Sashe 34
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Uhmmm." Ta fad'a ba tare data kalleshi ba, d'orawa yayi da "Zan samu kulawarki a wannan daren kuwa? Naga baba na yayi kane-kane a kan gadon."
D'agowa tayi ta kalleshi ta juya ta kalli Ameer dake ta baccinshi, sake kallonshi tayi tace "Ka d'auke shi mana saika kaishi d'akin su."
Kallon Ameer yayi shi ma ya zagaya zai d'auke shi yace "Allah kasa kar yaron nan ya hanani sakewa."
Murmushi tayi wanda harya fitar da sauti, kallonta yayi yace "Wallahi yaron nan rigimarki ce ya koya, ko da yana jariri bai hanani yin rayuwa da ke ba kamar yanda yanzun yake hana ni."
Zaune tayi bakin gadon tace "Watak'ila yana tsanani buk'atar a kasance auta ne shiyasa, yasan idan ya baka fili saika masa k'ane."
Harara ya cillo mata yace "Idan na tashi yi a hanani na gani, kinsan dai ko gabanshi na so zanyi yanda nake so ko?"
Dariya tayi tace "To ka barshi yanzu saimu jaraba mu gani."
A lokacin daya d'auki Ameer ne yace "Bana so na jefo shi k'asa ai."
K'arar bud'a k'ofa yasa Ameer bud'a ido tare da zabura ya kalli wanda ya d'auke shi dan ya hango mamanshi zaune, rintse ido Abbas yayi wanda yasa Ameer cikin muryar bacci cewa "Yeee! Dady na ganka bud'e idon."
Kafin ya bud'e idon ido ya sake cewa "Dady yaushe ka dawo? Ka kawo min computer ta?"
D'ago shi yayi suka kalli juna yace "Muje na kaika d'akinka ka kwanta da safe zan nuna maka wacce na siyo maka, ko Khalifa baya da irinta."
Ai sai Ameer ya dirko daga kafad'ar Abbas yace "Um um Dady, ni tare da Ammie na zan kwana, abinda ma tunda ka tafi tare muke kwana, kai kaje d'akin ka."
Da gudu ya yo kan Sameera ya kwanta kan cinyoyinta yana kallon Abbas, ganin yana nufoshi yana fad'in "In dai kana son na baka computer sai ka zo mun tafi, idan ba haka ba kuma sai dai na bawa *Amjad* (d'an Naseer) ita."
Zagaya hannayenshi yayi ta kunkumin Sameera ya mak'aleta sosai yace "Um um, bana so ni dai."
Dariya Sameera tayi rumgume shi tace "Babana kenan, yaro kwana a gado d'aya tare da mahaifiyarshi yafi mishi komai na duniya ko?"
"Eh Ammie." Kwance Abbas yayi kan gadon dan ko yace ya zare mishi ido kuka ne zai saka musu a daren nan, kallonshi yayi yace "Zo nan baba na nayi kewarka sosai."
Rarrafawa yayi ya kwanta kan k'irjin shi ya rumgume shi, Sameera ma kwance tayi ta d'ora kanta a kafad'ar shi tace "Ka ci abinci kuwa?"
Ido lumshe yace "Um." Tsautsayi yasa Sameera cewa "Auta na kayi abinci kaji, kasan..."
Wata k'ara ta saki saboda mintsinin da Abbas ya mata a mazaunai, zaune ta tashi idonta har sun fara ja saboda zafi, kallonshi tayi shi kuma ba tare daya kalleta ba yace "Gobe ma na sake jin kin kira shi auta kiga yanda zanyi da ke."
Kamar zata fashe da kuka tace "To meye a ciki dan na kira shi da auta dan Allah?"
