← Book details Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 198

Sashe 43

Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da k'yar ta kawo kanta gida tana kuka, amma kuma sai ta k'i yarda Saratu tasan abinda ya faru sai yar uwarta kad'ai abokiyar shawararta ta fad'a ma, Hassana ma ta shiga damuwa har ta kusa ta fita tashin hankali, amma haka suka dinga b'oyewa har lokaci ya dinga gangarawa, cikin hukuncin ubangiji kuma sai Allah ya fito musu da maza, d'aya d'an abokin Babansu ne yace yana son Hassana, sai wani mai mata biyu dake nan unguwarsu yace a bashi auren Husseina, dama mahaifinsu ya gaji dasu kamar yanda yake fad'a, dan haka ba'a d'auki lokaci ba aka d'aura musu aure kowace ta shiga d'akin aurenta.

_K'alubalen har yanzu bai fara ba, yayin da *BADAK'ALAR* yanzu ne zata soma._

😍 *See u guy's*😍
05/06/2020 à 20:36 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨
*BADAK'ALA*
👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨

*Labarin gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦

🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_12_

Zaha ta d'an shawarci mai gidan nata cewa ya za ayi aure haka kawai basu san waye shi ba, sannan ka d'auki 'ya ka bashi a sadaka, sanin dama sai anyi wannan cecekucen yasa yace shi zai yi wa 'yarshi duk wani abu da akewa kowace yar gata, haka lokacin ya ya fara tafiya dama kuma ba wani lokaci bane mai tsayi, har lokacin Zeeya da suley basu had'u ba dan k'iyayyarshi ce zalla a zuciyarta, shi kuma bai ma san ainihin me yake ji a game da ita ba, ana haka juma'a ta zo kuma aka d'aura aure, inda Alghabit ya wa suley wakilci liman kuma ya wa Zeeya, sadaki mafi girma da daraja ya biya wanda sai wane da wane, duk wata al'ada saida akayi ba'a bar komai ba, kafin nan amarya ta tare ita da halinta.

Zaman *doya* da *manja* suka fara, Zeeya dai banda gori da rashin kunya babu abinda take wa Suley, kullum ita ce fad'in bashi da kowa bashi da komai, da dukiyar ubanta yake duk wani abu na rayuwa, tunda sukayi aure basu kwana d'aki d'aya ba, dan lokacin shigowarshi nayi zata rufe na ta d'akin, abunci kam dama iya bakinta take dafawa, Suley yasha wahalar Zeeya fiye da tunanin mai karatu.

Ni kaina da ana bani labari na yaba da hak'urin shi, dan kad'an daga iskancin Zeeya yana iya d'iban ruwan wanka ta zubar da gangan ko kuma ta zuba wasu ruwan masu datti a ciki, ko kuma ta d'ibi k'asa ta zuba, ya kan shiga wanka ya rataya kayanshi a katanga da gangan ta d'auke kayan ta musu shark'af da ruwa, ankai matakin da saida Zeeya ta d'auki kayan Suley masu kyau wanda yake fita da shi tasa sabuwar wuk'a ta yagasu, Zeeya na iya ganin Suley zaune yana alwala ta d'auki sharar iskanci ta dinga bad'a mishi k'ura a jiki, wallahi wallahi yanda mai bani labarin ta fad'a min tace duk wannan iskancin idan tayi sai dai ya kalleta ya girgiza kai yace "Allah ya kyauta, ya ganar da ke gaskiya."

*Bayan wata d'aya* ya shirya tafiya gida dan ganin me ake ciki tunda yanzu Allah ya hore mishi kud'in mota harda ma na guzuri da tsaraba, haka ya sa kai ya tafi Zeeya bata damu ba dan dama nesa take so suyi da juna, bayan yaje ne ya samu labarin rasuwar mahaifiyarshi da ita kad'ai ta rage mi shi, hakan yasa shi dasa nashi kukan harya gode Allah, abin duniya ne ya taru ya mishi yawa, ga rashin uwa ga rashin sanin inda Husseina take, dan har yanzu babu wanda yace ya ganta da idon shi, haka Hassana ta bashi labarin rabon gadon da akayi tare da nuna masa yan dabbobin da aka basu, hakan ya b'ata mi shi rai sosai ta yanda har ya fara ikrarin cewa sai an sake wannan rabon gadon, dan son zuciya yayi yawa cikin wanda akayi, kuka sosai Hassana ta dinga yi tace yayi hak'uri kawai ya share ya barwa Allah, tunda gashi a cikin watannin da basu kai shekara ba har sun had'a garke, haka ya hak'ura badan ya so ba ita kuma tasan ko yanzu sai wani abun ya faru idan yayi maganar, haka ya shirya sake komawa wajen iyalinshi cike da burin son zama a mahaifarshi, sai dai abu d'aya ba zai yiwu lokaci d'aya haka yace zai dawo da Zeeya garin nan ba a yanda take, dan haka ya shirya ya shirya ya tafi ya kuma ce Hassana ta ci gaba da saka ido wajen neman yer uwarsu, idan an samu labari to taje kasuwa ta samu fatake dake yawon fatauci har zuwa Agadez ta bayar da sak'o za'a sanar da shi, sannan ta ci gaba da kula da duka gadon na su, haka ya koma ya samu Zeeya suka d'ora daga inda aka tsaya.

