Sashe 12
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A motar Junaid suka d'auki hanya ba ko waiwaiye saboda su isa da wuri, Ammar ma wani d'aki suka shiga wanda ya ware yake zuba duk wasu kaya da suka shafi na jinya, sannan har magunguna ke akwai da kayan aiki masu mahimmanci wanda babu su a ma k'asar baki d'aya, hakan yasa baya wasa wajen kula da su, zaune Amar yayi kan gado Ammar yasa k'aramin almakashi da k'ada da yan ruwan kashe ciwo yana goge masa, babu mai kallon idon wani bare magana, saida ya gama ya duba inda ke buk'atar a rufe yasa k'aramin bandeji ya rufe mishi, ba tare daya kalleshi a yace "Kana jin jiri?"
Saida ya d'an dafe kai yace "Eh, dan da k'yar ma na kawo kaina nan, na so na ce ka goye ni amma kuma..."
Kallonshi yayi yace "Amma kuma me?"
"Kana hushi da k'aninka, d'an uwanka, shak'ik'inka, sannan abokin rayuwarka." Duk yayi maganar ne cikin marairaicewa, k'ala bai ce masa ba sai ma wasu kwalaye dayake fito da su yana son d'auko wani magani, ya sha wahala kafin ya d'auko ya bud'e ya d'auki wanda yake buk'ata ya mayar da sauran, fitowa yayi daga d'akin jim kad'an ya dawo, ruwa ya bashi a roba tare da maganin yasha, d'aya maganin kuma ya sa a cikin kofi da ruwa, saida ya gama tafasa ya mik'a mishi ya shanye ya aje kofin, ba tare daya kalli fuskarshi ba yace "Ka kwanta kan gadon nan."
Ganin ya juya zai fita yasa Amar cewa "Har zuwa wane lokaci?"
Ba tare daya juyo ba yace "Har a busa k'aho."
Murmushi kawai Amar yayi shi kuma ya fice, yana fita kuma motar shi ya fad'a ya tayar, mai gadi na bud'e k'ofa ya suri motar yayi waje, hanya ya d'auka shima kamar zai tashi sama, shi ma dai kamar su Junaid hanyar gidan roumji ya nufa, sai dai duk gudunshi bai iya riskar su Junaid ba dan sun rigashi d'aukar hanya kuma suma gudu suke sosai.
*K'arfe* 06:20 na yamma Amar ya fito cikin shiri ya samu Ummy ya mata sallama yace zai tafi shima k'auye saboda kar ran Abba ya b'ace, cike da damuwa tace "Amar kayi hak'uri mana zuwa gobe sai mu tafi tare, tunda kaga ba lafiya ne da kai ba."
Dariyar gefen labb'a yayi yace "Haba Ummy lafiya ta lau fa, ki bari naje kawai kar Abba ya ga kamar bamu ji maganar sa bane, kuma kinga dukansu fa ina kyautata zaton can suka tafi, kinga gwara nima na hanzarta na tafi ko da ana sallah magriba ne saina isa."
Cikin sanyi tace "Shikenan Amar, Allah ya tsare ka ya kare gabanka da bayanka."
Murmushi yayi sosai yace "Ameen Ummy, sai mun dawo."
"A dawo lafiya." Ta fad'a tana binshi da kallo harya fita.
Yana fita su Hamna na shigowa da motonsu dan saida suka kai d'inki sannan suka dawo gida, haka ma ba jimawa Umaima ta shigo gidan tare da drebanta, sai Jamila da ta shigo gaf da magrib daga école.
*Gidan roumji*
Rana ta fad'i sosai su Junaid suka iso, tunda suka fito daga mota lieutenant da colonel ke kallonsu da mamaki, k'arasowa sukayi cikin mutane suka gaishesu da girmamawa tare da musu ta'aziya, sun shiga cikin gidan dan yiwa na cikin gida suma sai ga motar boss ta karyo kwana, da k'arfi ya ci burki ya kashe motar ya fito makulli da waya a hanu, ga kyau ga kyan tsari da hallita sai dai a wurina babu kyan hali, da k'akk'arfar tafiyar nan tashi ya k'araso yana sallama amma fa wanda yayi sa'a ne kad'ai ke ya ji sallamar dan kamar bai so yayi ba, saida yayi zaune ya tank'washe k'afafun shi kafin ya fara bawa na kusa da shi hannu, colonel kam daya tsura mishi ido a ranshi cewa yayi "Lallai yaro na, wannan da ace kai général ne na soja da anshiga uku, ko mu dake iyayanka dai saida muka gaishe da mutane kafin muka zauna saboda wurin mutuwa ne, amma kai sai bayan ka zauna kake gaishe da wanda ke kusa da kai, humm."