Ido rufe kamar wanda zaiyi bacci yana ci gaba da shafa bayan Ameer yace "Saboda yawon kiran na shi da auta zaisa wata rana ki fad'a lokacin amsar addu'a, ni kuma so nake sai kin dire min sha biyu insha Allahu." Shiru ta mishi ta kwanta, gashinta yake shafawa da d'aya hannun a haka har bacci ya d'auke su.
*BASRABA*
Tunda garin Allah ya waye Takawa yake jin kamar ba shi ba, a haka har akayi sallah la'asar ya dawo b'angaren shi kan kilisarshi ya kishigid'a, haka kawai yaji yana buk'atar ganin liman, dan haka yasa d'aya daga cikin masu tsaron k'ofar shi ya nemo mishi liman, kusan dama unguwar duk duk fadawan fada ne a ciki, dan haka ba jimawa sai gashi ya dawo tare da liman, jakadiyar uwar d'aki na ganin haka ta garzaya ta fad'awa uwar d'aki, cikin tashin hankali tace "Kin tabbatar liman ne ya shiga wajenshi?"
Cikin girmamawa tace "Ko zanyi k'arya uwar d'aki harshena yayi kad'an daya furta miki k'arya, yanda na ga liman tare da bafaden nan ina fatan ganin annabi haka."
Wata ajiyar zuciya ta sauke marar dad'in sauti tace "Tashi kije, amma kar kiyi nisa dan zan buk'ace ki."
Tashi tayi ta fita ita kuma ta d'auki waya ta kira waziri, yana danna ok ya sake danna wurin nad'ar duk maganar da zasuyi kafin yayi magana, cikin tashin hankali tace "Waziri ka ce na bar komai a hannunka, amma gashi kana neman ka mana kwance da aiki, ko kasan cewa takawa ya nemi ganin liman? Yanzu haka suka turakarshi."
"What!" Cewar waziri, sausauta murya yayi yace "Ki gafarce ni uwar d'aki, yau ba sai gobe ba zan miki maganin matsalar nan."
"Ka tabbatar?"
"Na baki tabbacin haka." D'if ta kashe wayar, sai lokacin kuma ta tambayi kanta "Amma me yasa baki tambayeshi meye zaiyi ba?"
Shiru tayi tana tunani kafin daga bisani ta d'aga kafad'a irin bai dameta ba tare da cewa "Koma me zaiyi indai zaisa a fasa auren kuma naga yarinyar can Ameera cikin garari to hakan ya isheni."
A wajen takawa da liman kuma sun jima suna tattaunawa kafin ya mishi maganar neman auren Safiyya, nan liman ya nuna mishi ba komai ya kuma gamsu da bayanan takawa, amma duk da haka saida yace idan har akwai matsala to gwara abar maganar, takawa ya nuna mishi babu komai kawai suyi musu fatan alkairi, da haka takawa ya nemi alfarmar a d'aura auren nan kusa, amma liman yace a bashi lokaci dan sanar da mahaifiyar yarinyar da ita yarinyar kanta, cikin mutumta juna suka gama tattaunawarsu liman ya bar takawa lafiya.
Bayan tafiyar liman haka kawai takawa ya nemi ganin duka iyalin na shi a turakarshi, nan suka hallara uwaye da 'ya'ya maza da mata, nasiha ya dinga musu da gargad'i da jan kunne akan rayuwa, daga bisani ya musu addu'a tare da jadadda musu rik'o da zumunci, kar su yarda su bari mulki ko abin duniya ya shiga tsakaninsu, da haka kowa ya tashi ya koma inda ya fito suka bar takawa lafiya k'alau.
Wannan ganin shine na k'arshe da suka mishi da numfashi a tare da shi, domin kuwa waziri ne ya biya wasu yan daba guda biyu sukayi shiga irinta fadawan gidan aka shigo dasu gidan a motar dreba ta kai yara makaranta, wajen takawa suka shiga suka taushe mishi kai da pillow har saida ya daina numfashi, tunda asuba kuma aka farga da rasuwar takawar, liman daya zo masallaci da k'arfin gwiwar sanar dashi kowa ya amince, kuma bayan nan yayi istikhara kan lamarin, duk da ubangiji ya nuna mishi wani duhu a cikin abun amma kuma hasken dake ciki shi yafi yawa, dan haka ya zo da niyyar idan sun gama sallah ya fad'a mishi ya amince ko juma'ar da zata zo ma za'a iya d'aura auren ba damuwa.
