Sashe 180
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Biki yayi biki* ta bakin wani mawak'i, ba kid'a ba wak'a amma fa holewa ake, b'angarenshi ya sake tabka mishi gyara na rashin mutumci, haka kuma yana can ana gyara masa gidansa dan yace wannan ita ce abokiyar gwabzawa sai sun matsa daga kusan manya karsu kashe su basu shirya ba. Ita kanta Hamna k'awayenta sun mata bajinta sosai, dan har daga Niamey da Katsina wasu sun zo aurenta, taji dad'i sosai na ganinsu a kusa da ita a wannan lokaci.
Ko da magriba tayi Ummy ta tsaya tsayin daka wajen gyara amaryarta kuma surukarta, wata mahaukaciyar doguwar riga ta tsadadden tissue aka saka mata, yaji d'inki sosai mai d'aukar ido da d'aukar hankali, tun daga sama zuwa hannaye har gwiwa a matse yake, amma daga k'asa sai aka bud'e sosai yayi tsatsaye har yana jan k'asa, kwalliya ta d'auka daga wajen wata k'awarta ta ban mamaki, kwalliya ce daidai da fuskarta inda aka d'ora komai kan muhallinsa, d'aurin d'an kwali kam kamar ba hannu ne yayi aikin ba, dama duk wani abin da zata saka saida Ummy ta turare shi har da pant da bras d'inta, sannan ita ma aka sa ta zauna kan kujerar turaren bayan an turare mata jiki, abubuwan da Ummy ta k'ara bata tasha ta ci taji tana neman yin amai, tana daf da fashewa da kuka tana fad'in "Wallahi Ummy amai zanyi, ya ishe ni haka dan Allah."
Da sauri mai kwalliyar tace "Rufa min asiri Hamna karki zubo da hawaye a idon nan."
Hararanta tayi tace "Dallah kwalliyar me?"
Karb'a Ummy tayi tace "Shikenan to barshi haka, ai muna tare dake a gidan."
Ummy zata fita daga d'akin wayarta tayi k'ara, ko da ta d'auka tace "Ango ya akayi?"
Daga inda yake yace "Ummy kun shirya? Mota fa na nan tafe d'aukar kankana."
Saida ta kalli Hamna dake ta had'e rai k'awarta na cewa ta dinga murmushi dan Allah sannan tace "Me ye na sauri Ammar? Kuma nan da can d'in zata shiga mota? To ai ko hannu aka sa sai a tura motar k'ofar gidan."
"A'a Ummy sarauniya ce yau, bari mota zata kaita."
"To shikenan." Ummy ta fad'a dan abar canzen, ta d'auka mota d'aya ce yake nufi da zata d'auki amaryar, amma abun mamaki da firgita tunanin mai rai sai jininin motoci suka ji, sanda aka fito ne suka ganewa kansu sarautar Allah, kai Umy ita dai a ganinta motocin nan bana abokanshi bane kad'ai kamar harda hayarsu akayi, mota ta bawa guda arba'in baya ta kusa kaiwa hamsin, to wace tsiyar zasuyi da su, in suka shiga ina za'a kaisu, to wata motar ma yanda ta zo haka ta juya ta koma bata d'auki ko sauro ba bare mutum.
Bakin duniya, da suka kwashi matan mutane gudu na idon duniya suka dinga yi dasu, aa fa gudun ma a cikin tsari suke yin shi, dan babu motar data fita daga layin da suke, saida suka lula suka kai k'uryar ali d'an sofo sannan suka kutsi hanyar da saida ta sada su da zarya ta k'arshen k'ashe-sheshe, yawo kawai sukayi mutune tun ana jin dadi su dai har wani ya fara k'orafi saboda dare ya k'ara yi, sai lokacin kad'ai suka koma aka aje amarya aka shigar da ita gidan ta.
