Sashe 148
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon daya mata tare da cije leb'enshi yana wani shegen murmushi yasa ta kallon Amna dake dariya tace "Taya kike tunanin zai tasar min yer uwa, kuma ko ba komai ai ni da yaranshi duk muna cikin motar."
Motarta ta nufa tana mik'a masa makullin tace "Bismillah."
Hararanta yayi yace "Drebanki ne ni da zan tuk'a ki?"
Jefa mishi makullin tayi ta bud'a gidan baya ta d'auki yaran d'aya bayan d'aya duk ta zaunar dasu, har zata zauna ya jawo ribom d'inta daya fito waje ya shiga wajen yaran ya zauna yana fad'in "Ba inda zan tuk'aki kinji yarinya."
Cikin jin haushi ta kalleta ta cire d'an kwalin ta mayar da ribom d'inta ta d'aura kallabin, zatayi magana Amna ta zagaya wajen mai tuk'i tana fad'in "Ya isa dan Allah, zauna nan ni saina tuk'a."
Lek'owa yayi daga ciki yace "Ke duniyata fita a idona in rufe, ai da kinga kina tuk'i to ki tabbata tukunyar tuwo ce ko kuma kan gado kike kina wainani son ranki, amma ba dai mota ba."
Sunkuyar da kai Amna tayi ta dawo gaba inda Hamna ta kalleshi tayi tsaki tace "Anji sanyi ba'a rufa ba Ammar, wai kai yaushe zaka girma ne?"
Ko kallonta baiyi ba yace "Ranar dana samu isasshen nono nasha."
Wani kallo ta masa mai nuni da cewa ashe ni ce banda hankali, saida ta shiga ta zauna tana mak'ala mad'aurinta tace "Yace baya so ki tuk'a mota mana saboda yana takaicin ya siya miki."
Saida ya d'auki Ameera ya d'ora kan k'afarshi yace "To banda kud'i, yan gidan nan naku kuma kowa taurin zuciyar tsiya ne dashi, k'aramin abu baya sa zuciyarsu ta kusa tsayawa bare na samu kud'i ta hanyarsu, dubi kakar nan taku kwanan baya mun d'auka zata shek'a ne amma ta tashi da ranta kuma."
Dariya suka bushe da ita Hamna har da rik'e ciki, tayar da motar sukayi taja suka fita, tun kafin ta hau titi yace "Ke kin tabbata dai kin iya tuk'i ko? Karki zo ki jawo min mutuwa, burina nan gaba duniyata ta haifa min yara goma sha d'aya."
Kallon Amna tayi tace "Ki ce mijinki ya min shiru akwai abubuwa da nake so su zauna min a kai, dan in ya ci gaba da surutun nan na tabbata saina manta har sunana ma."
"Haka kawai malama saina rufe baki na, babu wanda ya isa ehe."
Tafiya suke sosai cikin farin ciki dan dariya kawai yake basu suna karb'a, duk yanda Hamna take son ta dake ta fita shirginshi abun ya gagara, idan yayi wata katob'arar dole take darawa, yanzun ma yara duk sunyi bacci, kallon Hamna yayi ta madubi yace "Kankana wai ina budurwata ne?"
Saida ta nuna alamar b'acin rai tace "Wallahi Ammar karka sake kirana kankana, na fad'a maka bana so ko."
Amna kuma tana juyowa tace "Wacece kuma budurwarka?"
Kallonta Hamna tayi tace "Amie, ita yake so ita kuma bata da lokacin shi, ya addabeta nima kuma ya addabeni, na fad'a masa idan ya k'ara min maganar ta zan fad'a miki dan ba zai yiwu na ci amanarki ba."
Dariya yayi ya kalli Amna yace "Ya kike kallona? Ki fad'a mata mijinki mai lafiya ne ire irenku goma ma zan iya ji daku."
Juyowa Hamna tayi baki bud'e tace "Bala'i, ire irenmu ko ire iren matarka?"
Saida ya kalli tsakiyar idonta yace "Ku nace, dukanku dake da ita da takwas kamar ku."