*Wata shida* suka d'auka a haka kafin ta fara kunno masa wutar saiya saketa, ita a dole ta gaji da zama da shi saiya saketa, shi kuma ya fad'a mata abinda ba zai iya ba kenan saboda darajar mahaifinta a wurinshi, duk dan tasa ya saketa saita fara fita barkatai ba tare da saninshi ba, idan ta fita har ta kan iya kai dare bata dawo ba, idan ya tambaye ta daga ina kike sai dai tace "Daga wajen wanda zuciya ta ke so, idan kuma kana da zuciya ka sakeni tun kafin na kawo maka cikin da baka da iko a kan shi."

Girgiza kai kawai yake yace "Allah ya kyauta, ya ganar dake gaskiya."

"Ya dai ganar da kai, dan kaine ke k'in gaskiya kake rufe ido ma idan ka ganta, na fad'a maka ya fi yawan gashin rak'umi cewa vana sonka, amma ka k'i rabuwa da ni na huta kaima ka huta."

Haka abubuwa ke tafiya ba dad'in yau bare na gobe, kuma duk fitar da take babu inda take zuwa, daga gidan 'yan uwa sai abokai, duk da bata da ilimin addini da kuma sanin yakamata, amma tasan zina da aure babban bala'i ne, shiyasa bata sake zina ba tunda sukayi aure, ana hakane har ranar dai ta ji tana buk'atar kusanci da namiji, tun safiyar ranar Suley ya ga banbanci, daga yanda take lumshe ido tana kallonshi, murya k'asa k'asa cikin wani irin yanayi, rigar dake jikinta ta matseta sosai ta fito mata da komai, haka shi dai ya fice ya barta dan baisan me hakan ke nufi ba baima fahimci meye damuwar ba, yana fita taji haushi sosai inda tasa hannunta tana ta shafar k'irjin ta da take jin yana mata k'yaik'ayi, haka ta wuni ba kuzari har lokacin dawowar Suley, dole ta yanke shawarar tunkararshi da kanta, ya dawo kamar yanda ya saba ya shiga wanka bayan ya aje kayanshi inda ba zata iya gani ba bare ta d'auka, tsaf ya gama ya saka kayanshi, saida ya fara lek'owa dan tunanin kar azo ta fara sharar nan ta rashin gaba, jin shiru yasa ya k'arasa fitowa gaba d'aya, mamakin rashin ganinta yake a tsakar gidan har yayi gaggawar shigewa d'akin shi ya maida k'ofa ya rufe, juyawar da zaiyi sai ko Zeeya zaune bakin gadonshi na k'arfe, gabanshi ne ya shiga fad'uwa ta ko ina yana kallon hannayenta kar azo da makami take, tasowa tayi ta nufo shi ta fara shafashi, ido ya zaro yana kallonta yace "Zeeya'atu kasheni zakiyi?"

Cike da salo na yan duniya tace "Kai ne dai zaka kasheni idan baka kulani ba."

Hannunshi ta kamo ta d'ora tafin hannunshi akan nononta na b'angaren dama, tana jin haka ta wani lumshe ido tare da zage rigar tayi k'asa, shi kam yana jin babu rigar da tayi shamaki saiya rufe ido yace "Sallalahu sanyi k'alau."

😂😂😂 *Maganar fa babbace domin kuwa harkace wannan ta kakanninmu*

Sai wannan rana ce Suley yasan da wannan duniyar dake b'oye jikin kowace mace, a wannan rana ce yayi dana sanin k'in zuwa tun da wuri, musamman da Zeeya ta zage ta nuna mishi ita fa 'yar barikin gida ce, sam mantawa yayi a wannan lokacin saida ya samu nutsuwa ya tuna da hakan, ita kanta Zeeya ta yaba da namijin k'ok'arin shi, dan inhar zata fad'i gaskiya to ya zo mata yanda take burin azo mata, buk'atar ta na biya ta koma Zeeyar ta ta asali, ta sake fito da salon rashin mutumci iri iri, *sati* uku babu wani abinda ya sake shiga tsakaninsu saida Suley yaji ya kai mak'ura ba zai iya hak'ura ba ya sameta har d'akin ta ya labb'eta, amma sai cewa tayi idan har yana so ta yarda saiya siyo mata gasashen nama na bakin kasuwa, tasan tafiya ce mai nisa amma haka ya daure ya je ya kawo, duk da haka saida ta gama wainashi taga kamar zai mata kuka kafin tayi wanka ta fito ta kwanta kan gado ta wani kalleshi tace "To taho."

_Sai kace zaki bawa yaro nono._

Jiki na rawa ya haura kan gado, tashi tayi zaune cikin tsawa tace "To ni ce zan cire maka kayan?"

Saukowa ya sakeyi daga kan gado ya cire kayan zai sake haurawa tace "Kaga muje ma d'akin ka, na fasa anan d'in."

Haka yabi bayanta bawan Allah shi dai ya samu nutsuwa kawai, a d'akin nashi ma saida taji yana daf da shiga ta zabura ta tashi zaune tace "Kaga ruwa nake so nasha, duk naman nan ya tsaya min a k'irji."

"To, to bara na kawo miki." Ya fad'a yana barin d'akin bai ko da nutsuwar da zaisan babu kaya a jikinshi, da irin wannan iskancin ta dinga ja masa rai, har saida ya shiga ya fara kenan ta sake yakice shi daga jikinta tace ya isa haka ta gaji, da sauri ya durko k'asa ya rik'e k'afar ta yace "Ki wa Allah Zeeya kiyi hak'uri, wallahi ba zan iya ba, ki fad'i duk abinda kike so ni kuma zan miki shi."
Chapter 43 · 0% Book details