afafu da suka kumbura sumtum, cikinta yafi na Umaimah girma nesa ba kusa ba, cikin nutsuwa take cin bredinta mai yanka nan tana shafeshi da la vache qui rit, zaune tayi ta fizge bredin tana fad'in "Sakarya kawai, kina da ciki kina ta fama da abubuwan da zasu bud'a miki yaronki a cikin cikin, ki zo kisha wahala kafin ki haihu."
Hannu ta tara mata tace "Taimaka ban wannan na k'arasa to."
"An k'i." Ta fad'a tana d'auke d'an kwalin ta aje bayanta ta kalleta tace "Jamila wace asibiti take?"
Cike da shak'iyanci ta wani murgud'a mata baki tace "Asibitin mijina mana."
Sai kawai taji gabanta ya fad'i daga anbaton mijinta, da mamaki ta kalleta tace "Anya kuwa Amna bai koya miki iskanci ba, ke ma fa kin lalace yanzu."
"A'a ni bai koya min ba, kawai dai abun ne kamar a karatu, yana biya min ni kuma na hardace shi a kaina."
Tab'e baki tayi tace "Lallai mai miji." Amna ce tace "Yer uwa dama ina so ki zo, akwai matsala fa..."
Duk da ta kai k'arshen abinda take son fad'a amma saida ta juya ta kalli k'ofar da taji sallamarshi. Yana shigowa ya tsaya kamar wanda aka dakatar dashi, idonshi cikin nata wacce k'afafunta ke tank'washe tana jujjuya wayarta dake hannunta, *sanyin idaniya*, yau ne ya tabbatar da kalmar sanyin idaniya da ake fad'a, domin kuwa sanyin nan bai tsaya iya idonsa ba saida ya zarce har k'ark'ashin zuciyarsa ya isar da sak'on cewa wata mai matuk'ar mahimmanci ta iso wacce akayi kewarta na wani lokaci, dawowa yayi hayyacinshi ya fara takowa yana sauke jakarshi daga kafad'a ya kalli Amna yana fad'in "Duniyata bak'uwa kikayi?"
Kallon Hamna tayi tana dariya tare da bata gefen fumcinta da taga ya nufota tasan me zaiyi, sumbatarta yayi tana cewa "Sannu da zuwa, ya aiki, kayi hak'uri nayi nauyi ba zan iya tashi tarbanka ba."
Jakar ya aje kan kujera ya zauna daf da Amna yana rik'ota jikinshi yace "Je sais ma chérie, ya kika wuni?"
Cikin shagwab'a tace "Lafiya lau, kai fa?"
Hamna ya kalla wacce a taswirar zaman nasu suna kusan juna ne dukansu inda shi da ita suke fuskantar juna Amna ce kawai ta shiga tsakaninsu, yana kallon ita kuma tana dalla masa harara, wani bala'in haushinshi taji saika mata yake, yanda har taji ya fara tasiri wajen jin haushin yer uwarta ma data biye masa, akan me zasu raina mata wayo haka? Dan ita bata da auren ko me? D'auke idonta tayi daga kansu sai Ammar ne da yace "Ke baki iya gaishe da mutane ba?"
"Eh." Shine ta fad'a tana juya baki kamar zata tsinka shi, d'agowa yayi daga kishingid'en da yayi yana fad'in "Ke kankana ni? Ni kike ce ma eh?"
Da sauri taja baya tana fad'in "An fad'a d'in, kaga malam karka takura min fa, na fad'a maka ka daina shiga harkata, ba wajenka na zo ba ni wajen yer uwata na zo."
Jujjuyawa ya farayi alamar yana neman abunda zai jefa mata, da sauri ta tashi tsaye ta zagaya bayan kujera ta tsaya tana hararanshi, tsayawa yayi daga neman abun ya k'ura mata ido, a ranshi yace "Shegiya har tayi shirin gudu, ass kawai take jira."
Mamakin k'ibar da yaga ta k'ara yake yi, saida ya k'ara kallo da kyau yace "Ke kankana, murguzawa, yaushe kika mulmuje haka? Me tonton ya dinga baki acan kika koma haka?"
Cikin jin haushi tace "Tubarkallah maye ka ci kanka, ina ruwanka da k'ibata inba sa ido ba, to kurwata tafi k'arfinka maye kawai."
Zunbur ya mik'e ya nufeta, tana ganin haka ta tattare rigar bi ta bayan kujerar shi kuma tsalle yayi ya dira bayan kujerar da niyyar tarbanta, cikin sa'a ta zille ta fita da gudu tana fad'in "Jarababbe kawai ka shafa min lafiya mana in kana da zuciya."
Tsaye yayi ya dafe k'ugu da hannu d'aya yana binta da murmushi, wani dad'i yaji na ziyartarshi saboda yayi abinda ya jima baiyi ba, juyowa yayi kan Amna dake binsu da dariya kawai tana kallo, ita kanta tayi kewar wani abu data jima ba tayi ba, kallon dramarsu ba, dawowa yayi ya zauna yana sauke numfashi alamar gajiya.
*01:39* ta farka saboda jin kukan Shureim, tasowa tayi daga kan gadon sanye da gajerar rigar bacci, a hankali ta bud'a d'akin ta lek'o tana hangen d'akinsu Ummy, akan abun matakala ta tangale hannu d'aya ta buga tagumi, sannu sannu wani tausayin yaron taji yana shigarta, *uwa* bata tare dashi, *uba* ma haka baisan dashi ba, ta jima tsaye tana tunani da taji yayi shiru kuma ta sake jin kukanshi, kafin daga bisani ta koma d'aki ta kwanta tana jin sautin har yau.
Tunda ta dawo hayyacinta abun ya tsaya mata a rai, Huda 'yar shi ce dama, lallai ita kam kam ta gama auren Jibril kenan har abada, daga gadon asibitin nan gidansu zata wuce wajen iyayenta, kuma tayi niyya ko kasheta Hajia zatayi ba zata zauna dashi ba, bare ma tasan yanda Hajia bata k'aunarsu ba zata matsa mata ba, tana wannan tunanin ya shigo d'akin da sallama tare da wasu abokanshi su biyu, su Soueiba da Zeinabu suka amsa suka gaisa sosai, zaune yayi bakin gadon yana kallonta ita ma zaune take k'afafu mik'e sai rigarta data d'an d'age kad'an, cikin kulawa yace "Ya jikin naki?"
Kallon da take masa yasa ya fara tsarguwa da shi, saida tayi niyya sannan tace "Jiki ba sauk'i."
Kowa na d'akin kallonta sukayi inda Zeinabu tace "Jamila ba'a cewa haka, da sauk'i ake cewa duk tsananin da ake ji, ko kuma kice angode Allah."
Kallonta tayi a harzuk'e ta nuna shi da yatsa ta d'ago daga zaman da tayi tace "Bayan duk abinda ya min ne zai wani tambayeni ya jikina? Jibril akan me zaka k'i fad'a min gaskiya? Kana ji kana gani 'yar iskar nan ta dinga min buru-uba a cikin gida tana nuna min ta ma fini saninka, ashe gaskiya ta fad'a nice mahaukaciya da..."