Sun d'auki awa d'aya a k'alla kafin suka isa dan ba gudu take ba, kamar yanda suka yi tunani kam hakane ya faru, Hadiza da Chua'ibu sunyi farin ciki sosai na ganinsu tare, sunyi walwala sunyi hira da mahaifiyarsu sosai, inda daga k'arshe Hadiza ke tambayar Hamna ya labarin aure, kamar dai yanda ta saba yanzun ma cewa tayi kawai tayi ta mata addu'a, har yanzu bata samu wanda ya dace bane, amma data samu zasu ji labarin aurenta ita ma, Amna ce ta kalli mahaifiyarsu tace "Mama wallahi tana da samari masu nutsuwa da hankali, kawai bata shirya aure bane, amma kar kiga manyan mutanen dake zuwa wajenta gida."
Cikin jin haushi tace "K'arya nayi kenan? Ina ruwanki da maganarmu? Karki koma saka min baki."
Kallon mahaifiyarsu tayi zatayi magana Hadiza tace "Dakata Hamna, inhar kinsan gaskiya ne abinda ta fad'a to kiyi gaggawar tsayar da mijin aure, Hamna ba zan ji dad'i ba yau idan kika lalata mana sunan zuri'a, duk da ba a hannuna kuka tashi ba amma Hajia zata d'ora min laifin gurb'atarki, dan haka ina rok'onki dan Allah ki fitar da miji kiyi aurenki ki huta tun kafin girma ya k'ara kamaki, mace ce ke d'an lokacinki k'alilan ne, sannan idon mutane dayawa zai iya komawa kanki duba da aikinki da kuma abinda kike hawa yanzu, ki taimaka kinji ki rufa mana asiri da ma kanki."
Saida tayi k'ok'arin had'e kukanta tace "Naji Mama."
Hararan Amna tayi da take ganin ita ta had'ata da Maman, dariya ta mata ta mik'e ta fita daga d'akin, cikin nutsuwa Hadiza ta sake kallonta tace "Hamna, ki tabbatar min da wani abu d'aya mana."
Kallonta tayi hakan yasa ta cewa "Ki kula da kanki, ki kare mutumcinki kema bar ki kaishi inda ya dace."
Kasa tsayawa sukayi sai kawai suka zubo mata, cikin tausayin kanta ta fad'a k'afar maman tana kuka, hakan ne ya tayar mata da hankali ta fara tambayarta "Hamna lafiya? Daga magana, ko wani abun ne ya faru?"
Girgiza kai kawai tayi amma ba tace komai ba, da k'yar ta rarrasheta sai ajiyar zuciya da take saukewa.
*A da* malam Rabi'u kad'ai take shakka, amma yanzu har shi d'in ta daina tsoronshi musamman daya k'ara tsufa, fita ma bai cika yi ba inba masallaci ba ko wani abu daya zama dole, a baya mai zaman kanta ce, amma yanzu bayan rabuwar aurensu da Junaid ta zama karuwar gida, tana fita sanda take so ne kuma ta dawo sanda ta ga dama, kakarta ta rasu wata biyu da suka wuce daga ita sai mahaifiyarta yanzu a gidan, bud'ewar idonta yanzu babu inda bata zuwa neman kud'inta ta dawo, mahaifiyarta ta zubawa sarautar Allah ido, dan maganarta ba dama ba sosai take fitowa ba har yanzu bare kuma ta mata fad'a sosai har ta jita, sai dai fatan shiriya kawai ta gari.
Sai bayan magriba suka shigo gari, gaba d'aya falon Hajia suka yada zango suna sauke gajiya, Amna da duk bata jin dad'i ne take k'ok'arin gyara zamanta amma Ameera ta hana ta damar haka, cikin saurin hawan da bata san ko na meye ba ta d'an tureta tana fad'in "Dan Allah Ameera ki matsa min na huta, haba ke kenan sai lak'uwa."
Kallonta Ammar yayi ya kamo hannunta yana fad'in "Ke taho nan kinji, rabu da uwarki ta ji da d'an k'anninku wanda ke neman koya mata masifa."
Kallon kallo dai kawai akayi amma babu wanda yace wani abu, sai Amna cikin tausa murya tace "Wane k'aninsu kuma?"
Murmushi ya mata yace "Na cikinki mana da zai iya kai tsawon wata biyu zuwa d'aya da rabi."
Shiru kawai tayi ita ma sai tunanin maganarsa data fara, suna haka Junaid ya shigo da sallama da kuma fara'a a fuskarshi, gaisawa sukayi kafin ya matsa kusan Hajia, yanda yake sunne kai yasa ta kalleshi tace "Ya dai malam?"