Iyaye duk kanta suka taru inda suke mata nasiha kan hak'uri, saida kowa ya gama na shi Hajia da Husseina su dai suka fad'a mata ta zama mai d'auke kai daga lamarin bawan Allah nan, wannan taurin kai da fad'a masa magana kai tsaye ta kiyaye, tayi kamar yer uwarta har ta koma ga Allah ba'a tab'a jin ko sautin muryarsu ba da sunan tashin hankali, ita dai sauraronsu kawai take, amma ba zata iya abinda Amna tayi ba, wacce ta fad'a mata idan wani ya b'ata mishi rai saiya huce kanta ta hanyar darzata kan gado ko kuma ya mata wanka da ruwan sanyi ko sata cin abincin da batayi niyya ba, to ita yaushe zata iya da kwatirarsa? Ai ya kasheta ko ita ta kashe shi ne kawai.
A sannu sannu aka watse aka barta ita kadai, zaune kan gado tana k'arewa d'akin kallo, saida ta gama tas sannan ta mayar da fuskarta cikin babban mayafinta tana kallon hannayenta masu ban lalle, Ammar? Ammar? Mahaukaci ne fa suka had'ata dashi.
*Uwar Lalla kinji fa?*
*Yana* saman hanya tare da Amar na tuk'i sai su Junaid a baya lieutenant ya kira shi, d'auka yayi lieutenant yace "Kana ina Ammar?"
"Abba ina kan hanya."
Cikin d'an jin kunya yace "Ka siye kaza ne?"
Murmushi yayi yace "Abba duk angon dake son jin dad'i dolenshi ai ya siyo kaza."
Su Amar kallonshi sukayi sai Abba da yace "To ka siyo guda biyu ina son d'aya nima."
Tafin hannu yasa ya rufe fuska wai kunya yana fad'in "Lah Abba na wallahi ka bani kunya, kai ma kaza kake so? Kenan dai uwata zata mana k'ane."
Had'e fuska yayi yace "Kai bana son iskanci, ita kad'ai ce mai k'wan haihuwa? To da uwarka nake ni."
Ido ya zaro cike da shak'iyanci yace "Kai Abba na Ummy fa, kayi hak'uri dan Allah kaje wajen uwa Zeitu."
"Ammar." Ya fad'a cikin muryar karsashi, a hankali yace "Na'am Abba."
"To ka siyo ka kawo min, kuma dan ubanka da kai zamu je siyan bakin uwarta ka tunda kai ka zigeta har yanzu bata kula ni."
Tintsirewa yayi da dariya yace "Abba na karka damu, ni d'in nan nine na rabaku kuma ni zan had'a ku, bari na siyo maka kaji manya guda uku, d'aya ta yau d'aya ta gobe d'aya ta jibi."
Girgiza kai lieutenant yayi kawai ya kashe wayar, shi kam gyara zama yayi kamar mai shirin bacci yana fad'in "Abba ba dan karka karya min uwa ba ma ai da saina saka maka magani a kazar nan."
Dariya suka saka inda Junaid yace "D'an iska dai baiji dad'i ba wallahi."
"Inji uban wa?" Ya fad'a idonshi a rufe, Jibril ne yace "Inji shi mana."
Wata k'arar ya fitar a bakinshi irin a banza kenan, Amar yace ma "Muje a siyowa Abba kaji, shi ma yau dad'i yake so yaji."
Kallonshi Amar yayi yace "Yanzu kai banda abunka ina Hassan ina wannan abu na yara? Ai sai ku masu tafasashen jini."
Bud'a ido yayi ya kalleshi sama da k'asa yace "Ko yanzu ka had'ashi da yarinya Allah zaka yi mamakin sakamakon da zai haifar."
Su dai dariya suke har suka isa wajen madugu😋, tik'a tik'an kaji ya siya kafin suka wuce gida, da shigarsu suka samu lieutenant a waje, wuyan rigarshi ya shak'a yace "Sai mun je ka bata hak'uri, tunda ka hure mata kunne yanzu gaisuwarma sai dai kaji ta wani ce, ina kwana."
