Sashe 163
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali Amna ta bud'a idonta, dishi dishi take gani da k'yar ta saisaita ta sauke idon akan Hamna data fi gani da kyau, murmushin k'arfin hali ta mata cikin muryar da bata fitowa sosai tace " *Saboda ke na dawo Hamna*."
Da mamaki suka kalli juna ita da Ammar suka kuma kallonta, a hankali tace "Ban gane saboda ni ba? Daga ina?"
Ba tare da murmushin nan ya bar fuskarta ba tace "Gidan da ba'a dawowa mana, saboda ke na dawo yer uwa, bana so na barki ba tare dana tafi da sanin kina hannun wanda ya dace ba, sannan ina so na bar amanar yarana hannunki, ko ba komai suna kallon uwa saboda yer uwata ce ke kuma fuskarmu d'aya, dan Allah yer uwa ki samu mai nagarta da kamala wanda zai iya k'aunarki a duk yanda kike kuma har abada kamar *miji na.*"
Hawayen da suka taho ma Hamna ne tayi saurin gogewa ta kalli Ammar tace "Me yasa take magana haka?"
Dariya Amna tayi har hak'oran makkarta ya fito tace "Ki saurare ni mana."
Girgiza kai tayi tace "Kinga kiyi shiru dan Allah baki da lafiya."
Mik'ewa tayi zata fita Amna tace "Yer uwa."
Tsayawa tayi ta juyo, saida ta lumshe ido tace "Ba zan tab'a damuwa da halin da zan bar yarana ba saboda na bar musu ke."
Da gudu Hamna ta fita daga d'akin tana kuka, kallonta yayi ya rik'e hannunta yace "Duniyata kiyi shiru ba'a son magana kinji."
Murmushi ta masa tace "Ina so nayi magana da yer uwata yah Ammar."
Cike da tabbatarwa yace "Shikenan kiyi shiru yanzu, idan jikinki ya k'ara kyau zan kira miki ita."
Wani murmushi tayi mai ciwo tace "Na fad'a maka zan kai gobe ne?"
Kafeta yayi da ido yace "Zaki kai insha Allahu har ma ki wuce."
Wani murmushin ta sake masa tace "Malam taimaka min na tashi ina so nayi sallah."
Saida yayi ajiyar zuciya yace "Kiyi hak'uri Amna, a yanayin da kike zaki iya jinkirta sallah."
Had'e fuska tayi tace "Ba ruwanka kawai ka tashe ni nayi sallah, idan na mutu me kake so na fad'awa Allah, idan kuma ba zaka iya ba ka kira min Ummy."
Zuba mata ido kawai yayi yana kallo, abinda ya lura dashi kawai zafin aikin da aka mata ne yanzu ya had'e mata jiki yasa take sambatun nan, da taji ya k'yaleta sai kawai ta fara k'ok'arin tashi tana fad'in "Ni banga anfanin zamanka anan ba in ba zaka sani yin sallah ba, kawai ka barni na tashi na gaishe da ubangiji na."
Rik'eta ya kwantar da ita yana daddab'ata, kamar wacce k'walwarta ta samu matsala haka take fad'in "Ammar ka sake ni na tashi nayi sallah, bana son haka wallahi ko kad'an, wai kai kake da aljanna ne da zaka saka ni a ciki? Ko so kake Allah ya k'ona ni."
Bai saketa ba bai kuma tashi ba saida Ummy ta shigo dubata saboda Hamna data fita tana kuka kuma ta k'i magana, da sauri ta fita ta d'auko allura ta zo ta mata, ba jimawa bacci ya d'auketa kad'ai ya sake ta.
*Kullum* haka Amna take tunda ta haihu, mai saurin kuka da tausayi baya iya tsayawa kusanta saboda maganganunta masu karyar da zuciya ne, indai idonta biyu ba bacci take ba to maganganu ne zatayi ta sakowa, duk wanda zai zo ganinta saita mishi nasiha, ka kula da yaranka kn kana da su, ka kula da mijinka in kana da shi, ka dage wajen karatunka in mai karatu ne, hakan ne yasa duk wanda yaje ganinta sai dai ya dawo yana zubar da hawaye, a cikin k'ank'anin lokaci kowa maganarta yake. Yaro kam ko da ta haife shi dama aka d'orashi kan madara, da fari anyi hakane saboda ganin jikinta, amma yanzu abinda ya tabbatar ma kowa tana jin jiki shine, duk yanda yaron zaiyi kuka a kawo mata shi ta bashi nono saita k'i, haka zata dage ita ba zata bashi nono ba, sai manya suka fara tunanin ko iska ne dan babu abinda basa yi, addu'a aka dage da mata amma babu abinda ke sauyawa, wani lokacin tana bacci haka zaka ga hawaye na bin fuskarta, data farka sai dai ta tashi da kuka, to fa zata iya yin awa goma ba tace um bare um um ba, haka suka kwashi kwana *bakwai* a asibiti, sallamarta akayi suka koma gida dan sun ce ciwonta bana asibiti bane.