Cike da kunya da fargaban abinda zai faru yace "Hajia dama na zo muyi magana ne."
"Akan me?" Ta fad'a ba annashuwa a tare da ita, saida ya d'an k'ara sauta muryarsa yace "Akan Salma ne."
Ba tare data kalleshi ba tace "Wace Salma fa?"
"Salma ta tonton Sani."
Da k'arfi ta juyo kanta ta kalleshi, cikin tsananin mamaki tace "Me kuma ya had'aka da ita? Meya faru?"
Sunkuyar da kai yayi kafin yace "Hajia dama ni da ita muna soyayya ne, shine yanzu na..."
"Ka me?" Yanda tayi magana da k'arfi tare da mik'ewa yasa kowa kallonta, saida ta gyara tsayuwarta tana fuskantarshi tace "...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_55_
"Junaid yanzu ma wani sabon rashin mutumcin ne ka zo min dashi? Ina ce kana d'aya daga cikin wanda suka fi kowa sanin bana buk'atar doguwar mu'amula tsakanin ahalina dana Inussa (yayan Alhaji), shine yanzu zaka zo min da wata banzar magana wacce k'arshe nasan zaka ce kana son auren jikarshi ne, to ban yarda ba kaji na fad'a maka, in kuma kace kaji ka gani to zan zuba maka ido a karo na biyu."
Kallonta yayi yace "Kiyi hak'uri Hajia idan ranki ya b'ace, wannan karan a shirye nake dana miki biyayya, idan har baki amince na aureta ba zan hak'ura, dan ba zan k'ara sab'ama umarninki ba."
Cike da zak'alk'alewa tace "To ban yarda ba, kaje ka nemi wata yarinyar ba dai wannan ba."
"Shikenan Hajia." Ya fad'a yana barin falon, da kallo Ammar ya bishi har ya fita, tab'e baki yayi ya d'auki Ameera dake ta narke masa ya fice shima, ko da Amna taje ta same shi har ya shiga wanka, yana fitowa duk taga yanayinshi ya canza amma ba tace komai ba, yana shiryawa cikin k'ananan kaya ya sake d'aukar makullin mota ya zo kusa da ita ya sumbaci goshinta yace "Zan fita saina dawo."
Motarta ta nufa tana mik'a masa makullin tace "Bismillah."
Hararanta yayi yace "Drebanki ne ni da zan tuk'a ki?"
Jefa mishi makullin tayi ta bud'a gidan baya ta d'auki yaran d'aya bayan d'aya duk ta zaunar dasu, har zata zauna ya jawo ribom d'inta daya fito waje ya shiga wajen yaran ya zauna yana fad'in "Ba inda zan tuk'aki kinji yarinya."
Cikin jin haushi ta kalleta ta cire d'an kwalin ta mayar da ribom d'inta ta d'aura kallabin, zatayi magana Amna ta zagaya wajen mai tuk'i tana fad'in "Ya isa dan Allah, zauna nan ni saina tuk'a."
Lek'owa yayi daga ciki yace "Ke duniyata fita a idona in rufe, ai da kinga kina tuk'i to ki tabbata tukunyar tuwo ce ko kuma kan gado kike kina wainani son ranki, amma ba dai mota ba."
Sunkuyar da kai Amna tayi ta dawo gaba inda Hamna ta kalleshi tayi tsaki tace "Anji sanyi ba'a rufa ba Ammar, wai kai yaushe zaka girma ne?"
Ko kallonta baiyi ba yace "Ranar dana samu isasshen nono nasha."
Wani kallo ta masa mai nuni da cewa ashe ni ce banda hankali, saida ta shiga ta zauna tana mak'ala mad'aurinta tace "Yace baya so ki tuk'a mota mana saboda yana takaicin ya siya miki."
Saida ya d'auki Ameera ya d'ora kan k'afarshi yace "To banda kud'i, yan gidan nan naku kuma kowa taurin zuciyar tsiya ne dashi, k'aramin abu baya sa zuciyarsu ta kusa tsayawa bare na samu kud'i ta hanyarsu, dubi kakar nan taku kwanan baya mun d'auka zata shek'a ne amma ta tashi da ranta kuma."