*Abuja*
Tunda asuba da sukayi sallah sukayi karatu suke zaune falo cikin raha da k'aunar juna, Abbas ne ya kalli Raihan yace "Mama na wai har yanzu sakamakon na ku bai fito bane?"
Cikin sakin fuska tace "Dady yau zai fito, anjima kad'an zamu je mu dubo."
Kallon Abdul yayi yace "Abdul, anjima ka shirya zamu fita tare da kai a motarka."
Da girmamawa ya amsa da "Ok Dady, zuwa k'arfe nawa?"
Kallonshi Abbas yayi yasan ya tambaya ne dan ya shirya kafin lokacin, dan haka yace mishi " 08:00 pm."
Jinjina kai yayi yace "Ok Dady."
Cike da kunya Raihan ta kalle shi tace "Dady, alk'awarin mu?"
Da mamaki yace " Wane alk'awari kuma nayi mama na?"
Sanda kanta tayi k'asa cikin kunya tace "Dady u promise me zaka fitar damu abroad idan result d'in mu yayi kyau."
Murmushi yayi yace "To banda rigimar mama na ai result d'in bai fito ba, ki jira ya fito sai mu gani."
Cikin sangarta tace "Dady gaskiya mun fasa zuwa abroad d'in, mu *Niger* muke so mu tafi."
Murmushi yayi kafin yace wani abu Ammie dake zaune tace "Shawara mai kyau, kinga kenan lokaci yayi da zaku kaiwa auntynku ziyara."
Rauda ce da sauri tace "Wace auntynmu kuma?"
Hararanta Ammie tayi tace "Husna da zatayi aure niger ba dalilin auntynku dake aure a can bane ita ma harta samu miji a can."
Cikin yanayin na tuno Rauda tace "Ohhh hakane fa, ki ce aunty *Khairiya* ('yar Bakura yaya ga Husna), gaskiya indai hakane aunty Raihan zanje tare da ke nima na ga niger."
Cikin ruwan sanyi Raihan tace "Babu inda zaki bini yarinya, ki jira idan auren Husna ya tashi saiku tafi tare da Ammie."
Abbas ne yace "To ai ko ke baza ki ba sai auren ya tashi, in ya so daga basraba saiku wuce niger d'in."
Turo baki tayi tace "Amma dai Dady za'a baro ni can wurin aunty Khairiya ko?"
Mik'ewa yayi yana fad'in "U have a choice." Ganin ya nufi kitchen yasa Khalifa cewa "Dady kayi b'atan kai, nan fa madafa ce."
Juyowa yayi yace "Wajen matata zanje, dukanku nan kun manta da ita tana can tana faman girka mana abinda zamu ci."
Dariya Khalifa yayi ya d'ago mishi yatsa irin 👍yace "Fatan alkairi Dady, amma fa banda fad'a kuma, kar ku zo ku rikice mana sai munje rabo."
Dariya Abbas yayi ya mishi dak'uwa yana fad'in "Hancin ubanka Imran."
Yana bud'a k'ofar kitchen d'in Harira ce ya fara hangowa suna ta kai da kawowa, wani bak'in ciki ne yaji ya taso mishi tare da tuna abubuwan da suka faru a baya, k'aramin tsaki yayi ya juya zai fita sai kuma Sameera ta juyo, murmushi ta sakar masa ta mik'awa Razeena had'in kabejin da tayi tace "Ki saka a fridge kafin a kammala sauran."