*Ranar da* suka dawo gida...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_62_
*A ranar da* suka dawo gida kuma wani ikon Allah sai abun yayi sauk'i, ta ci abinci sosai tayi wanka ta gyara kanta sosai, kowa yayi farin ciki da faruwar hakan, musamman Hamna tafi kowa farin ciki, har yamma dai babu wata matsalar komai, yaro dai ne tana saka shi a nono zata cire shi ta aje, an idar da sallah magriba Ummy ta kalli Hamna tace "Hamna ki taimaka ki siyo mana kayan sanyin da za'a saka mishi mana, dan da alama garin akwai hadari."
Amsawa tayi da "To Ummy."
Mik'ewa Ummy tayi tana fad'in "Bari na d'auko miki kud'in."
Da sauri tace "A'a Ummy ki barshi ma akwai a hannu na."
Da sauri Amna dake zaune k'afafu mik'e ta d'aga rigarta inda aka mata aiki tace "Kin gani ko Ummy, zata kula dasu ko bayan ba raina."
Hararanta Hamna tayi tace "Uwarki zan ci kika sake mana maganar mutuwa."
Da sauri tasa hannu ta rufe baki tace "Nayi shiru to, yi hak'uri tafi Hajia."
Murmushi Hamna tayi ta tashi ta fita, a farfajiyar ta had'u da Shureim da gudu ya tareta, dafa shi tayi tace "Daga ina kake?"
Cikin muryarshi ta yara yace "K'ofar gida ni da yaya Ammar da Appa."
Kallonshi kawai tayi da ido, wanda ya kamata ya kira Appa shi ya kira da yaya, wanda ke mazaunin kakanshi kuma ya kira da Appa, wannan wace irin *BADAK'ALA* ce? Cikin tunani bata san ta fara tafiya ba saida taji ya rik'e hannunta yana fad'in "Aunty ina zaki je? Ina zuwa."
Kallonshi tayi tace "To muje mu siyowa sabon bebynmu kaya ko."
Da gudu ya rigata k'arasawa wajen motar, bud'ewa tayi ta shigar dashi sannan ta shiga, mai gadi na bud'e mata k'ofar anan ta ganshi tsaye tare da Abba da Labaran, sauke gilashin tayi tare "Abba barkanku."
"Ina zaki je?" Ita ce tambayar daya jefo mata, cikin ladabi tace "Ummy ce ta aike ni na siyowa bébé kayan sanyi, amma yanzu mun dawo dan tace akwai hadari a gari."
Cikin sakin fuska yace "Shikenan sai kin dawo."
Kallon Shureim yayi yace "Hein ba magana?"
Ammar kawai ya kalla yace "Yaya na tafi."
Murmushi ya masa yace "Saika dawo, ka kula da kanka."
Wucewa tayi suka d'auki hanya, sun bar nan kenan Amie ta zo yin barka, gaishesu tayi suka amsa ta tambayi Ammar ya mai jiki da bébé, cikin amon muryar da yake nuna babu wasa ya amsa mata, ciki ta shiga kai tsaye b'angare Amna ta nufa, nan ta samu Ummy suka gaisa, saida suka gama gaisawa fa Amna sannan tace "Ummy ina Hamna take?"
Cikin sakin fuska tace "Hamna ko bata jima da fita ba, amma yanzu zata dawo nasan ba zata kai ko kasuwa ba."
Hira suka fara tab'awa da Amna sai Ummy data bar musu falon, ba jimawa da fitar Ummy kuma Hamna ta dawo, Zeituna ta ci karo da ita saita fad'a mata yanzu Ummy ta shiga ciki, dan haka saita shiga kawai inda Shureim ke mata rigimar ta koma yawo dashi, kai tsaye d'akinta suka shiga ta same ta tana duba wasu kaya, kallonta tayi tace "Har kun dawo wai?"