Lieutenant kuma haushin Ammar ne d'in ya kusa kashe shi shiyasa ma ya d'auke kallonshi daga kan Ammar d'in dan kar zuciya ta kwashe shi ya mareshi, yana gama tashi ta'aziyar ya fara danna waya, da sauri Labaran ya kalleshi yace "Ammar ka shiga ciki mana ku gaisa da matan."
Kallonshi yayi lokaci d'aya kuma ya mayar da kallonshi kan wayar, yana kallon wayar tashi ya mik'e yasa takalminshi ya nufi cikin gidan a ranshi yana fad'in "Yanzu mutum na shiga zasu saka maka ido suna kallo, kowace burinta ka mata magana ta ji dad'i, mtssss, shiyasa na tsani shiga irin taron nan."
*Ikon Allah sai kallo, to Ammar me ka d'auki matan? Sai kace wasu tsofaffin...*😏
Yana kallonsu su Junaid suma suna kallonshi haka kowa ya gama ya fito, suna zuwa kuma wasu har sun nufi masallaci wasu kuma na alwala, suma alwala sukayi suka nufi masallacin, tare sukayi sallah suka fito, fitowar lieutenant da colonel yayi daidai da shigowar Amar cikin kwanar, lieutenant a ranshi yace "Wato yaran nan sun raina mutane ko? Amma laifin duk na waccen babban kwabon ne."
Tsaye yayi hakan yasa colonel ma tsayawa, su Junaid da Ammar na fitowa lieutenant yace su zo, Amar na ganinsu saboda ya hasko fitilar motarshi ya tsaya wajensu ya fito, cikin girmamawa yace "Abba ina wuninku, har kunyi sallah ko? Bara nima na yi alwala."
Zai wuce lieutenant ya dawo da shi baya ya kallesu dukansu yace "Wato da na ce ku taho gaba d'aya shine kowa yayi gaban kanshi, yanzu ribar me kuka ci da kuka nunawa mutane ku kanku ba had'e yake ba?"
Shiru sukayi dukansu suna kallon k'asa sai boss da idonshi ke kan wayarshi yana latsawa ya rumgume hannu d'aya, juyawa lieutenant yayi ya kalli Ammar d'in da ya ga ya mayar dashi wani d'an iska ma, wani haushi ne ya kashe shi sai kawai yasa tafin hannu ya bangaji k'eyar Ammar, bai ankara ba yaji bugun dan haka ya juyo ya kalli mahaifin nashi, had'e fuska yayi ba alamar wasa yace "Abba meye haka? Kai baka san cewa kai shine mutum ba? Duk wani abu mai mahimmanci a cikin k'wak'walwa yake, so kake kasa na rasa komai nawa?"
Hannu ya d'aga da nufin sake mazgeshi colonel yayi saurin rik'e hannunshi yace "Ba kamata yayi ace ka fara tambayar meya faru ba kafin duk wannan b'acin ran, ko baka kula da fuskar Amar bane, sannan ka dubi Junaid ma, baka tunanin ko wani abu ya samesu a hanyar?"
Fizge hannunshi yayi yana kallon Ammar yayi k'wafa kafin ya kallesu yace "To naji, wa zai fad'a mana meya faru?"
Shiru sukayi sai wuk'i-wuk'i da ido da sukeyi, Labaran ne ya kalli Jamil yace "Kai ba tambayarku ake ba kuka mana shiru?"
Jamil kam kallon Ammar yayi wanda ya ga ya kalleshi, idonshi kad'ai suka fassara mishi manufar kallonshi, dan haka ya ja baki yayi gum saboda tsoro, sai dai ya manta gaba da gabanta, colonel ne cikin tsawa yace " Wai ya ana muku magana kuka mana shiru? Shin ku yan mata ne bare ku d'auka son ku muke."