Karb'a tayi ita kuma ta juya wajenshi tana ci gaba da murmushi harta isa tana fad'in "Barka yallab'ai, har kun kammala karatun?"
D'agowa tayi ta kalleshi ta juya ta kalli Ameer dake ta baccinshi, sake kallonshi tayi tace "Ka d'auke shi mana saika kaishi d'akin su."
Kallon Ameer yayi shi ma ya zagaya zai d'auke shi yace "Allah kasa kar yaron nan ya hanani sakewa."
Murmushi tayi wanda harya fitar da sauti, kallonta yayi yace "Wallahi yaron nan rigimarki ce ya koya, ko da yana jariri bai hanani yin rayuwa da ke ba kamar yanda yanzun yake hana ni."
Zaune tayi bakin gadon tace "Watak'ila yana tsanani buk'atar a kasance auta ne shiyasa, yasan idan ya baka fili saika masa k'ane."
Harara ya cillo mata yace "Idan na tashi yi a hanani na gani, kinsan dai ko gabanshi na so zanyi yanda nake so ko?"
Dariya tayi tace "To ka barshi yanzu saimu jaraba mu gani."
A lokacin daya d'auki Ameer ne yace "Bana so na jefo shi k'asa ai."
K'arar bud'a k'ofa yasa Ameer bud'a ido tare da zabura ya kalli wanda ya d'auke shi dan ya hango mamanshi zaune, rintse ido Abbas yayi wanda yasa Ameer cikin muryar bacci cewa "Yeee! Dady na ganka bud'e idon."
Kafin ya bud'e idon ido ya sake cewa "Dady yaushe ka dawo? Ka kawo min computer ta?"
D'ago shi yayi suka kalli juna yace "Muje na kaika d'akinka ka kwanta da safe zan nuna maka wacce na siyo maka, ko Khalifa baya da irinta."
Ai sai Ameer ya dirko daga kafad'ar Abbas yace "Um um Dady, ni tare da Ammie na zan kwana, abinda ma tunda ka tafi tare muke kwana, kai kaje d'akin ka."
Da gudu ya yo kan Sameera ya kwanta kan cinyoyinta yana kallon Abbas, ganin yana nufoshi yana fad'in "In dai kana son na baka computer sai ka zo mun tafi, idan ba haka ba kuma sai dai na bawa *Amjad* (d'an Naseer) ita."
Zagaya hannayenshi yayi ta kunkumin Sameera ya mak'aleta sosai yace "Um um, bana so ni dai."
Dariya Sameera tayi rumgume shi tace "Babana kenan, yaro kwana a gado d'aya tare da mahaifiyarshi yafi mishi komai na duniya ko?"
"Eh Ammie." Kwance Abbas yayi kan gadon dan ko yace ya zare mishi ido kuka ne zai saka musu a daren nan, kallonshi yayi yace "Zo nan baba na nayi kewarka sosai."
Rarrafawa yayi ya kwanta kan k'irjin shi ya rumgume shi, Sameera ma kwance tayi ta d'ora kanta a kafad'ar shi tace "Ka ci abinci kuwa?"
Ido lumshe yace "Um." Tsautsayi yasa Sameera cewa "Auta na kayi abinci kaji, kasan..."
Wata k'ara ta saki saboda mintsinin da Abbas ya mata a mazaunai, zaune ta tashi idonta har sun fara ja saboda zafi, kallonshi tayi shi kuma ba tare daya kalleta ba yace "Gobe ma na sake jin kin kira shi auta kiga yanda zanyi da ke."
Kamar zata fashe da kuka tace "To meye a ciki dan na kira shi da auta dan Allah?"
Ido rufe kamar wanda zaiyi bacci yana ci gaba da shafa bayan Ameer yace "Saboda yawon kiran na shi da auta zaisa wata rana ki fad'a lokacin amsar addu'a, ni kuma so nake sai kin dire min sha biyu insha Allahu." Shiru ta mishi ta kwanta, gashinta yake shafawa da d'aya hannun a haka har bacci ya d'auke su.