"Wallahi Ummy, kinga kayan." Ta fad'a tana mik'a mata ledar, bud'ewa tayi tana dubawa sai Shureim dake kamo hannunta da k'arfi yana fad'in "Ki bani ni, ki bani."
Umly ce ta kalleshi tace "Wai me za'a baka?"
Dan kar Ummy ta dakeshi yasa Hamna sakar masa makullin, yana jin ta sake masa saiya fita a guje ta bishi da kallo, tana juyowa suka had'a da Ummy dake murmushi, cikin taushin murya tace "Ki k'ara hak'uri Hamna, insha Allahu komai ya kusa zuwa k'arshe, tunda a
mahaifin yaron nan ya canza al'amuran gidan nake son fad'a ma Hajia, matsalar d'aya ita ce ta yanda zan fara fad'a, amma nasan ko da na fad'a rai ba zai b'ace ba kamar zamanin baya."
Cike da damuwa Hamna ta kalleta tace "Ummy ni kaina tsoro nake ji, wallahi kullum tunanin al'amarin gigita k'walwata yake, duk da yanzu dai abubuwa sun canza, amma muyi kallon abun ta b'angaren yer uwata da kuma Abba, Ummy ya zasu ji idan suka ji maganar nan, ya yer uwata zata kalleni taji wai Shureim d'ana ne, d'an nawa ma wanda na haifa tare da mijinta, duk da dai kafin aurensu ne amma abun akwai gigitarwa, sannan Abba da yake mishi kallon d'an shi shima ya zaiji Ummy?"
Jinjina kai Ummy tayi tace "Wallahi Hamna karki so ki tona raina kiji yanda a kowace rana nake bacci da fargaban nan, ni kaina nasan wannan abune mai matuk'ar d'aure ne, abune da ko da ya tab'a faruwa to ba dai a k'asar hausa ko kuma anan kusa ba, k'anwata Gaishata da bana b'oye ma komai, amma sai gashi wannan karan har alk'awarin fad'a mata da nayi bai cika ba, Hamna tun tana tambayata na fad'a mata har ta kai ta gaji ta daina, ni kaina bansan ta inda zan fara kawo k'arshen labarin nan da nine na fara shi ba tun farko."
Cikin jimami tace "Kawai Ummy mu jira Amna ta samu lafiya a gama sabgar nan, kukan kura kawai zamuyi mu fad'a, in ya so ayita ta k'are kawai ko mun huta mu ma."
Jinjina kai tayi tace "Allah ya shige mana gaba."
Da mamaki suka kalli juna ita da Ammar suka kuma kallonta, a hankali tace "Ban gane saboda ni ba? Daga ina?"
Ba tare da murmushin nan ya bar fuskarta ba tace "Gidan da ba'a dawowa mana, saboda ke na dawo yer uwa, bana so na barki ba tare dana tafi da sanin kina hannun wanda ya dace ba, sannan ina so na bar amanar yarana hannunki, ko ba komai suna kallon uwa saboda yer uwata ce ke kuma fuskarmu d'aya, dan Allah yer uwa ki samu mai nagarta da kamala wanda zai iya k'aunarki a duk yanda kike kuma har abada kamar *miji na.*"
Hawayen da suka taho ma Hamna ne tayi saurin gogewa ta kalli Ammar tace "Me yasa take magana haka?"
Dariya Amna tayi har hak'oran makkarta ya fito tace "Ki saurare ni mana."
Girgiza kai tayi tace "Kinga kiyi shiru dan Allah baki da lafiya."
Mik'ewa tayi zata fita Amna tace "Yer uwa."
Tsayawa tayi ta juyo, saida ta lumshe ido tace "Ba zan tab'a damuwa da halin da zan bar yarana ba saboda na bar musu ke."
Da gudu Hamna ta fita daga d'akin tana kuka, kallonta yayi ya rik'e hannunta yace "Duniyata kiyi shiru ba'a son magana kinji."
Murmushi ta masa tace "Ina so nayi magana da yer uwata yah Ammar."
Cike da tabbatarwa yace "Shikenan kiyi shiru yanzu, idan jikinki ya k'ara kyau zan kira miki ita."
Wani murmushi tayi mai ciwo tace "Na fad'a maka zan kai gobe ne?"
Kafeta yayi da ido yace "Zaki kai insha Allahu har ma ki wuce."
Wani murmushin ta sake masa tace "Malam taimaka min na tashi ina so nayi sallah."
Saida yayi ajiyar zuciya yace "Kiyi hak'uri Amna, a yanayin da kike zaki iya jinkirta sallah."