Dariya suka bushe da ita Hamna har da rik'e ciki, tayar da motar sukayi taja suka fita, tun kafin ta hau titi yace "Ke kin tabbata dai kin iya tuk'i ko? Karki zo ki jawo min mutuwa, burina nan gaba duniyata ta haifa min yara goma sha d'aya."
Kallon Amna tayi tace "Ki ce mijinki ya min shiru akwai abubuwa da nake so su zauna min a kai, dan in ya ci gaba da surutun nan na tabbata saina manta har sunana ma."
"Haka kawai malama saina rufe baki na, babu wanda ya isa ehe."
Tafiya suke sosai cikin farin ciki dan dariya kawai yake basu suna karb'a, duk yanda Hamna take son ta dake ta fita shirginshi abun ya gagara, idan yayi wata katob'arar dole take darawa, yanzun ma yara duk sunyi bacci, kallon Hamna yayi ta madubi yace "Kankana wai ina budurwata ne?"
Saida ta nuna alamar b'acin rai tace "Wallahi Ammar karka sake kirana kankana, na fad'a maka bana so ko."
Amna kuma tana juyowa tace "Wacece kuma budurwarka?"
Kallonta Hamna tayi tace "Amie, ita yake so ita kuma bata da lokacin shi, ya addabeta nima kuma ya addabeni, na fad'a masa idan ya k'ara min maganar ta zan fad'a miki dan ba zai yiwu na ci amanarki ba."
Dariya yayi ya kalli Amna yace "Ya kike kallona? Ki fad'a mata mijinki mai lafiya ne ire irenku goma ma zan iya ji daku."
Juyowa Hamna tayi baki bud'e tace "Bala'i, ire irenmu ko ire iren matarka?"
Saida ya kalli tsakiyar idonta yace "Ku nace, dukanku dake da ita da takwas kamar ku."
Sun d'auki awa d'aya a k'alla kafin suka isa dan ba gudu take ba, kamar yanda suka yi tunani kam hakane ya faru, Hadiza da Chua'ibu sunyi farin ciki sosai na ganinsu tare, sunyi walwala sunyi hira da mahaifiyarsu sosai, inda daga k'arshe Hadiza ke tambayar Hamna ya labarin aure, kamar dai yanda ta saba yanzun ma cewa tayi kawai tayi ta mata addu'a, har yanzu bata samu wanda ya dace bane, amma data samu zasu ji labarin aurenta ita ma, Amna ce ta kalli mahaifiyarsu tace "Mama wallahi tana da samari masu nutsuwa da hankali, kawai bata shirya aure bane, amma kar kiga manyan mutanen dake zuwa wajenta gida."
Cikin jin haushi tace "K'arya nayi kenan? Ina ruwanki da maganarmu? Karki koma saka min baki."
Kallon mahaifiyarsu tayi zatayi magana Hadiza tace "Dakata Hamna, inhar kinsan gaskiya ne abinda ta fad'a to kiyi gaggawar tsayar da mijin aure, Hamna ba zan ji dad'i ba yau idan kika lalata mana sunan zuri'a, duk da ba a hannuna kuka tashi ba amma Hajia zata d'ora min laifin gurb'atarki, dan haka ina rok'onki dan Allah ki fitar da miji kiyi aurenki ki huta tun kafin girma ya k'ara kamaki, mace ce ke d'an lokacinki k'alilan ne, sannan idon mutane dayawa zai iya komawa kanki duba da aikinki da kuma abinda kike hawa yanzu, ki taimaka kinji ki rufa mana asiri da ma kanki."
Saida tayi k'ok'arin had'e kukanta tace "Naji Mama."
Hararan Amna tayi da take ganin ita ta had'ata da Maman, dariya ta mata ta mik'e ta fita daga d'akin, cikin nutsuwa Hadiza ta sake kallonta tace "Hamna, ki tabbatar min da wani abu d'aya mana."
Kallonta tayi hakan yasa ta cewa "Ki kula da kanki, ki kare mutumcinki kema bar ki kaishi inda ya dace."
Kasa tsayawa sukayi sai kawai suka zubo mata, cikin tausayin kanta ta fad'a k'afar maman tana kuka, hakan ne ya tayar mata da hankali ta fara tambayarta "Hamna lafiya? Daga magana, ko wani abun ne ya faru?"
Girgiza kai kawai tayi amma ba tace komai ba, da k'yar ta rarrasheta sai ajiyar zuciya da take saukewa.