*BASRABA*
Tunda garin Allah ya waye Takawa yake jin kamar ba shi ba, a haka har akayi sallah la'asar ya dawo b'angaren shi kan kilisarshi ya kishigid'a, haka kawai yaji yana buk'atar ganin liman, dan haka yasa d'aya daga cikin masu tsaron k'ofar shi ya nemo mishi liman, kusan dama unguwar duk duk fadawan fada ne a ciki, dan haka ba jimawa sai gashi ya dawo tare da liman, jakadiyar uwar d'aki na ganin haka ta garzaya ta fad'awa uwar d'aki, cikin tashin hankali tace "Kin tabbatar liman ne ya shiga wajenshi?"
Cikin girmamawa tace "Ko zanyi k'arya uwar d'aki harshena yayi kad'an daya furta miki k'arya, yanda na ga liman tare da bafaden nan ina fatan ganin annabi haka."
Wata ajiyar zuciya ta sauke marar dad'in sauti tace "Tashi kije, amma kar kiyi nisa dan zan buk'ace ki."
Tashi tayi ta fita ita kuma ta d'auki waya ta kira waziri, yana danna ok ya sake danna wurin nad'ar duk maganar da zasuyi kafin yayi magana, cikin tashin hankali tace "Waziri ka ce na bar komai a hannunka, amma gashi kana neman ka mana kwance da aiki, ko kasan cewa takawa ya nemi ganin liman? Yanzu haka suka turakarshi."
"What!" Cewar waziri, sausauta murya yayi yace "Ki gafarce ni uwar d'aki, yau ba sai gobe ba zan miki maganin matsalar nan."
"Ka tabbatar?"
"Na baki tabbacin haka." D'if ta kashe wayar, sai lokacin kuma ta tambayi kanta "Amma me yasa baki tambayeshi meye zaiyi ba?"
Shiru tayi tana tunani kafin daga bisani ta d'aga kafad'a irin bai dameta ba tare da cewa "Koma me zaiyi indai zaisa a fasa auren kuma naga yarinyar can Ameera cikin garari to hakan ya isheni."
A wajen takawa da liman kuma sun jima suna tattaunawa kafin ya mishi maganar neman auren Safiyya, nan liman ya nuna mishi ba komai ya kuma gamsu da bayanan takawa, amma duk da haka saida yace idan har akwai matsala to gwara abar maganar, takawa ya nuna mishi babu komai kawai suyi musu fatan alkairi, da haka takawa ya nemi alfarmar a d'aura auren nan kusa, amma liman yace a bashi lokaci dan sanar da mahaifiyar yarinyar da ita yarinyar kanta, cikin mutumta juna suka gama tattaunawarsu liman ya bar takawa lafiya.
Bayan tafiyar liman haka kawai takawa ya nemi ganin duka iyalin na shi a turakarshi, nan suka hallara uwaye da 'ya'ya maza da mata, nasiha ya dinga musu da gargad'i da jan kunne akan rayuwa, daga bisani ya musu addu'a tare da jadadda musu rik'o da zumunci, kar su yarda su bari mulki ko abin duniya ya shiga tsakaninsu, da haka kowa ya tashi ya koma inda ya fito suka bar takawa lafiya k'alau.
Wannan ganin shine na k'arshe da suka mishi da numfashi a tare da shi, domin kuwa waziri ne ya biya wasu yan daba guda biyu sukayi shiga irinta fadawan gidan aka shigo dasu gidan a motar dreba ta kai yara makaranta, wajen takawa suka shiga suka taushe mishi kai da pillow har saida ya daina numfashi, tunda asuba kuma aka farga da rasuwar takawar, liman daya zo masallaci da k'arfin gwiwar sanar dashi kowa ya amince, kuma bayan nan yayi istikhara kan lamarin, duk da ubangiji ya nuna mishi wani duhu a cikin abun amma kuma hasken dake ciki shi yafi yawa, dan haka ya zo da niyyar idan sun gama sallah ya fad'a mishi ya amince ko juma'ar da zata zo ma za'a iya d'aura auren ba damuwa.