Had'e fuska tayi tace "Ba ruwanka kawai ka tashe ni nayi sallah, idan na mutu me kake so na fad'awa Allah, idan kuma ba zaka iya ba ka kira min Ummy."
Zuba mata ido kawai yayi yana kallo, abinda ya lura dashi kawai zafin aikin da aka mata ne yanzu ya had'e mata jiki yasa take sambatun nan, da taji ya k'yaleta sai kawai ta fara k'ok'arin tashi tana fad'in "Ni banga anfanin zamanka anan ba in ba zaka sani yin sallah ba, kawai ka barni na tashi na gaishe da ubangiji na."
Rik'eta ya kwantar da ita yana daddab'ata, kamar wacce k'walwarta ta samu matsala haka take fad'in "Ammar ka sake ni na tashi nayi sallah, bana son haka wallahi ko kad'an, wai kai kake da aljanna ne da zaka saka ni a ciki? Ko so kake Allah ya k'ona ni."
Bai saketa ba bai kuma tashi ba saida Ummy ta shigo dubata saboda Hamna data fita tana kuka kuma ta k'i magana, da sauri ta fita ta d'auko allura ta zo ta mata, ba jimawa bacci ya d'auketa kad'ai ya sake ta.
*Kullum* haka Amna take tunda ta haihu, mai saurin kuka da tausayi baya iya tsayawa kusanta saboda maganganunta masu karyar da zuciya ne, indai idonta biyu ba bacci take ba to maganganu ne zatayi ta sakowa, duk wanda zai zo ganinta saita mishi nasiha, ka kula da yaranka kn kana da su, ka kula da mijinka in kana da shi, ka dage wajen karatunka in mai karatu ne, hakan ne yasa duk wanda yaje ganinta sai dai ya dawo yana zubar da hawaye, a cikin k'ank'anin lokaci kowa maganarta yake. Yaro kam ko da ta haife shi dama aka d'orashi kan madara, da fari anyi hakane saboda ganin jikinta, amma yanzu abinda ya tabbatar ma kowa tana jin jiki shine, duk yanda yaron zaiyi kuka a kawo mata shi ta bashi nono saita k'i, haka zata dage ita ba zata bashi nono ba, sai manya suka fara tunanin ko iska ne dan babu abinda basa yi, addu'a aka dage da mata amma babu abinda ke sauyawa, wani lokacin tana bacci haka zaka ga hawaye na bin fuskarta, data farka sai dai ta tashi da kuka, to fa zata iya yin awa goma ba tace um bare um um ba, haka suka kwashi kwana *bakwai* a asibiti, sallamarta akayi suka koma gida dan sun ce ciwonta bana asibiti bane.
*Ranar da* suka dawo gida...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_62_
*A ranar da* suka dawo gida kuma wani ikon Allah sai abun yayi sauk'i, ta ci abinci sosai tayi wanka ta gyara kanta sosai, kowa yayi farin ciki da faruwar hakan, musamman Hamna tafi kowa farin ciki, har yamma dai babu wata matsalar komai, yaro dai ne tana saka shi a nono zata cire shi ta aje, an idar da sallah magriba Ummy ta kalli Hamna tace "Hamna ki taimaka ki siyo mana kayan sanyin da za'a saka mishi mana, dan da alama garin akwai hadari."
Amsawa tayi da "To Ummy."
Mik'ewa Ummy tayi tana fad'in "Bari na d'auko miki kud'in."
Da sauri tace "A'a Ummy ki barshi ma akwai a hannu na."
Da sauri Amna dake zaune k'afafu mik'e ta d'aga rigarta inda aka mata aiki tace "Kin gani ko Ummy, zata kula dasu ko bayan ba raina."
Hararanta Hamna tayi tace "Uwarki zan ci kika sake mana maganar mutuwa."
Da sauri tasa hannu ta rufe baki tace "Nayi shiru to, yi hak'uri tafi Hajia."
Murmushi Hamna tayi ta tashi ta fita, a farfajiyar ta had'u da Shureim da gudu ya tareta, dafa shi tayi tace "Daga ina kake?"
Cikin muryarshi ta yara yace "K'ofar gida ni da yaya Ammar da Appa."
Kallonshi kawai tayi da ido, wanda ya kamata ya kira Appa shi ya kira da yaya, wanda ke mazaunin kakanshi kuma ya kira da Appa, wannan wace irin *BADAK'ALA* ce? Cikin tunani bata san ta fara tafiya ba saida taji ya rik'e hannunta yana fad'in "Aunty ina zaki je? Ina zuwa."