Wani kallo Ammar ya mishi yace "Idan ma yan mata ne mu sai mu tsaya muna sauraron tsofaffi irinku."
Labaran kam bushewa yayi da dariya inda lieutenant ya zabura zai bugeshi Labaran d'in ya rik'e shi, cikin dariyarshi yace "To ai gaskiya ya fad'a, tsofaffin ne mu mana."
Kamar daga sama suka ji saukar mari ji kake "Tauuuuuu."
Da sauri Junaid ya dafe kunci saboda wani mahaukacin mari da colonel ya watsa mishi yana fad'in "Iskanci kai, ana muku magana zaku d'auke mu wasu shashashu."
Lieutenant ne yace "Meye haka saboda Allah? Yanzu shine kenan yayi laifi a wurin nan? Me ya sa ba zaka mari wannan ba dake kusa da kai yana mana shak'iyanci sai wannan? Saboda a ganinka wannan ne ka haifa su kuma wad'annan duk 'ya'yan yan uwanka ne, mtsss."
Lieutenant Jamil ya kalla ya zaro ido yace "Yanzu zaku fad'a mana meya faru da har yasa ku ka k'i bin umarnin dana baku na a taho tare?"
Cikin rawar murya Jamil yace " Dama da zamu..."
Karaf Amar ya karb'a da cewa "Ni ne fa na samu had'ari akan moton wani abokina, shine da na zo gida sai aka ce su Junaid su taho saboda Ammar shi ya duba min ciwon, bayan Ummy ta zo gida kuma sai shima suka ce ya taho, ni kuma ganin duk sun taho yasa na kasa hak'ura na taho."
Colonel ne ya kalli Junaid yace "To kai kuma uban wa ya ci uwaka a bakin na ka?"
Bawan Allah Junaid sai lokacin ya d'auke hannu daga kuncinshi yace "To ni kuma waye zai dake ni a baki ina d'an soja guda."
Jinjina kai yayi yace "Da kyau to tunda kana tuna hakan."
Mayar da kallonshi yayi kan boss da ke harkar gabanshi kamar baisan sunayi ba ya kamo hannunshi yace "Soja d'an soja muje ko."
Wucewa sukayi inda suma suka bi bayansu lieutenant na jin haushin colonel saboda sam baya ganin laifin Ammar, zaka iya cewa ma yafi nuna mishi k'auna fiye da Junaid da kuma Umaima da Jamila.
Saida ya d'an dafe kai yace "Eh, dan da k'yar ma na kawo kaina nan, na so na ce ka goye ni amma kuma..."
Kallonshi yayi yace "Amma kuma me?"
"Kana hushi da k'aninka, d'an uwanka, shak'ik'inka, sannan abokin rayuwarka." Duk yayi maganar ne cikin marairaicewa, k'ala bai ce masa ba sai ma wasu kwalaye dayake fito da su yana son d'auko wani magani, ya sha wahala kafin ya d'auko ya bud'e ya d'auki wanda yake buk'ata ya mayar da sauran, fitowa yayi daga d'akin jim kad'an ya dawo, ruwa ya bashi a roba tare da maganin yasha, d'aya maganin kuma ya sa a cikin kofi da ruwa, saida ya gama tafasa ya mik'a mishi ya shanye ya aje kofin, ba tare daya kalli fuskarshi ba yace "Ka kwanta kan gadon nan."
Ganin ya juya zai fita yasa Amar cewa "Har zuwa wane lokaci?"
Ba tare daya juyo ba yace "Har a busa k'aho."
Murmushi kawai Amar yayi shi kuma ya fice, yana fita kuma motar shi ya fad'a ya tayar, mai gadi na bud'e k'ofa ya suri motar yayi waje, hanya ya d'auka shima kamar zai tashi sama, shi ma dai kamar su Junaid hanyar gidan roumji ya nufa, sai dai duk gudunshi bai iya riskar su Junaid ba dan sun rigashi d'aukar hanya kuma suma gudu suke sosai.