*Abuja*
Tunda asuba da sukayi sallah sukayi karatu suke zaune falo cikin raha da k'aunar juna, Abbas ne ya kalli Raihan yace "Mama na wai har yanzu sakamakon na ku bai fito bane?"
Cikin sakin fuska tace "Dady yau zai fito, anjima kad'an zamu je mu dubo."
Kallon Abdul yayi yace "Abdul, anjima ka shirya zamu fita tare da kai a motarka."
Da girmamawa ya amsa da "Ok Dady, zuwa k'arfe nawa?"
Kallonshi Abbas yayi yasan ya tambaya ne dan ya shirya kafin lokacin, dan haka yace mishi " 08:00 pm."
Jinjina kai yayi yace "Ok Dady."
Cike da kunya Raihan ta kalle shi tace "Dady, alk'awarin mu?"
Da mamaki yace " Wane alk'awari kuma nayi mama na?"
Sanda kanta tayi k'asa cikin kunya tace "Dady u promise me zaka fitar damu abroad idan result d'in mu yayi kyau."
Murmushi yayi yace "To banda rigimar mama na ai result d'in bai fito ba, ki jira ya fito sai mu gani."
Cikin sangarta tace "Dady gaskiya mun fasa zuwa abroad d'in, mu *Niger* muke so mu tafi."
Murmushi yayi kafin yace wani abu Ammie dake zaune tace "Shawara mai kyau, kinga kenan lokaci yayi da zaku kaiwa auntynku ziyara."
Rauda ce da sauri tace "Wace auntynmu kuma?"
Hararanta Ammie tayi tace "Husna da zatayi aure niger ba dalilin auntynku dake aure a can bane ita ma harta samu miji a can."
Cikin yanayin na tuno Rauda tace "Ohhh hakane fa, ki ce aunty *Khairiya* ('yar Bakura yaya ga Husna), gaskiya indai hakane aunty Raihan zanje tare da ke nima na ga niger."
Cikin ruwan sanyi Raihan tace "Babu inda zaki bini yarinya, ki jira idan auren Husna ya tashi saiku tafi tare da Ammie."
Abbas ne yace "To ai ko ke baza ki ba sai auren ya tashi, in ya so daga basraba saiku wuce niger d'in."
Turo baki tayi tace "Amma dai Dady za'a baro ni can wurin aunty Khairiya ko?"
Mik'ewa yayi yana fad'in "U have a choice." Ganin ya nufi kitchen yasa Khalifa cewa "Dady kayi b'atan kai, nan fa madafa ce."
Juyowa yayi yace "Wajen matata zanje, dukanku nan kun manta da ita tana can tana faman girka mana abinda zamu ci."
Dariya Khalifa yayi ya d'ago mishi yatsa irin 👍yace "Fatan alkairi Dady, amma fa banda fad'a kuma, kar ku zo ku rikice mana sai munje rabo."
Dariya Abbas yayi ya mishi dak'uwa yana fad'in "Hancin ubanka Imran."
Yana bud'a k'ofar kitchen d'in Harira ce ya fara hangowa suna ta kai da kawowa, wani bak'in ciki ne yaji ya taso mishi tare da tuna abubuwan da suka faru a baya, k'aramin tsaki yayi ya juya zai fita sai kuma Sameera ta juyo, murmushi ta sakar masa ta mik'awa Razeena had'in kabejin da tayi tace "Ki saka a fridge kafin a kammala sauran."
Karb'a tayi ita kuma ta juya wajenshi tana ci gaba da murmushi harta isa tana fad'in "Barka yallab'ai, har kun kammala karatun?"