Kallonshi tayi tace "To muje mu siyowa sabon bebynmu kaya ko."
Da gudu ya rigata k'arasawa wajen motar, bud'ewa tayi ta shigar dashi sannan ta shiga, mai gadi na bud'e mata k'ofar anan ta ganshi tsaye tare da Abba da Labaran, sauke gilashin tayi tare "Abba barkanku."
"Ina zaki je?" Ita ce tambayar daya jefo mata, cikin ladabi tace "Ummy ce ta aike ni na siyowa bébé kayan sanyi, amma yanzu mun dawo dan tace akwai hadari a gari."
Cikin sakin fuska yace "Shikenan sai kin dawo."
Kallon Shureim yayi yace "Hein ba magana?"
Ammar kawai ya kalla yace "Yaya na tafi."
Murmushi ya masa yace "Saika dawo, ka kula da kanka."
Wucewa tayi suka d'auki hanya, sun bar nan kenan Amie ta zo yin barka, gaishesu tayi suka amsa ta tambayi Ammar ya mai jiki da bébé, cikin amon muryar da yake nuna babu wasa ya amsa mata, ciki ta shiga kai tsaye b'angare Amna ta nufa, nan ta samu Ummy suka gaisa, saida suka gama gaisawa fa Amna sannan tace "Ummy ina Hamna take?"
Cikin sakin fuska tace "Hamna ko bata jima da fita ba, amma yanzu zata dawo nasan ba zata kai ko kasuwa ba."
Hira suka fara tab'awa da Amna sai Ummy data bar musu falon, ba jimawa da fitar Ummy kuma Hamna ta dawo, Zeituna ta ci karo da ita saita fad'a mata yanzu Ummy ta shiga ciki, dan haka saita shiga kawai inda Shureim ke mata rigimar ta koma yawo dashi, kai tsaye d'akinta suka shiga ta same ta tana duba wasu kaya, kallonta tayi tace "Har kun dawo wai?"
"Wallahi Ummy, kinga kayan." Ta fad'a tana mik'a mata ledar, bud'ewa tayi tana dubawa sai Shureim dake kamo hannunta da k'arfi yana fad'in "Ki bani ni, ki bani."
Umly ce ta kalleshi tace "Wai me za'a baka?"
Dan kar Ummy ta dakeshi yasa Hamna sakar masa makullin, yana jin ta sake masa saiya fita a guje ta bishi da kallo, tana juyowa suka had'a da Ummy dake murmushi, cikin taushin murya tace "Ki k'ara hak'uri Hamna, insha Allahu komai ya kusa zuwa k'arshe, tunda a
mahaifin yaron nan ya canza al'amuran gidan nake son fad'a ma Hajia, matsalar d'aya ita ce ta yanda zan fara fad'a, amma nasan ko da na fad'a rai ba zai b'ace ba kamar zamanin baya."
Cike da damuwa Hamna ta kalleta tace "Ummy ni kaina tsoro nake ji, wallahi kullum tunanin al'amarin gigita k'walwata yake, duk da yanzu dai abubuwa sun canza, amma muyi kallon abun ta b'angaren yer uwata da kuma Abba, Ummy ya zasu ji idan suka ji maganar nan, ya yer uwata zata kalleni taji wai Shureim d'ana ne, d'an nawa ma wanda na haifa tare da mijinta, duk da dai kafin aurensu ne amma abun akwai gigitarwa, sannan Abba da yake mishi kallon d'an shi shima ya zaiji Ummy?"
Jinjina kai Ummy tayi tace "Wallahi Hamna karki so ki tona raina kiji yanda a kowace rana nake bacci da fargaban nan, ni kaina nasan wannan abune mai matuk'ar d'aure ne, abune da ko da ya tab'a faruwa to ba dai a k'asar hausa ko kuma anan kusa ba, k'anwata Gaishata da bana b'oye ma komai, amma sai gashi wannan karan har alk'awarin fad'a mata da nayi bai cika ba, Hamna tun tana tambayata na fad'a mata har ta kai ta gaji ta daina, ni kaina bansan ta inda zan fara kawo k'arshen labarin nan da nine na fara shi ba tun farko."
Cikin jimami tace "Kawai Ummy mu jira Amna ta samu lafiya a gama sabgar nan, kukan kura kawai zamuyi mu fad'a, in ya so ayita ta k'are kawai ko mun huta mu ma."
Jinjina kai tayi tace "Allah ya shige mana gaba."