*K'arfe* 06:20 na yamma Amar ya fito cikin shiri ya samu Ummy ya mata sallama yace zai tafi shima k'auye saboda kar ran Abba ya b'ace, cike da damuwa tace "Amar kayi hak'uri mana zuwa gobe sai mu tafi tare, tunda kaga ba lafiya ne da kai ba."
Dariyar gefen labb'a yayi yace "Haba Ummy lafiya ta lau fa, ki bari naje kawai kar Abba ya ga kamar bamu ji maganar sa bane, kuma kinga dukansu fa ina kyautata zaton can suka tafi, kinga gwara nima na hanzarta na tafi ko da ana sallah magriba ne saina isa."
Cikin sanyi tace "Shikenan Amar, Allah ya tsare ka ya kare gabanka da bayanka."
Murmushi yayi sosai yace "Ameen Ummy, sai mun dawo."
"A dawo lafiya." Ta fad'a tana binshi da kallo harya fita.
Yana fita su Hamna na shigowa da motonsu dan saida suka kai d'inki sannan suka dawo gida, haka ma ba jimawa Umaima ta shigo gidan tare da drebanta, sai Jamila da ta shigo gaf da magrib daga école.
*Gidan roumji*
Rana ta fad'i sosai su Junaid suka iso, tunda suka fito daga mota lieutenant da colonel ke kallonsu da mamaki, k'arasowa sukayi cikin mutane suka gaishesu da girmamawa tare da musu ta'aziya, sun shiga cikin gidan dan yiwa na cikin gida suma sai ga motar boss ta karyo kwana, da k'arfi ya ci burki ya kashe motar ya fito makulli da waya a hanu, ga kyau ga kyan tsari da hallita sai dai a wurina babu kyan hali, da k'akk'arfar tafiyar nan tashi ya k'araso yana sallama amma fa wanda yayi sa'a ne kad'ai ke ya ji sallamar dan kamar bai so yayi ba, saida yayi zaune ya tank'washe k'afafun shi kafin ya fara bawa na kusa da shi hannu, colonel kam daya tsura mishi ido a ranshi cewa yayi "Lallai yaro na, wannan da ace kai général ne na soja da anshiga uku, ko mu dake iyayanka dai saida muka gaishe da mutane kafin muka zauna saboda wurin mutuwa ne, amma kai sai bayan ka zauna kake gaishe da wanda ke kusa da kai, humm."
Lieutenant kuma haushin Ammar ne d'in ya kusa kashe shi shiyasa ma ya d'auke kallonshi daga kan Ammar d'in dan kar zuciya ta kwashe shi ya mareshi, yana gama tashi ta'aziyar ya fara danna waya, da sauri Labaran ya kalleshi yace "Ammar ka shiga ciki mana ku gaisa da matan."
Kallonshi yayi lokaci d'aya kuma ya mayar da kallonshi kan wayar, yana kallon wayar tashi ya mik'e yasa takalminshi ya nufi cikin gidan a ranshi yana fad'in "Yanzu mutum na shiga zasu saka maka ido suna kallo, kowace burinta ka mata magana ta ji dad'i, mtssss, shiyasa na tsani shiga irin taron nan."
*Ikon Allah sai kallo, to Ammar me ka d'auki matan? Sai kace wasu tsofaffin...*😏
Yana kallonsu su Junaid suma suna kallonshi haka kowa ya gama ya fito, suna zuwa kuma wasu har sun nufi masallaci wasu kuma na alwala, suma alwala sukayi suka nufi masallacin, tare sukayi sallah suka fito, fitowar lieutenant da colonel yayi daidai da shigowar Amar cikin kwanar, lieutenant a ranshi yace "Wato yaran nan sun raina mutane ko? Amma laifin duk na waccen babban kwabon ne."
Tsaye yayi hakan yasa colonel ma tsayawa, su Junaid da Ammar na fitowa lieutenant yace su zo, Amar na ganinsu saboda ya hasko fitilar motarshi ya tsaya wajensu ya fito, cikin girmamawa yace "Abba ina wuninku, har kunyi sallah ko? Bara nima na yi alwala."
Zai wuce lieutenant ya dawo da shi baya ya kallesu dukansu yace "Wato da na ce ku taho gaba d'aya shine kowa yayi gaban kanshi, yanzu ribar me kuka ci da kuka nunawa mutane ku kanku ba had'e yake ba?"