Dariya yayi yace "Abba sake ni to ai ba guduwa zanyi ba."
Sakinshi yayi suka shiga ciki gidan ya d'an fara yin shiru alamar kowa ya tafi bawa makwancinshi hakk'inshi, kai tsaye d'akin Ummy suka shige a tare.
Ja sukayi suka tsaya ganin Ummy ta gama saka doguwar rigar bacci har k'asa tana d'aure gashinta da k'aramin mad'auri, kallonshi Ammar yayi yana dariya yace "Abba da alama ita ma hak'uri zaka bata, to gashi ni na tafi kafin na makance."
Juyawa yayi yana ajiye leda d'aya lieutenant ya jawoshi, juyowa tayi ta kallesu tace "Ya zaku shigo haka babu sallama?"
Juyawa tayi tana fad'in "Ko da yake ai kamar uba kamar d'ansa, ba mamaki kam."
K'arasa shiga sukayi inda lieutenant ke fad'in "To miye a ciki dan bamuyi sallama ba, kai da kaya ai duk mallakar wuya ne."
Kallonshi tayi fuska a had'e tace "Amma ai shi yaron mamallakina ne, ba shine ya mallake ni ba."
Kallon juna sukayi da Ammar yace "Wannan shalelen Hajia ko bayan raina fa shi zai rik'eki."
Ba alamar wasa tace "Shiyasa dama ka k'i bani takardata saboda kaga ka kusa mutuwa, kana so dole sai nayi maka wankan takaba."
Gaba d'aya suka juya suka kalleshi yana dariya, zaune Ummy tayi bakin gadon tana kallonshi, saida ya gaji da kanshi yace "Ummy Abba na kike wa fatan mutuwa? To ai bai tsufa ba."
Da hannu ta nuna masa tace "Ka duba da kyau ka gani, kwana nawa ne ya rage masa yayi ritaya (retraite)?"
Murmushi yayi yace "Amma Ummy ai a wajen aiki ne zaiyi ritaya, a gida kuwa yana nan da k'ark'onshi."
Lieutenant ta kalla tana d'an jujjuya baki tace "Zaku iya fita idan kun gama abinda ya kawo ku."
Kallon juna suka sake yi sai yayi laushi sosai yace "Abba ni zan tafi fatan nasara, mata uku ne dama ke matuk'ar jigata ni a duniyar nan, ga d'ayar nan."
Ya nuna Ummy sannan yace "D'ayar kuma yau ta shiga hannu na, d'ayan kuma kullum ina mata addu'a Allah ya kai rahama k'abarinta."
Saida har ya fita lieutenant ya bi bayanshi yace "Kai ni fa uwar nan taka tsoro ma take bani, ua zanyi da ita ne?"
"Kawo kunnenka kaji Abba." Mik'o masa yayi ya masa rad'a, saida ya gama ya kalleshi baki sake yace "Ammar kaji tsoron Allah, yanzu haka kake so na wa uwarka abinda ko da k'uruciya banyi ba."
Da ido da gira ya masa alamar kawai yayi kafin yace "Abba saida safe, karna tsaya gyara tsofaffin hannu ni kuma na samu matsala."
Da kallo ya bishi har ya fita, komawa yayi ciki ya sameta har ta kwanta, cire babbar rigarshi yayi ya shiga wanka, ya jima a ciki kafin ya fito ya saka doguwar riga ya zauna kusanta, hannu yasa ya tayar da ita zaune yana kallon fuskarta, cike da rarrashi yace "Sa'adatu na, fushin me kike yi dani haka har yanzu?"
Kawar da kai tayi gefe ta k'ara tsuke baki, murmushi yayi yace "Haba uwar ya'yana, matar da babu mai irinta a duniyar nan, kiyi hak'uri mana ki daina hushin nan Allah ba kya kyau da hushi, kifa tuna bamu tab'a samun sab'ani ba da ke."