*A da* malam Rabi'u kad'ai take shakka, amma yanzu har shi d'in ta daina tsoronshi musamman daya k'ara tsufa, fita ma bai cika yi ba inba masallaci ba ko wani abu daya zama dole, a baya mai zaman kanta ce, amma yanzu bayan rabuwar aurensu da Junaid ta zama karuwar gida, tana fita sanda take so ne kuma ta dawo sanda ta ga dama, kakarta ta rasu wata biyu da suka wuce daga ita sai mahaifiyarta yanzu a gidan, bud'ewar idonta yanzu babu inda bata zuwa neman kud'inta ta dawo, mahaifiyarta ta zubawa sarautar Allah ido, dan maganarta ba dama ba sosai take fitowa ba har yanzu bare kuma ta mata fad'a sosai har ta jita, sai dai fatan shiriya kawai ta gari.
Sai bayan magriba suka shigo gari, gaba d'aya falon Hajia suka yada zango suna sauke gajiya, Amna da duk bata jin dad'i ne take k'ok'arin gyara zamanta amma Ameera ta hana ta damar haka, cikin saurin hawan da bata san ko na meye ba ta d'an tureta tana fad'in "Dan Allah Ameera ki matsa min na huta, haba ke kenan sai lak'uwa."
Kallonta Ammar yayi ya kamo hannunta yana fad'in "Ke taho nan kinji, rabu da uwarki ta ji da d'an k'anninku wanda ke neman koya mata masifa."
Kallon kallo dai kawai akayi amma babu wanda yace wani abu, sai Amna cikin tausa murya tace "Wane k'aninsu kuma?"
Murmushi ya mata yace "Na cikinki mana da zai iya kai tsawon wata biyu zuwa d'aya da rabi."
Shiru kawai tayi ita ma sai tunanin maganarsa data fara, suna haka Junaid ya shigo da sallama da kuma fara'a a fuskarshi, gaisawa sukayi kafin ya matsa kusan Hajia, yanda yake sunne kai yasa ta kalleshi tace "Ya dai malam?"
Cike da kunya da fargaban abinda zai faru yace "Hajia dama na zo muyi magana ne."
"Akan me?" Ta fad'a ba annashuwa a tare da ita, saida ya d'an k'ara sauta muryarsa yace "Akan Salma ne."
Ba tare data kalleshi ba tace "Wace Salma fa?"
"Salma ta tonton Sani."
Da k'arfi ta juyo kanta ta kalleshi, cikin tsananin mamaki tace "Me kuma ya had'aka da ita? Meya faru?"
Sunkuyar da kai yayi kafin yace "Hajia dama ni da ita muna soyayya ne, shine yanzu na..."
"Ka me?" Yanda tayi magana da k'arfi tare da mik'ewa yasa kowa kallonta, saida ta gyara tsayuwarta tana fuskantarshi tace "...
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_55_
"Junaid yanzu ma wani sabon rashin mutumcin ne ka zo min dashi? Ina ce kana d'aya daga cikin wanda suka fi kowa sanin bana buk'atar doguwar mu'amula tsakanin ahalina dana Inussa (yayan Alhaji), shine yanzu zaka zo min da wata banzar magana wacce k'arshe nasan zaka ce kana son auren jikarshi ne, to ban yarda ba kaji na fad'a maka, in kuma kace kaji ka gani to zan zuba maka ido a karo na biyu."
Kallonta yayi yace "Kiyi hak'uri Hajia idan ranki ya b'ace, wannan karan a shirye nake dana miki biyayya, idan har baki amince na aureta ba zan hak'ura, dan ba zan k'ara sab'ama umarninki ba."
Cike da zak'alk'alewa tace "To ban yarda ba, kaje ka nemi wata yarinyar ba dai wannan ba."
"Shikenan Hajia." Ya fad'a yana barin falon, da kallo Ammar ya bishi har ya fita, tab'e baki yayi ya d'auki Ameera dake ta narke masa ya fice shima, ko da Amna taje ta same shi har ya shiga wanka, yana fitowa duk taga yanayinshi ya canza amma ba tace komai ba, yana shiryawa cikin k'ananan kaya ya sake d'aukar makullin mota ya zo kusa da ita ya sumbaci goshinta yace "Zan fita saina dawo."