Shiru sukayi dukansu suna kallon k'asa sai boss da idonshi ke kan wayarshi yana latsawa ya rumgume hannu d'aya, juyawa lieutenant yayi ya kalli Ammar d'in da ya ga ya mayar dashi wani d'an iska ma, wani haushi ne ya kashe shi sai kawai yasa tafin hannu ya bangaji k'eyar Ammar, bai ankara ba yaji bugun dan haka ya juyo ya kalli mahaifin nashi, had'e fuska yayi ba alamar wasa yace "Abba meye haka? Kai baka san cewa kai shine mutum ba? Duk wani abu mai mahimmanci a cikin k'wak'walwa yake, so kake kasa na rasa komai nawa?"
Hannu ya d'aga da nufin sake mazgeshi colonel yayi saurin rik'e hannunshi yace "Ba kamata yayi ace ka fara tambayar meya faru ba kafin duk wannan b'acin ran, ko baka kula da fuskar Amar bane, sannan ka dubi Junaid ma, baka tunanin ko wani abu ya samesu a hanyar?"
Fizge hannunshi yayi yana kallon Ammar yayi k'wafa kafin ya kallesu yace "To naji, wa zai fad'a mana meya faru?"
Shiru sukayi sai wuk'i-wuk'i da ido da sukeyi, Labaran ne ya kalli Jamil yace "Kai ba tambayarku ake ba kuka mana shiru?"
Jamil kam kallon Ammar yayi wanda ya ga ya kalleshi, idonshi kad'ai suka fassara mishi manufar kallonshi, dan haka ya ja baki yayi gum saboda tsoro, sai dai ya manta gaba da gabanta, colonel ne cikin tsawa yace " Wai ya ana muku magana kuka mana shiru? Shin ku yan mata ne bare ku d'auka son ku muke."
Wani kallo Ammar ya mishi yace "Idan ma yan mata ne mu sai mu tsaya muna sauraron tsofaffi irinku."
Labaran kam bushewa yayi da dariya inda lieutenant ya zabura zai bugeshi Labaran d'in ya rik'e shi, cikin dariyarshi yace "To ai gaskiya ya fad'a, tsofaffin ne mu mana."
Kamar daga sama suka ji saukar mari ji kake "Tauuuuuu."
Da sauri Junaid ya dafe kunci saboda wani mahaukacin mari da colonel ya watsa mishi yana fad'in "Iskanci kai, ana muku magana zaku d'auke mu wasu shashashu."
Lieutenant ne yace "Meye haka saboda Allah? Yanzu shine kenan yayi laifi a wurin nan? Me ya sa ba zaka mari wannan ba dake kusa da kai yana mana shak'iyanci sai wannan? Saboda a ganinka wannan ne ka haifa su kuma wad'annan duk 'ya'yan yan uwanka ne, mtsss."
Lieutenant Jamil ya kalla ya zaro ido yace "Yanzu zaku fad'a mana meya faru da har yasa ku ka k'i bin umarnin dana baku na a taho tare?"
Cikin rawar murya Jamil yace " Dama da zamu..."
Karaf Amar ya karb'a da cewa "Ni ne fa na samu had'ari akan moton wani abokina, shine da na zo gida sai aka ce su Junaid su taho saboda Ammar shi ya duba min ciwon, bayan Ummy ta zo gida kuma sai shima suka ce ya taho, ni kuma ganin duk sun taho yasa na kasa hak'ura na taho."
Colonel ne ya kalli Junaid yace "To kai kuma uban wa ya ci uwaka a bakin na ka?"
Bawan Allah Junaid sai lokacin ya d'auke hannu daga kuncinshi yace "To ni kuma waye zai dake ni a baki ina d'an soja guda."
Jinjina kai yayi yace "Da kyau to tunda kana tuna hakan."
Mayar da kallonshi yayi kan boss da ke harkar gabanshi kamar baisan sunayi ba ya kamo hannunshi yace "Soja d'an soja muje ko."
Wucewa sukayi inda suma suka bi bayansu lieutenant na jin haushin colonel saboda sam baya ganin laifin Ammar, zaka iya cewa ma yafi nuna mishi k'auna fiye da Junaid da kuma Umaima da Jamila.