Kallonshi tayi tace "Kasan da haka amma shine kan k'aramin abu zaka sauya min, naje neman sulhu kuma wai har kace min k'ofa a bud'e take na tafi baka rik'e ni, hummm."
Ko da magriba tayi Ummy ta tsaya tsayin daka wajen gyara amaryarta kuma surukarta, wata mahaukaciyar doguwar riga ta tsadadden tissue aka saka mata, yaji d'inki sosai mai d'aukar ido da d'aukar hankali, tun daga sama zuwa hannaye har gwiwa a matse yake, amma daga k'asa sai aka bud'e sosai yayi tsatsaye har yana jan k'asa, kwalliya ta d'auka daga wajen wata k'awarta ta ban mamaki, kwalliya ce daidai da fuskarta inda aka d'ora komai kan muhallinsa, d'aurin d'an kwali kam kamar ba hannu ne yayi aikin ba, dama duk wani abin da zata saka saida Ummy ta turare shi har da pant da bras d'inta, sannan ita ma aka sa ta zauna kan kujerar turaren bayan an turare mata jiki, abubuwan da Ummy ta k'ara bata tasha ta ci taji tana neman yin amai, tana daf da fashewa da kuka tana fad'in "Wallahi Ummy amai zanyi, ya ishe ni haka dan Allah."
Da sauri mai kwalliyar tace "Rufa min asiri Hamna karki zubo da hawaye a idon nan."
Hararanta tayi tace "Dallah kwalliyar me?"
Karb'a Ummy tayi tace "Shikenan to barshi haka, ai muna tare dake a gidan."
Ummy zata fita daga d'akin wayarta tayi k'ara, ko da ta d'auka tace "Ango ya akayi?"
Daga inda yake yace "Ummy kun shirya? Mota fa na nan tafe d'aukar kankana."
Saida ta kalli Hamna dake ta had'e rai k'awarta na cewa ta dinga murmushi dan Allah sannan tace "Me ye na sauri Ammar? Kuma nan da can d'in zata shiga mota? To ai ko hannu aka sa sai a tura motar k'ofar gidan."
"A'a Ummy sarauniya ce yau, bari mota zata kaita."
"To shikenan." Ummy ta fad'a dan abar canzen, ta d'auka mota d'aya ce yake nufi da zata d'auki amaryar, amma abun mamaki da firgita tunanin mai rai sai jininin motoci suka ji, sanda aka fito ne suka ganewa kansu sarautar Allah, kai Umy ita dai a ganinta motocin nan bana abokanshi bane kad'ai kamar harda hayarsu akayi, mota ta bawa guda arba'in baya ta kusa kaiwa hamsin, to wace tsiyar zasuyi da su, in suka shiga ina za'a kaisu, to wata motar ma yanda ta zo haka ta juya ta koma bata d'auki ko sauro ba bare mutum.
Bakin duniya, da suka kwashi matan mutane gudu na idon duniya suka dinga yi dasu, aa fa gudun ma a cikin tsari suke yin shi, dan babu motar data fita daga layin da suke, saida suka lula suka kai k'uryar ali d'an sofo sannan suka kutsi hanyar da saida ta sada su da zarya ta k'arshen k'ashe-sheshe, yawo kawai sukayi mutune tun ana jin dadi su dai har wani ya fara k'orafi saboda dare ya k'ara yi, sai lokacin kad'ai suka koma aka aje amarya aka shigar da ita gidan ta.
Iyaye duk kanta suka taru inda suke mata nasiha kan hak'uri, saida kowa ya gama na shi Hajia da Husseina su dai suka fad'a mata ta zama mai d'auke kai daga lamarin bawan Allah nan, wannan taurin kai da fad'a masa magana kai tsaye ta kiyaye, tayi kamar yer uwarta har ta koma ga Allah ba'a tab'a jin ko sautin muryarsu ba da sunan tashin hankali, ita dai sauraronsu kawai take, amma ba zata iya abinda Amna tayi ba, wacce ta fad'a mata idan wani ya b'ata mishi rai saiya huce kanta ta hanyar darzata kan gado ko kuma ya mata wanka da ruwan sanyi ko sata cin abincin da batayi niyya ba, to ita yaushe zata iya da kwatirarsa? Ai ya kasheta ko ita ta kashe shi ne kawai.
A sannu sannu aka watse aka barta ita kadai, zaune kan gado tana k'arewa d'akin kallo, saida ta gama tas sannan ta mayar da fuskarta cikin babban mayafinta tana kallon hannayenta masu ban lalle, Ammar? Ammar? Mahaukaci ne fa suka had'ata dashi.
*Uwar Lalla kinji fa?*
*Yana* saman hanya tare da Amar na tuk'i sai su Junaid a baya lieutenant ya kira shi, d'auka yayi lieutenant yace "Kana ina Ammar?"
"Abba ina kan hanya."
Cikin d'an jin kunya yace "Ka siye kaza ne?"
Murmushi yayi yace "Abba duk angon dake son jin dad'i dolenshi ai ya siyo kaza."
Su Amar kallonshi sukayi sai Abba da yace "To ka siyo guda biyu ina son d'aya nima."
Tafin hannu yasa ya rufe fuska wai kunya yana fad'in "Lah Abba na wallahi ka bani kunya, kai ma kaza kake so? Kenan dai uwata zata mana k'ane."
Had'e fuska yayi yace "Kai bana son iskanci, ita kad'ai ce mai k'wan haihuwa? To da uwarka nake ni."
Ido ya zaro cike da shak'iyanci yace "Kai Abba na Ummy fa, kayi hak'uri dan Allah kaje wajen uwa Zeitu."
"Ammar." Ya fad'a cikin muryar karsashi, a hankali yace "Na'am Abba."
"To ka siyo ka kawo min, kuma dan ubanka da kai zamu je siyan bakin uwarta ka tunda kai ka zigeta har yanzu bata kula ni."
Tintsirewa yayi da dariya yace "Abba na karka damu, ni d'in nan nine na rabaku kuma ni zan had'a ku, bari na siyo maka kaji manya guda uku, d'aya ta yau d'aya ta gobe d'aya ta jibi."
Girgiza kai lieutenant yayi kawai ya kashe wayar, shi kam gyara zama yayi kamar mai shirin bacci yana fad'in "Abba ba dan karka karya min uwa ba ma ai da saina saka maka magani a kazar nan."
Dariya suka saka inda Junaid yace "D'an iska dai baiji dad'i ba wallahi."
"Inji uban wa?" Ya fad'a idonshi a rufe, Jibril ne yace "Inji shi mana."
Wata k'arar ya fitar a bakinshi irin a banza kenan, Amar yace ma "Muje a siyowa Abba kaji, shi ma yau dad'i yake so yaji."
Kallonshi Amar yayi yace "Yanzu kai banda abunka ina Hassan ina wannan abu na yara? Ai sai ku masu tafasashen jini."
Bud'a ido yayi ya kalleshi sama da k'asa yace "Ko yanzu ka had'ashi da yarinya Allah zaka yi mamakin sakamakon da zai haifar."
Su dai dariya suke har suka isa wajen madugu😋, tik'a tik'an kaji ya siya kafin suka wuce gida, da shigarsu suka samu lieutenant a waje, wuyan rigarshi ya shak'a yace "Sai mun je ka bata hak'uri, tunda ka hure mata kunne yanzu gaisuwarma sai dai kaji ta wani ce, ina kwana."
Dariya yayi yace "Abba sake ni to ai ba guduwa zanyi ba."
Sakinshi yayi suka shiga ciki gidan ya d'an fara yin shiru alamar kowa ya tafi bawa makwancinshi hakk'inshi, kai tsaye d'akin Ummy suka shige a tare.
Ja sukayi suka tsaya ganin Ummy ta gama saka doguwar rigar bacci har k'asa tana d'aure gashinta da k'aramin mad'auri, kallonshi Ammar yayi yana dariya yace "Abba da alama ita ma hak'uri zaka bata, to gashi ni na tafi kafin na makance."
Juyawa yayi yana ajiye leda d'aya lieutenant ya jawoshi, juyowa tayi ta kallesu tace "Ya zaku shigo haka babu sallama?"
Juyawa tayi tana fad'in "Ko da yake ai kamar uba kamar d'ansa, ba mamaki kam."
K'arasa shiga sukayi inda lieutenant ke fad'in "To miye a ciki dan bamuyi sallama ba, kai da kaya ai duk mallakar wuya ne."
Kallonshi tayi fuska a had'e tace "Amma ai shi yaron mamallakina ne, ba shine ya mallake ni ba."
Kallon juna sukayi da Ammar yace "Wannan shalelen Hajia ko bayan raina fa shi zai rik'eki."
Ba alamar wasa tace "Shiyasa dama ka k'i bani takardata saboda kaga ka kusa mutuwa, kana so dole sai nayi maka wankan takaba."
Gaba d'aya suka juya suka kalleshi yana dariya, zaune Ummy tayi bakin gadon tana kallonshi, saida ya gaji da kanshi yace "Ummy Abba na kike wa fatan mutuwa? To ai bai tsufa ba."
Da hannu ta nuna masa tace "Ka duba da kyau ka gani, kwana nawa ne ya rage masa yayi ritaya (retraite)?"
Murmushi yayi yace "Amma Ummy ai a wajen aiki ne zaiyi ritaya, a gida kuwa yana nan da k'ark'onshi."
Lieutenant ta kalla tana d'an jujjuya baki tace "Zaku iya fita idan kun gama abinda ya kawo ku."
Kallon juna suka sake yi sai yayi laushi sosai yace "Abba ni zan tafi fatan nasara, mata uku ne dama ke matuk'ar jigata ni a duniyar nan, ga d'ayar nan."
Ya nuna Ummy sannan yace "D'ayar kuma yau ta shiga hannu na, d'ayan kuma kullum ina mata addu'a Allah ya kai rahama k'abarinta."
Saida har ya fita lieutenant ya bi bayanshi yace "Kai ni fa uwar nan taka tsoro ma take bani, ua zanyi da ita ne?"
"Kawo kunnenka kaji Abba." Mik'o masa yayi ya masa rad'a, saida ya gama ya kalleshi baki sake yace "Ammar kaji tsoron Allah, yanzu haka kake so na wa uwarka abinda ko da k'uruciya banyi ba."
Da ido da gira ya masa alamar kawai yayi kafin yace "Abba saida safe, karna tsaya gyara tsofaffin hannu ni kuma na samu matsala."
Da kallo ya bishi har ya fita, komawa yayi ciki ya sameta har ta kwanta, cire babbar rigarshi yayi ya shiga wanka, ya jima a ciki kafin ya fito ya saka doguwar riga ya zauna kusanta, hannu yasa ya tayar da ita zaune yana kallon fuskarta, cike da rarrashi yace "Sa'adatu na, fushin me kike yi dani haka har yanzu?"
Kawar da kai tayi gefe ta k'ara tsuke baki, murmushi yayi yace "Haba uwar ya'yana, matar da babu mai irinta a duniyar nan, kiyi hak'uri mana ki daina hushin nan Allah ba kya kyau da hushi, kifa tuna bamu tab'a samun sab'ani ba da ke."
Kallonshi tayi tace "Kasan da haka amma shine kan k'aramin abu zaka sauya min, naje neman sulhu kuma wai har kace min k'ofa a bud'e take na tafi baka rik'e ni, hummm."